Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu, ya sauka a Lagos a jiya Juma’a domin ziyarar aiki yayin da ƙasar ke shirin bikin cikar shekaru 65 da samun ƴancin kai daga turawan mulkin mallaka.

A cewar kakakin shugaban ƙasa, Bayo Onanuga, Tinubu ya tafi Legas ne bayan ya halarci naɗin sabon Olubadan na Ibadanland, Oba Rashidi Ladoja, a garin Ibadan, jihar Oyo.

Sarkin Musulmi Ya Taya Ladoja Murnar Zama Sabon Sarkin Ƙasar Ibadan  Yadda Aka Gudanar Da Taron Tuna Shekara 20 Da Rasuwar Dr Bala Usman

Yayin da yake a Lagos, shugaban ƙasa zai gana da manyan ƴan kasuwa da jiga-jigai a ɓangaren gwamnati domin tattaunawa kan ci gaban tattalin arzikin ƙasa. Haka kuma, a ranar Talata, 30 ga Satumba, zai ziyarci jihar Imo inda zai ƙaddamar da wasu muhimman aiyukan raya ƙasa na Gwamna Hope Uzodimma.

A wani ɓangare na bikin zagayowar ranar ƴancin kai, Tinubu zai kuma ƙaddamar da sabuwar cibiyar al’adu da fasaha ta ƙasa, wadda aka sake fasalta wa daga tsohuwar National Theatre zuwa Wole Soyinka Centre for Culture and the Creative Arts.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Tukur Mamu ya karbi N50m daga kuɗin fansar harin jirgin kasan Kaduna – DSS

Hukumar tsaro ta DSS ta zargi dan jarida kuma mai shiga tsakani da ’yan ta’addar da suka sace fasinjojin jrigin kasan Kaduna-Abuja a shekarar 2022, Tukur Mamu, da karbar Naira miliyan 50 daga kudin fansar fasinjojin.

Ana zargin Tukur Mamu da karbar kudin ne daga jagoran ’yan bindigar da ake kira da “Shugaba”.

Zulum ya ba kowanne ɗalibin Borno da ke karatu a Indiya tallafin N500,000 Ko sisi ba a biya ’yan bindiga ba kafin su saki ɗaliban da suka sace – Gwamnan Kebbi

Mamu na fuskantar tuhumar laifukan ta’addanci, ciki har da karɓar kuɗin fansa daga iyalan waɗanda aka yi garkuwa da su a harin jirgin Kaduna na ranar 28 ga Maris, 2022, hulɗa da kuɗaɗen ’yan ta’adda, hana aikin kwamitin babban hafsan tsaron kasa da aka kafa domin tattaunawa da masu garkuwa da mutanen, musayar saƙonnin murya da mai magana da yawun Boko Haram, da sauransu.

A ci gaba da shari’ar a ranar Talata, shaida na hukumae ta DSS na shida ya shaida wa kotu cewa ƙungiyar ta’addan ta nemi Mamu ya koya musu yadda ake buɗe shafin yanar gizo domin gudanar da ayyukansu.

Tun da farko, DSS ta bayyana cewa Mamu ya ba da shawara ga ƙungiyar ’yan ta’addan da su tattauna kai tsaye da iyalan waɗanda aka yi garkuwa da su, ba tare da shiga kwamitin babban hafsan tsaron da gwamnatin tarayya ta kafa ba.

Shaidar ya yi wannan bayani ne yayin fassara saƙonnin murya na Mamu a lokacin da ake yi masa tambayoyi a ƙasar Masar kafin a dawo da shi Najeriya.

A halin yanzu, Mamu ya shigar da Babban Lauyan Gwamnati kuma Ministan Shari’a, Lateef Fagbemi (SAN) kara a gaban Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja, bisa kiran shi da dan ta’adda.

Ya ce ya shigar da ƙarar ce kan kiran nasa da dan ta’adda da ministan ya yi, alhali ana tsaka da shari’ar tuhumar laifukan ta’addanci kuma har yanzu ba a kai ga yanke hukunci ba.

Alƙali ya dage shari’ar zuwa ranar 23 ga watan Fabrairun 2026, domin amincewa da jawaban ƙarshe na ɓangarorin da abin ya shafa bisa tanadin Sashe na 49 na Dokar da kuma Sashe na 36 na Kundin Tsarin Mulkin Najeriya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An janye ’yan sanda 11,566 daga gadin manyan mutane a faɗin Nijeriya
  • Rasuwar Sheikh Dahiru Bauchi ta bar babban gibi a Najeriya – Tinubu
  • Mutuwar Sheikh Dahiru Bauchi Babban Rashi Ne Ga Kasa Baki Daya- Shugaba Tinubu
  • Mutuwar Sheikh Dahiru Bauchi Babban Rashi Ne Ga Kasa Baki Daya
  • Jihar Jigawa Za Ta Rufe Karbar Kudaden Aikin Hajjin 2026 Ranar 24 Ga Watan Disamba
  • Tinubu ya ayyana dokar ta-ɓaci kan harkar tsaro
  • Tinubu ya ayyana dokar ta-ɓaci kan tsaro
  • Jami’an tsaro sun ƙaddamar da shirin murƙushe ’yan bindiga a Kaduna
  • Tukur Mamu ya karbi N50m daga kuɗin fansar harin jirgin kasan Kaduna – DSS
  • Tinubu Ya Nuna Farin Cikinsa Bisa Bayyanar Daliban Kebbi, Ya Bukaci a Ceto Sauran