Zaunannen wakilin kasar Sin a MDD, Fu Cong, ya bayyana a gun taron kwamitin sulhu na MDD game da yankin manyan tabkuna na Afirka a ranar 16 ga wata cewa, sakamakon ci gaba da kai hare-hare na kungiyar M23 a baya-bayan nan, ya ta’azzara yakin gabashin Kongo DRC, kuma daukacin yankin manyan tabkuna sun fada cikin rudani.

Dole ne kasashen duniya su yi aiki tare kuma su hada kai don kawar da wannan mummunar yanayin cikin gaggawa.

 

Fu Cong ya jaddada cewa, dole ne a gaggauta tsagaita bude wuta domin hana shi ci gaba da ruruwa. Babu wata hanyar soji da za ta magance rikicin gabashin Kongo DRC, kuma tattaunawa ta siyasa ita ce kawai mafita. Dole ne kasashen duniya su dauki kwararan matakai don tallafa wa kasashen yankin manyan tabkuna wajen magance tushen matsalolin da ke haifar da gazawar shugabanci da rashin daidaituwar ci gaba a yankin. (Mai fassara: Mohammed Yahaya)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

’Yan bindiga sun sace mata 5 a Kano

’Yan bindiga sun kai hari a Jihar Kano a daren Lahadi, inda suka yi garkuwa mata biyar ciki har da masu shayarwa.

Wani ganau ya ce ’yan bindigar sun kai harin ne a ƙauyen ’Yan Kwada da ke cikin yankin Faruruwa a Karamar Hukumar Shanono da ke Shiyyar Kano ta Arewa.

Wani mazaunin yankin ya shaida wa Aminiya cewa dandazon maharan sun yi dirar mikiya a garin ne ɗauke da muggan makamai, inda suka yi ta harbe-harbe tare da shiga gidaje suna yin awon gaba da mutane.

“Sun zo kamar yadda suka saba, suna harbi a iska suna karya ƙofofi. Sun tafi da mata biyar, ciki har da masu shayarwa,” in ji majiyar.

Abdulmumin Jibrin ya koma APC wata 2 bayan NNPP ta dakatar shi Mahaifiyar Minista Balarabe Lawal Abas ta rasu

Sai dai ya ce daga cikin matan da aka sace, biyu sun tsere sun dawo, yayin da ragowar ukun ke hannun ’yan bindigar.

Harin na daren Lahadi na zuwa ne bayan mako guda da sojoji suka hallaka ’yan bindigar kimanin 19 a yankin.

Mutanen Faruruwa da sauran kauyuka da ke kan iyakar Kano da Katsina na ci gaba da rayuwa cikin fargaba sakamakon hare-haren ’yan bindiga da ke faruwa lokaci zuwa lokaci.

A sakamakon tsananin rashin tsaro, an ruwaito cewa yawancin ƙauyuka sun zama kufai, inda mazauna suka tswre zuwa garin Faruruwa ko kuma zuwa birane don tsira da rayukansu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iran Da Pakistan Sun yi Kira Da Yin Aiki Tare Don Tunkarar  Makiyansu
  • Ministocin Harkokin Wajen Kasashen Iran Da Rasha Sun Tattauna Kan Rikicin Yankin
  • Za Mu Kare Sojojin Da Ke Bakin Aiki — Ministan Tsaro
  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 3 Tare Da Sace Babur A Nasarawa
  • ‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi Sama Da 200 A Katsina
  • An ceto mutane 86 daga hannun ’yan ta’adda a Borno
  • An ceto mutane 86 daga hannun ’yan ta’adda 29 a Borno
  • Yadda Sojoji Suka Tarwatsa Haramtattun Matatun Mai 14 A Yankin Neja Delta 
  • ’Yan bindiga sun sace mata 5 a Kano
  • Maduro ya yi kira ga taron CELAC da ya yi tir da ayyukan tsokana na Amurka yankin Caribbean