Aminiya:
2025-10-13@17:56:06 GMT

’Yan bindiga sun ƙaƙaba wa ƙauyuka harajin N10m a Neja

Published: 4th, October 2025 GMT

’Yan bindigar da ke addabar yankunan karkara sun kaƙaba sun ƙaƙaba musu haraji da ke kaiwa Naira miliyan 10 a Ƙaramar Hukumar Mashegu Jihar Neja.

Rahotanni sun nuna cewa an umarci al’ummomin yankunan Babban Rami da Kaboji su su biya Naira miliyan biyu-biyu.

Yankin Sabon Rijiya da Sabon Rami an umarce su da su Naira dubu 500, yayin da aka umarci ƙauyukan da ke kusa da Dajin Keji su tara Naira miliyan 10 gaba ɗaya.

Haka nan, ana ƙaƙaba wa al’ummar Khizi an kaƙaba musu harajin Naira miliyan shida, da wa’adin ranar Juma’a, 3 ga Oktoba, 2025.

Wata mata ta banka wa kanta wuta a Bauchi Sharri Jonathan ke wa Buhari don lashe zaɓen 2027 —Garba Shehu

Wani mazaunin yankin ya shaida wa Aminiya cewa: “’Yan bindigar sun kashe mutane da dama kuma suna ci gaba da kai hare-hare. Sun kaƙaba haraji ga ƙauyukan da ke gefen dazukan Ibbi da gandun dabbobi na Kanji National Park.

“Muna roƙon gwamnati ta gaggauta ɗaukar mataki, saboda yawancinmu manoma ne, kuma sama da kashi 90 cikin 100 na amfanin gona bai ma kai girbi ba.”

Wata majiyar ta bayyana cewa da dama daga cikin manoma an kashe su ko an yi garkuwa da su a gonakinsu, yayin da matafiya ke fuskantar kwanton ɓauna a kan tituna, wasu kauyuka kuma ana kona su gaba ɗaya.

Rundunar ’yan sanda a Jihar Neja ba ta fitar da wata sanarwa kan lamarin ba zuwa lokacin haɗa wannan rahoto.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Bindiga Haraji ƙaƙaba haraji Naira miliyan

এছাড়াও পড়ুন:

’Yan sanda sun ceto mutum 10 daga hannun ’yan bindiga a Kaduna

Rundunar ’Yan Sandan Jihar Kaduna, ta samu nasarar ceto mutum 10 da ’yan bindiga suka yi garkuwa da su tsawon watanni huɗu da suka gabata a Ƙaramar Hukumar Kagarko.

A cikin sanarwar da kakakin rundunar, DSP Mansir Hassan, ya fitar, ya bayyana cewa daga cikin waɗanda aka ceto har da yara masu shekaru ɗaya, uku da kuma 13.

Tinubu ya yi wa Maryam Sanda afuwa Gwamnan Kebbi ya bai wa sojoji kyautar motoci 6 da babura 30 don inganta tsaro

DSP Mansir, ya ce ’yan bindigar sun kai farmaki ƙauyen Kushe Makaranta, inda suka sace mutanen daga gidajensu sannan suka kai su dajin da ke kusa da Rijana.

Rundunar, ta ce aikin ceto mutanen ya samu ne ta haɗin gwiwar ’yan sanda, jami’an DSS, da kuma sojoji.

Wani mazaunin yankin ya shaida cewa suna matuƙar farin ciki da wannan nasara, musamman ganin cewa mutanen sun kwashe watanni a hannun ’yan bindiga cikin tsananin wahala.

Hukumomin tsaro sun ce ana ci gaba da bincike domin kamo sauran ‘yan bindigar da suka tsere, tare da inganta matakan tsaro a yankin don kauce wa sake faruwar irin wannan lamarin.

“Za mu ci gaba da aiki tare da sauran hukumomi don tabbatar da cewa babu wata ƙungiyar ‘yan ta’adda da za ta samu mafaka a Kaduna,” in ji DSP Mansir Hassan.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ‘Yan Sandan Jihar Neja Sun Tabbatar Da Masu Sa-kai Kan Sahihiyar Kariya.
  • Soja ya kashe matarsa, ya hallaka kansa a Jihar Neja
  • Wata Kotu a Faransa ta yi watsi da rufe wata makarantar musulmi a birnin Nice  
  • China Ta Sha Alwashin Maida Martani Kan Harajin Trump A Kanta Na 100%
  • ’Yan sanda sun ceto mutum 10 daga hannun ’yan bindiga a Kaduna
  • Sojoji Sun Kashe Ƴan Ta’adda 9, Sun Ƙwato Naira Miliyan 5 A Borno
  • ‘Yansanda Sun Tabbatar Da Mutuwar Wata Ba’amurkiya Da Ta Ziyarci Saurayinta A Jihar Delta
  • Dalilin IFAD Na Zuba Naira Biliyan 16 A Fannin Noma A Benuwe
  • ’Yan bindiga sun kashe sojoji 3 a Kebbi 
  • ’Yan bindiga sun kashe Civilian JTF 8 a Zamfara