Leadership News Hausa:
2025-08-05@14:20:04 GMT

Cutar Mashaƙo Ta Kashe Yara Biyu A Kaduna

Published: 4th, May 2025 GMT

Cutar Mashaƙo Ta Kashe Yara Biyu A Kaduna

Cutar Mashaƙo ta ɓarke a unguwar Tukur-Tukur da ke garin Zaria ta jihar Kaduna, inda ta yi sanadiyar mutuwar yara biyu. Wannan ɓarkewar ta haifar da damuwa game da shirye-shiryen kiwon lafiya a Nijeriya. Abdulazeez Suleiman daga ƙungiyar Northern Elders Forum ya tabbatar cewa mutuwar ta faru cikin sa’o’i 48 bayan bayyanar alamun cutar.

“Wannan ɓarkewar da ta biyo bayan wata irinta ‘yan watannin da suka gabata – inda ta kashe mutane huɗu – yana nuna gazawar tsarin kiwon lafiya da rashin isasshiyar allurar rigakafi a yankunan karkara,” in ji Suleiman. Cutar Diphtheria cuta ce mai saurin yaɗuwa wacce ke haifar da kumburin maƙogwaro da wahalar numfashi.

Cutar Mashako Ta Yi Sanadin Mutuwar Yara 520 — Gwamnatin Kano Kisan Mummuken Cutar Mashako A Nijeriya Da Sassan Duniya

Suleiman ya yi kira da a ɗauki mataki nan take: “Muna bukatar gaggawar yin allurar rigakafi, da wayar da kan jama’a, da inganta kayan aiki.

Hukumar kula da lafiya ta jihar Kaduna ta tura tawaga cikin sauri don kai ɗauki yayin da take binciken yiwuwar alaƙa da wasu lokuta na baya-bayan nan a jihohin makwabta. Ana shawarartar iyaye da su tabbatar da cewa yara sun sami allurar rigakafi da kuma sanar da alamun cutar nan da nan.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Cutar Mashako

এছাড়াও পড়ুন:

An sace jaririya sa’o’i kaɗan bayan haihuwarta a asibitin Ekiti

An nemi wata jaririya sa’o’i kaɗan bayan haihuwarta an rasa a Cibiyar Lafiya ta Okeyinmi da ke Ado-Ekiti, babban birnin Jihar Ekiti, a ranar Litinin.

Wani ganau ya ce an gano ɓatan jaririyar ne lokacin da ma’aikatan jinyar da ke bakin aiki suka je su duba lafiyarta da safiyar wannan Litinin ɗin.

Za a samu ruwan sama kamar da bakin ƙwarya na kwanaki uku a faɗin Nijeriya — NiMet Shirin kashe N712bn kan gyaran filin jirgin Legas ya tayar da ƙura

Lamarin na ba-zato-ba-tsammani ya haifar da fargaba musamman yadda ɗimauta uwar jaririyar da kuma wasu daga cikin mutanen da ke cikin harabar asibitin.

Tuni dai an garzaya da ma’aikatan da ke kula da ɗakin haihuwa da uwar jaririyar da mai gadi da wasu da ake zargi zuwa ofishin ’yan sanda domin ci gaba da bincike.

Aminiya ta ruwaito cewa wasu masu neman na abinci a kusa da asibitin sun shiga ɗimuwa matuƙa dangane da faruwar lamarin.

Mai magana da yawun rundunar ’yan sanda na jihar, SP Sunday Abutu, ya ce yanzu haka akwai mutum huɗu da ake zargi da suka shiga hannu, “kuma suna bayar da bayanai masu amfani da za su taimaka a binciken.”

Abutu ya ce Kwamishinan ‘yan sanda na jihar, Mista Joseph Eribo, ya umurci sashen bincike na musamman (CID) da su gudanar da cikakken bincike domin tabbatar da dawo da jaririyar cikin ƙoshin lafiya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sanata Buba ya ƙaddamar da allurar rigakafin dabbobi kyauta
  • An sace jaririya sa’o’i kaɗan bayan haihuwarta a asibitin Ekiti
  • Gwamna Buni Ya Bukaci Sabon Sarkin Gudi Ya Jagoranci Zaman Lafiya, Hadin Kai, Da Ci Gaban Kasa
  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane Da Dama A Kauyukan Zamfara
  • Gwamnatin Sakkwato Za Ta Kashe fiye da Naira Miliyan 200 Wajen Gyara Tashar Talabijin Ta Kasa NTA
  • Wani Dan Siyasa Ya Shirya Addu’o’i Na Musamman Domin Samun Zaman Lafiya A Zamfara
  • Kashe N712bn Kan Gyaran Filin Jiragen Saman Legas Rashin Sanin Ya Kamata Ne – ADC 
  • An kama dilallan ƙwaya 28 a cikin barikin sojoji a Kaduna
  • Son Zai Bar Tottenham Zuwa Amurka Bayan Shafe Shekaru 10 A Ingila
  • Kashi 40 Na Ƙananan Yara A Nijeriya Ke Fuskantar Barazanar Yunwa — Rahoto