Isra’ila Ta Yi Barazanar Kai Hare-Hare Kan Iran Kamar Hamas Da Hezbollah
Published: 8th, May 2025 GMT
Houthis sun kai hari kan babban filin jirgin sama na Isra’ila kusa da Tel Aviv a ranar Lahadi, a wani ɓangare na yaƙi da ‘yan tawayen ke yi kan Isra’ila, a matsayin tallafin ga Falasdinawa a Gaza. Iran ta musanta cewa ta goyi bayan Houthis a harin.
Duk da haka, Isra’ila ta mayar da martani kan Houthis tare da kai hare-hare kan filin jirgin sama na babban birnin Sana’a da ke hannun ‘yan tawayen da kuma tashoshin wutar lantarki a kewayen birnin.
Amurka da Houthis sun cimma yarjejeniyar sasantawa, kamar yadda Oman ta sanar a ranar Talata, inda ta ce yarjejeniyar za ta tabbatar da ” ‘yancin kewayawa” a cikin bahar maliya, inda ‘yan tawayen suke kai hare-hare kan jiragen ruwa.
Houthis sun yi alƙawarin ci gaba da kai hare-hare kan Isra’ila da jiragen ruwan Isra’ila a cikin bahar Maliya duk da yarjejeniyar da ta kawo ƙarshen hare-haren da Amurka ta kai wa Yemen.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: Iran Isra ila kai hare hare kan
এছাড়াও পড়ুন:
Hare-haren Hizbullah Sun Jazawa HKI A Fagen Gona Asarar Dala Miliyan 108
Wani rahoto na musamman da HKI ta gudanar akan asarar da ta fuskanta sanadiyyar yaki da Hizbullah, ya bayyana cewa, a fagen aikin gona kawai sun yi asarar dalar Amurka miliyan 108 wacce ta fara daga 8 ga watan Oktoba 2023.
Kungiyar ReGrow Israel” ta ce, yakin da aka yi da Hizbullah ya yi barna gagaruma a fagen aikin gona da asarar da ta kai ta dala miliyan 108 a kan iyaka da Lebanon.
Nazarin wannan kungiyar ya kuma kara da cewa; Tun daga ranar 8 ga watan Oktoba 2023 har zuwa lokacin tsagaita wutar yaki a karshen 2024, hare-haren Hizbullah sun lalata muhimmacin cibiyoyi a “Isra’ila” da kuma haddasa gobara mai girma, da hakan ya tilastawa mazaunan yankin, musamman manoma yin hijira.
Bugu da kari, binciken ya ce, barnar da yakin ya haddasa akan gonaki, ya haddasa koma baya a fagen samar da abinci, da kuma kawar da daidaito a kasuwanni.
Shugabar zartarwa ta kungiyar “ReGrow Isra’el” Danil Abraham, ta sanar da cewa; Barnar da aka samu a kan iyaka da Lebanon tana da girman gaske, da kuma rikiritarwa, ta kuma shafi yanki mai girma fiye da fagen dagar Gaza.
Abraham ta kuma ce; Sai 9000 aka kai wa arewacin “HKI” hare-hare da makamai masu linzami da jiragen sama marasa matuki, da hakan ya sa gonaki masu yawa su ka kone. Haka nan kuma kaso 60% na manoman a Arewacin HKI, sun dakatar da ayyukansu baki daya.