Zaunannen wakilin kasar Sin a MDD, Fu Cong, ya bayyana a gun taron kwamitin sulhu na MDD game da yankin manyan tabkuna na Afirka a ranar 16 ga wata cewa, sakamakon ci gaba da kai hare-hare na kungiyar M23 a baya-bayan nan, ya ta’azzara yakin gabashin Kongo DRC, kuma daukacin yankin manyan tabkuna sun fada cikin rudani.

Dole ne kasashen duniya su yi aiki tare kuma su hada kai don kawar da wannan mummunar yanayin cikin gaggawa.

 

Fu Cong ya jaddada cewa, dole ne a gaggauta tsagaita bude wuta domin hana shi ci gaba da ruruwa. Babu wata hanyar soji da za ta magance rikicin gabashin Kongo DRC, kuma tattaunawa ta siyasa ita ce kawai mafita. Dole ne kasashen duniya su dauki kwararan matakai don tallafa wa kasashen yankin manyan tabkuna wajen magance tushen matsalolin da ke haifar da gazawar shugabanci da rashin daidaituwar ci gaba a yankin. (Mai fassara: Mohammed Yahaya)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Fransa Ta Kira Yi Kasashen Turai Da Sake Bitar Alakarsu Da “Isra’ila”

Ministan harkokin wajen Faransa ya kira yi tarayyar turai da ta sake bitar alakarta da Isra’ila saboda ci gaba da kisan kiyashin da take yi wa al’ummar Gaza da kuma hana shigar da kayan agaji.

 Matakin na Faransa dai ya biyo bayan na kasashen Spain, Ireland da kuma Holland, da suke son ganin an gudanar da bincike akan ko hare-haren Gaza din sun karya wani sashe na yarjejeniyar tasu. A karkashin yarjeniyoyin tarayya a tsakanin turai da HKI da akwai batun kare hakkin bil’adama.

Tun a cikin watan Yuni na 2000 ne nahiyar turai din ta kulla yarjejeniyar ayyuka a tsakaninta da HKI a fagage da dama, da hakan ya bai wa Tel Aviv fifiko na musamman a cikin kasuwannin turai. Harkokin kasuwanci a tsakaninsu ya kai dala biliyan 46.8 a 2022.

Ministan harkokin wajen Faransa  Jean-Noël Barrot ya bayyana cewa; Saboda matsayar Isra’ila akan gaza, ya zama wajibi a yi bitar alakarta da tarayyar turai.

Barrot ya bayyana tsananta hare-haren akan Gaza da kuma hana shigar da kayan abinci da cewa ” Ba abu ne da za a lamunta da shi ba.”

Haka nan kuma ya bayyana hare-haren na Isra’ila da cewa; cin zarafin Karaman dan’adam ne da kuma keta dokokin kasa da kasa, kuma yana cin karo da tsaron Isra’ila da Faransa ta yi alkawalin karewa,to amma duk abinda mutum ya shuka shi zai girba.

Gabanin Faransa, Faransa, kasar Holland ta yi kira irin wannan na yin bitar alaka da Isra’ila,wacce ministan harkokin wajen na Faransa ya ce, yana goyon baya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sojojin HKI Sun Bude Wuta Kan Jami’an Diblomasiyyar Wadanda Suka Je Jenin
  • Sharhin Bayan Labarai: Iran Zata Ci Gaba Da Tashe Uranium Tare Da Yarjeniya Ko Babu Ita
  • Sarkin Yawa Ya Fi Sarkin Karfi
  • Fransa Ta Kira Yi Kasashen Turai Da Sake Bitar Alakarsu Da “Isra’ila”
  •  Sojojin HKI Suna Ci Gaba Da Kashe Falasdinawa ‘Yan Gudun Hijira A Lokacin Da Suke Bacci
  • Tattaunawar Iran da Amurka na inganta zaman lafiya a yankin : Araghchi
  • Kasashen duniya 22 sun bukaci Isra’ila da ta dawo da agaji gaba daya a Gaza
  • Yankin Taiwan Ba Shi Da Iko Ko Hujjar Halartar Taron WHA
  • Sharhin Bayan Labarai: Dandalin Tattaunawa Na Tehran
  • Gwamnatin Kano Ta Dakatar Da Nuna Wasu Manyan Fina-Finai 22