Manchester United Na Zawarcin Kane, Mainoo Na Son Ya Bar Old Trafford
Published: 25th, September 2025 GMT
Manchester United na zawarcin dan wasan gaban Ingila Harry Kane, mai shekara 32, wanda zai iya barin Bayern Munich a bazara mai zuwa.(Star), external
Kocin Tottenham Thomas Frank ya ce Kane, wanda ya fi kowa zura kwallaye a kulob din, ‘za su karbe shi da hannu biyu” idan ya dawo , amma ba ya tsammanin dan wasan zai bar kungiyarsa ta Jamus a yanzu.
Dan wasan tsakiya na Ingila Kobbie Mainoo, mai shekara 20, ya soma shirin barin Manchester United a watan Janairu domin neman wata kungiyar kwallon kafa .Ya samu wata kungiya da ta nemi a ba ta shi aro sai dai Man U ta yi watsi da tayin a bazara . (Mirror), external
Bayern Munich na tunanin sabunta kwantiragin dan wasan Faransa Michael Olise, mai shekara 23, bayan an alakanta shi da komawa Liverpool.(Liverpool Echo), external
Arsenal ta tuntubi dan wasan Turkiyya Kenan Yildiz, mai shekara 20, amma Juventus, wacce ta ki amincewa da tayin da Chelsea ta yi masa a lokacin bazara, ta kimanta shi kan Yuro miliyan 80 zuwa 100 . (Tutto Juve via Goal, external)
Chelsea na sha’awar dan wasan bayan Faransa Ismael Doukoure, mai shekara 22, wanda a halin yanzu yana kungiyar Strasbourg mallakar BlueCo, a dai dai lokacin da wasu kungiyoyin firimiya da dama ke zawarcinsa.(TBR Football), external
Aston Villa na son dan wasan gaban Ingila Jadon Sancho mai shekara 25 ya cigaba da taka mata leda na din din, Man U ce ta bada aron dan wasan ga Aston Villa. (National World)
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Wasanni mai shekara
এছাড়াও পড়ুন:
Super Falcons za su ƙaurace wa wasannin Nijeriya saboda riƙe musu alawus
’Yan wasan tawagar ƙwallon ƙafar Nijeriya ta Mata, Super Falcons, sun yi barazanar ƙaurace wa wasannin sada zumunta da Najeriya za ta buga a watan Disamba mai kamawa.
’Yan wasan sun ce za su ƙaurace wa wasannin ne idan har Hukumar Kwallon Kafa ta Najeriya (NFF) ta ci gaba da jinkirta biyan kuɗaɗen alawus-alawus da suke biyo tun na Gasar Olympics da aka yi a birnin Paris a 2024.
Andrea Thompson ta zama mace mafi ƙarfi a duniya Tinubu ya ayyana dokar ta-ɓaci kan matsalar tsaroWasu majiyoyi daga ƙungiyar sun tabbatar cewa ’yan wasan na ci gaba da jiran a biya su haƙƙoƙinsu na wasannin da suka buga, ciki har da alawus na nasarar da suka samu a gasar Olympics, duk da cewa Najeriya ta fice tun a matakin rukuni bayan shan kashi a hannun Brazil da Spain da Japan.
Wani jami’in tawagar, wanda ya nemi a ɓoye sunansa, ya ce ’yan wasan gaba ɗaya sun amince cewa ba za su halarci kowanne wasa ba muddin ba a biya su haƙƙoƙinsu ba.
Ana sa ran Najeriya za ta buga jerin wasannin sada zumunta daga ranar 2 zuwa 10 ga watan Disamba, a wani ɓangare na shirye-shiryen Super Falcons domin tunkarar gasar cin Kofin Afrika ta Mata na 2026.
A halin yanzu, NFF ba ta fitar da jerin sunayen ’yan wasan da za su wakilci Najeriya a wasannin ba.