Amurka ta matsa wa ƙasashe da ke fuskantar haraji su amince da Starlink
Published: 8th, May 2025 GMT
Amurka ta matsa wa gwamnatocin wasu ƙasashe da Shugaba Donald Trump ya ƙaƙaba musu haraji su amince da kamfanin intanet na Starlink mallakin Elon Musk a ƙasashensu.
Elon Musk shi ne mai kuɗin duniya kuma babban makusanci ne ga Shugaba Donald Trump.
Jaridar Washington Post ce ta ruwaito hakan a ranar Laraba, tana mai ambaton sakonnin waya na Ma’aikatar Harkokin Waje.
Sakonnin sun nuna yadda ofishin Jakadancin Amurka da ma’aikatar suka matsa wa ƙasashe don su kawar da duk wata cikas ga kamfanonin tauraron dan Adam, yana mai ambaton kamfanin Starlink da sunanta, kamar yadda jaridar Post ta ruwaito.
Takardun ba su nuna cewa gwamnatin Trump ta buƙaci a ba da fifiko ga Starlink a musayar rage haraji ba, kamar yadda jaridar ta ruwaito.
’Yan sanda sun kama harsasai 500 a Filato An kwantar da kishiyoyi a asibiti bayan sun sha ‘Kayan Mata’Amma sun nuna cewa Sakataren Harkokin Waje, Marco Rubio, ya umurci jami’ai da su matsa ƙaimi don samun amincewar ka’idoji ga kamfanin tauraron dan Adam na Starlink, mallakar Elon Musk.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Starlink
এছাড়াও পড়ুন:
HOTUNA: Yadda aka yi jana’izar ’yan ɗaurin auren da aka kashe a Filato
An yi jana’izar ’yan ɗaurin auren da aka kashe a garin Mangu, da ke Ƙaramar Hukumar Mangu ta Jihar Filato.
Waɗanda aka kashe sun haɗa da maza, mata da yara.
Dole a ɗauki mataki kan waɗanda suka kashe ’yan ɗaurin aure a Filato — Uba Sani Mahaifin Rahama Sadau ya rasuDukkaninsu mazauna unguwar Basawa-Anguwan Rimi ne da ke Ƙaramar Hukumar Zariya a Jihar Kaduna.
Sun tashi ne daga Zariya zuwa Ƙaramar Hukumar Qua’an Pan da ke Jihar Filato domin halartar ɗaurin aure, amma aka kai musu hari a hanya.
An yi jana’izarsu tare da birne su da yammacin ranar Asabar a maƙabartar Hayi, ƙarƙashin tsauraran matakan tsaro.
Malamai a Mangu sun ce iyalan mamatan sun amince a birne su a Filato domin kaucewa shiga tashin hankali a garinsu.
Kafin yi musu jana’iza, malamai sun roƙi Musulmai su ɗauki lamarin a matsayin ƙaddara daga Allah, su kuma guji ɗaukar doka a hannunsu.
Sheikh Suleiman Haruna, ɗaya daga cikin malamai a yankin da ya jagoranci jana’izar, ya buƙaci jama’a da su zauna lafiya tare da yin haƙuri da juna.
Gwamnan Jihar Filato, Caleb Mutfwang, ya yi Allah-wadai da harin, inda ya umarci jami’an tsaro da su kamo masu hannu a lamarin.
Ga hotunan yadda jana’izar ta wakana: