An Kama Wani Ɗan Ghana Bisa Zargin Kai Mata Hajji Ba Tare Da Lasisi Ba
Published: 5th, May 2025 GMT
Rundunar tsaron dake lura da aikin Hajji ta kama wani ɗan ƙasar Ghana bisa zargin ƙoƙarin fitar da mata huɗu daga ƙasashen waje zuwa Makkah ba tare da lasisin Hajj ba.
Matan, waɗanda ke cikin mota, an yi amfani da ɗakin kaya na motar domin ɓoye su don gujewa dokokin Hajj.
Gwamnatin Katsina Ta Sauya Masu Yi Wa Alhazai Hidima A Saudiyya Maniyyata Daga Turai Akan Dawakai Sun Isa Kasar Saudiyya Domin Yin Aikin Hajjin 2025Rundunar tsaron ta kama direban motar tare da mata huɗun, sannan aka miƙa su ga hukumar da ta dace don aiwatar da hukuncin doka.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: Kasar Saudiyya
এছাড়াও পড়ুন:
An kama mutum 2 kan sukar shugaban karamar hukuma a Kano
An kama mutum biyu ’yan jam’iyyar NNPP a Karamar Hukumar Tofa da ke Jihar Kano, kan sukar Shugaban Karamar Hukumar, Ibrahim Yakubu Addis, a Facebook.
Wadanda da aka kama sun hada da Murtala Garba Doka da Shamsu Safiyanu Lambu wanda aka fi sani da Shamzeet Lambu.
Najeriya ta yi watsi da sanya sunanta cikin jerin kasashen da ake tauye ’yancin addini Gwamnatin Tarayya ta fara shirin sayar da matatun manta ga ’yan kasuwaRahotanni sun bayyana cewar shugaban karamar hukumar ne ya bayar da umarnin kama su ne a ranar Litinin.
Shamzeet Lambu ya wallafa a Facebook, inda ya zargi shugaban karamar hukumar da kin kammala aikin titin Lambu zuwa Banki zuwa Yarimawa da Jakata, wanda gwamnatin jiha ta amince da shi kan kudi kimanin naira miliyan 240.
A rubutun da ya wallafa cikin harshen Hausa, Lambu ya ce: “Naira miliyan 240 kudinmu a Burji, Allah Ya saka mana.”
Rahotanni sun nuna cewa an fara tsare mutanen biyu a ofishin ’yan sanda na Tofa, kafin daga bisani aka mayar da su hedikwatar rundunar da ke kwaryar birnin Kano a Bompai domin ci gaba da bincike.
Shugaban matasa na yankin, Kwamared Nazifi Ado Lambu, ya tabbatar da kamen, inda ya ce hakan ya tayar da hankalin jama’a a yankin.
“E, an kama su saboda rubutun da suka yi a Facebook game da aikin titi. An tsare su a Tofa kafin daga bisani aka kai su Bompai,” in ji shi.
Wani mazaunin Lambu, wanda ya nemi a sakaya sunansa, ya ce al’ummar yankin sun dade suna rokon shugaban karamar hukumar kan gyara titin.
“Ya taba yin alkawarin zai gina titin da bututun ruwa da kwalta, amma bayan gwamnatin jiha ta amince da aikin, sai aka tsaya a iya share titi da zuba yashi, sai kuma aka bar aikin,” in ji mazaunin.
Da aka tuntubi shugaban karamar hukumar, Ibrahim Yakubu Addis, ya ce shi ne ya kai kara ofishin binciken laifuka (CID) domin a tabbatar da gaskiyar zargin da ake yi masa.
“Ba mu yi musu komai ba illa tambayarsu su kawo hujjar zargin da suka yi. Mutane da yawa suna ganin abin da ake wallafawa a intanet, kuma ba wannan ne karo na farko da suke irin wannan ba,” in ji shi.
Ya kuma ce adadin kudin aikin da suke zargi ba gaskiya ba ne.
“Gwamna ya amince da aikin da kudi kasa da Naira miliyan 100, ba miliyan 240 ba.
“Mun dai ce su kawo hujja kawai,” in ji shugaban.
Kamen mutanen biyu ya haifar da ce-ce-ku-ce a Karamar Hukumar Tofa, inda jama’a ke kira da a warware lamarin cikin lumana.