Rundunar tsaron dake lura da aikin Hajji ta kama wani ɗan ƙasar Ghana bisa zargin ƙoƙarin fitar da mata huɗu daga ƙasashen waje zuwa Makkah ba tare da lasisin Hajj ba.

Matan, waɗanda ke cikin mota, an yi amfani da ɗakin kaya na motar domin ɓoye su don gujewa dokokin Hajj.

Gwamnatin Katsina Ta Sauya Masu Yi Wa Alhazai Hidima A Saudiyya Maniyyata Daga Turai Akan Dawakai Sun Isa Kasar Saudiyya Domin Yin Aikin Hajjin 2025

Rundunar tsaron ta kama direban motar tare da mata huɗun, sannan aka miƙa su ga hukumar da ta dace don aiwatar da hukuncin doka.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Kasar Saudiyya

এছাড়াও পড়ুন:

’Yan kungiyar asiri: Mutum 95 sun shiga hannu a Edo

Rundunar ’yan sandan Jihar Edo ta kama mutane 95 da ake zargi da ayyukan ƙungiyoyin asiri.

An kama mutanen ne a wani farmaki da aka kai kan masu aikata laifukan da suka shafi kungiyoyin asiri a garin Benin City da kewaye a makon da ya gabata.

Kwamishinan ’yan sanda, Monday Agbonik, ya bayyana cewa an gurfanar da 64 daga cikin wadanda ake zargin suna da alaka da kungiyoyin Maphites, Eiye, da Aye kuma ake zarginsu da kisan gilla da aka yi kwanan nan a rikicin kungiyoyin asiri.

Kayan da aka ƙwato sun hada da bindigogi biyu ƙirar gida, bindiga guda mai tashi daya, da harsashi 24.

’Yan sandan sun shawarci iyaye da su kula da ayyukan ’ya’yansu kuma sun gargadi matasa da kada su shiga kungiyoyin da ba bisa ka’ida ba wadanda ke kawo hatsari ga rayuwarsu.

Bincike na ci gaba da gudana kan sauran wadanda ake zargin.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ya Kamata Mata ‘Yan Fim Su Rike Mutuncin Kansu – Aisha Tafida Gombe
  • Yadda Wasu Mata Ke Gallaza Wa ‘Ya’yansu Domin Bakanta Wa Mazajensu
  • Sojojin Sun Kakkabe Wasu Manyan ‘Yan Bindiga A Zamfara
  • Kiwon Lafiya: Jihar Kwara Ta Bayyana Yadda Karancin Likitoci Ke Kawo Mata Cikas
  • An kama masu garkuwa da mutane 3 da kuɓutar da wasu
  • ’Yan kungiyar asiri: Mutum 95 sun shiga hannu a Edo
  • Kotu Ta Daure Wasu Mutum Biyu Da Suka Yi Wa Yarinya ‘Yar Shekara 14 Fyade A Birnin Kebbi
  • Likitoci A Amurka A  Amurka Sun Bukaci A Kawo Karshen Abinda Ke Faruwa A Gaza
  • An Kama Wani Babban Jami’in Sojan Kasar Burtaniya A Najeriya Tare Da Zarginsa Da Shigo Da Makamai