Amurka ta matsa wa ƙasashe da ke fuskantar haraji su amince da Starlink
Published: 8th, May 2025 GMT
Amurka ta matsa wa gwamnatocin wasu ƙasashe da Shugaba Donald Trump ya ƙaƙaba musu haraji su amince da kamfanin intanet na Starlink mallakin Elon Musk a ƙasashensu.
Elon Musk shi ne mai kuɗin duniya kuma babban makusanci ne ga Shugaba Donald Trump.
Jaridar Washington Post ce ta ruwaito hakan a ranar Laraba, tana mai ambaton sakonnin waya na Ma’aikatar Harkokin Waje.
Sakonnin sun nuna yadda ofishin Jakadancin Amurka da ma’aikatar suka matsa wa ƙasashe don su kawar da duk wata cikas ga kamfanonin tauraron dan Adam, yana mai ambaton kamfanin Starlink da sunanta, kamar yadda jaridar Post ta ruwaito.
Takardun ba su nuna cewa gwamnatin Trump ta buƙaci a ba da fifiko ga Starlink a musayar rage haraji ba, kamar yadda jaridar ta ruwaito.
’Yan sanda sun kama harsasai 500 a Filato An kwantar da kishiyoyi a asibiti bayan sun sha ‘Kayan Mata’Amma sun nuna cewa Sakataren Harkokin Waje, Marco Rubio, ya umurci jami’ai da su matsa ƙaimi don samun amincewar ka’idoji ga kamfanin tauraron dan Adam na Starlink, mallakar Elon Musk.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Starlink
এছাড়াও পড়ুন:
Iran Ta Bukaci Kasashen Turai Su Shiga Tattaunawar Nukliya Da Take Yi Da Amurka
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran Esmail Baghaaei ya bukaci kasashen turai da su shiga a dama da su kan tattaunawa dangane da shirin nukliyar kasar Iran na zaman lafiya. Ya kuma jaddada cewa Iran tana turjiya ga dukkan tunanin Amurka na wargaza shirin Nukliyar kasar Iran kwata-kwata.
Baghaei ya kara da cewa duk da cewa Iran a shirye take a ci gaba da tattaunawa kan shirin makamashin nukliyar kasar, da sake farfado da yarjeniyar JCPOA ta shekara ta 2015 amma kuma ba zata taba barin hakkinta na mallakar fasahar nukliya da luma sarrafashi a hanyoyin da yarjeniyar NPT ta amince da su ba.
Kuma da alamun tattaunawar tsakanin Amurka da Iran ya daki dutse, saboda sun sami sabani a kan wasu al-amura wadanda basu shafi Nukliya ba, don haka ne aka fasa taron roma wanda yakamata a gudanar a ranar asabar da ta gabata. Batun cewa Mike Waltz mai bawa shugaban kasar Amurka shawara kan tsaro yana son cusawa gwamnatin Amurka ra’ayin Benyamin Natanyahu firai ministan HKI a tattaunawar Amurka da Iran, ya ce, wannan al-amari ne na cikin gida ga gwamnatin Amurka, amma abinda ya shafi Iran shi ne menene Amurka zata gabatar a kan teburin tattaunawa da ita.
Don haka ne Iran take bukatar kasashen Turai su shigo a dama da su a cikin wannan tattaunawar.