Isra’ila Ta Yi Barazanar Kai Hare-Hare Kan Iran Kamar Hamas Da Hezbollah
Published: 8th, May 2025 GMT
Houthis sun kai hari kan babban filin jirgin sama na Isra’ila kusa da Tel Aviv a ranar Lahadi, a wani ɓangare na yaƙi da ‘yan tawayen ke yi kan Isra’ila, a matsayin tallafin ga Falasdinawa a Gaza. Iran ta musanta cewa ta goyi bayan Houthis a harin.
Duk da haka, Isra’ila ta mayar da martani kan Houthis tare da kai hare-hare kan filin jirgin sama na babban birnin Sana’a da ke hannun ‘yan tawayen da kuma tashoshin wutar lantarki a kewayen birnin.
Amurka da Houthis sun cimma yarjejeniyar sasantawa, kamar yadda Oman ta sanar a ranar Talata, inda ta ce yarjejeniyar za ta tabbatar da ” ‘yancin kewayawa” a cikin bahar maliya, inda ‘yan tawayen suke kai hare-hare kan jiragen ruwa.
Houthis sun yi alƙawarin ci gaba da kai hare-hare kan Isra’ila da jiragen ruwan Isra’ila a cikin bahar Maliya duk da yarjejeniyar da ta kawo ƙarshen hare-haren da Amurka ta kai wa Yemen.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: Iran Isra ila kai hare hare kan
এছাড়াও পড়ুন:
Karin ƙananan hukumomi 2 sun yi sulhu da ’yan bindiga a Katsina
Ƙaramar Hukumar Sabuwa da ta Ɗandume a Jihar Katsina sun rattaba hannu kan yarjejeniyar zaman lafiya da ’yan bindiga, a wani yunƙuri na kawo ƙarshen hare-hare, kashe-kashe da sace-sacen da suka daɗe suna addabar yankin.
An gudanar da taron sulhun ne a ranar Asabar a ƙauyen Kabalawa Dungun Mua’zu, da ke iyaka da ƙananan hukumomin biyu, amma yana ƙarƙashin Sabuwa.
Da wannan ci-gaban, adadin ƙananan hukumomi da suka ƙulla yarjejeniyar sulhu da ’yan bindiga a jihar ya kai tara.
Sauran sun haɗa da Batsari da Kankara, Kurfi da Musawa da Ɗanmusa da Jibia da kuma Faskari.
Yadda aka kashe jami’an tsaro 53 cikin mako biyu NAJERIYA A YAU: Yadda Wata Bakuwar Cuta Take Cin Naman Jikin Mutanen MalabuShugaban Ƙaramar Hukumar Sabuwa, Sagir Tanimi, da takwaroransa na Ɗandume, Bashir Gyazama, sun halarci taron, inda aka ce su ne suka taimaka wajen cimma yarjejeniyar.
Taron wanda ya ɗauki sa’o’i da dama ya haifar da wasu muhimman matsaya da ɓangarorin biyu suka cimma.
An amince da dakatar da kai hari, inda ’yan bindiga suka yi alƙawarin daina kai hare-hare a ƙauyuka.
Haka kuma an ba su damar shiga garuruwa da ƙauyuka domin harkokin kasuwanci ba tare da tsoron cutarwa daga jama’a ba.
Bugu da ƙari, ’yan bindigar sun yi alƙawarin sako mutanen da suka yi garkuwa da su, sai dai sun roƙi gwamnati ta yi ƙoƙarin ganin an saki ’ya’yansu da ke tsare.
Ɓangarorin biyu sun kuma sha alwashin yin aiki tare domin tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankin.
A yayin taron, ’yan bindiga da dama sun halarta ɗauke da manyan makamai, tare da shugabanninsu da suka haɗa da Idi Muwage da Alhaji Kabiru da Kachalla Rusku da Kachalla Murtala da Kachalla Mai Saje da Kachalla Dawa da Ardo Abdulsalam Fatika da kuma Alhaji Labi.
Shugaban kwamitin zaman lafiya, Dakta Salisu Ladan, ya bayyana cewa manufar yarjejeniyar ita ce dawo da zaman lafiya mai ɗorewa da kawo ƙarshen kashe-kashe da garkuwa da mutane da sauran munanan ayyuka.
Ya ƙara da cewa, “Shugabannin yankin sun tabbatar wa ’yan bindigar da tsaron rayukansu tare da maraba da su don su ci gaba da gudanar da harkokin kasuwanci a kasuwannin yankin.”
Haka kuma an cimma matsaya cewa za a buɗe kasuwar shanu ta Ɗandume da aka rufe saboda matsalar tsaro, domin bai wa ’yan bindigar damar kawo dabbobinsu da yin ciniki.