Zaunannen wakilin kasar Sin a MDD, Fu Cong, ya bayyana a gun taron kwamitin sulhu na MDD game da yankin manyan tabkuna na Afirka a ranar 16 ga wata cewa, sakamakon ci gaba da kai hare-hare na kungiyar M23 a baya-bayan nan, ya ta’azzara yakin gabashin Kongo DRC, kuma daukacin yankin manyan tabkuna sun fada cikin rudani.

Dole ne kasashen duniya su yi aiki tare kuma su hada kai don kawar da wannan mummunar yanayin cikin gaggawa.

 

Fu Cong ya jaddada cewa, dole ne a gaggauta tsagaita bude wuta domin hana shi ci gaba da ruruwa. Babu wata hanyar soji da za ta magance rikicin gabashin Kongo DRC, kuma tattaunawa ta siyasa ita ce kawai mafita. Dole ne kasashen duniya su dauki kwararan matakai don tallafa wa kasashen yankin manyan tabkuna wajen magance tushen matsalolin da ke haifar da gazawar shugabanci da rashin daidaituwar ci gaba a yankin. (Mai fassara: Mohammed Yahaya)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

An kama tsohon fursuna ya je fashi da bindiga AK-47

Jami’an Rundunar Leƙen Asiri ta musamman a Jihar Kwara sun cafke wani tsohon ɗan gidan yari mai suna Godday Agaadi da bindiga ƙirar AK-47.

An kama Emmanuel Okah ne bayan an same shi da bindigar AK-47 da harsashi guda 25 a jikinsa, a lokacin da yake sanye da kayan ’yan sanda.

Dubunsa ta cika ne yana ƙoƙarin satar talotalo a unguwar Omu Aran da ke ƙaramar hukumar Irepodun.

Kwamishinan ’Yan Sanda na jihar, Adekimi Ojo, ya bayyana a taron manema labarai a ƙarshen mako cewa binciken da jami’an suka gudanar ne ya kai ga cafke Agaadi.

An kama sojojin da suka yi yunƙurin juyin mulki a Benin An gano gawar malamin Islamiyya da ya ɓace a Neja

Ya ƙara da cewa bincike ya ci gaba har ya kai ga kama wasu mutane biyu da ake zargin abokan aikinsa, ciki har da wani boka mai shekaru 41 mai suna Oyeniyi Olabode.

Kwamishinan ya ce babban wanda ake zargi tsohon ɗan gidan yari ne da ke da tarihin aikata laifukan tashin hankali a yankin Omu Aran.

’Ya tabbatar da cewa dukkansu uku suna hannun ’yan sanda, kuma ana ci gaba da bincike domin gano sauran mambobin ƙungiyar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • MِِِِDD:  Kisan Kare Dangin Da Isra’ila Ta yi A Gaza Shi Ne Farko Da Yafi Jan Hankalin duniya
  • Kasashen Iran Da Azarbaijan Sun Amince Da Ci Gaba Da Tuntubar Juna Domin Warware Duk Wani Rikici
  • Iran Da Kasashen Afrika Sun Daura Dammarar Karfafa Alakar Kimiyya Tsakaninsu
  • Rashin Tsaro: Gwamnatin Tarayya ta gaza — Kwankwaso
  • An kama tsohon fursuna ya je fashi da bindiga AK-47
  • Dalilin yawaitar juyin mulki a Afirka ta Yamma
  • Iran Ta Gargadi Kasashen Larabawa Dangane Da Tsibiran Kasar Guda Uku A cikin Tekun Farisa
  • Iran Ta Zama Zakaran  Duniya A Wasan “Taekwondo” Na Masu Shekaru Kasa Da 21
  • Afirka Ta Kudu: An Kashe Mutane 11 A Wani Bude Wuta Na Kan Mai Uwa Da Wabi
  • Iran Da Masar Sun yi Kira Da Kawo Karshen Keta Hurmin Gaza da Labanon da Isra’ila ke yi