Don su wuce zuwa zagaye na gaba, Real Madrid na buƙatar ta zura ƙwallaye huɗu ba tare da ta bari Arsenal ta zura ƙwallo ko ɗaya ba.

Idan kuma suka ci ƙwallo uku, kamar yadda Arsenal ta ci su, za a ƙara lokaci domin a fidda wanda yi nasara.

Fitaccen ɗan wasan Faransa, Kylian Mbappe, wanda bai taɓa lashe gasar Zakarun Turai ba, yana fatan ya lashe kofin karo na farko tare da Real Madrid.

Wannan wasa zai ba shi damar jan ragamar ƙungiyar don yin nasara a gaban dubban magoya bayanta.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Arsenal ƙwallo Tarihi Wasa

এছাড়াও পড়ুন:

Jonathan ya dawo Najeriya bayan juyin mulki ya ritsa da shi a Guinea-Bissau

Tsohon shugaban kasa Goodluck Jonathan ya dawo Najeriya bayan juyin mulkin sojoji ya ritsa da shi a ƙasar Guinea-Bissau inda ya je sa ido kan zaben ƙasar.

Jonathan ya isa filin jirgin sama na Nnamdi Azikiwe da ke Abuja da yammacin Alhamis, kusan kwana biyu bayan sojoji sun karɓi mulki a ƙasar da ke yammacin Afirka.

Ya kamata ’yan majalisar Najeriya su koma zaman wucin gadi – Ndume An janye ’yan sanda 11,566 daga yi wa manyan mutane rakiya – Egbetokun

Ya isa filin jirgin sama na Abuja a cikin jirgin gwamnatin Guinea-Bissau, inda tawagar magoya baya da jami’an gwamnati suka tarbe shi.

Tsohon shugaban kasar ya je Guinea-Bissau ne don sa ido kan zaben shugaban kasa da na majalisar dokoki a matsayin shugaban tawagar sa ido ta dattawan Afirka ta Yamma.

Tawagarsa, tare da ta Ƙungiyar Tarayyar Afirka (AU) da Ƙungiyar Raya Tattalin Arzikin Kasashen Yammacin Afirka (ECOWAS), suna ci gaba da aikinsu lokacin da sojoji suka yi juyin mulki a Guinea-Bissau.

Wannan lamari ya bar tsohon shugaban kasar tare da sauran mambobin tawagar masu sa ido cikin rashin tabbas da damuwa kan lafiyar su.

Sai dai ma’aikatar harkokin wajen Najeriya ta bayyana cewa tsohon shugaban kasa yana cikin koshin lafiya kuma ya bar Guinea-Bissau.

“Tsohon shugaban kasa Goodluck Ebele Jonathan yana cikin koshin lafiya kuma ya fita daga Guinea-Bissau,” in ji mai magana da yawun ma’aikatar, Kimiebi Ebienfa.

“Ya tafi ne da jirgi na musamman tare da mambobin tawagarsa, ciki har da Ibn Chambas.”

Sojojin Guinea-Bissau sun ƙwace iko da ƙasar a ranar Laraba, inda suka dakatar da tsarin zaben ƙasar tare da rufe iyakokinta, kwanaki bayan gudanar da zaben shugaban kasa da na majalisar dokoki.

Bayan juyin mulkin, shugaban ofishin soja na fadar shugaban kasa, Janar Denis N’Canha, ya ce kwamitin da ya ƙunshi dukkan sassan sojoji, ya karɓi jagorancin ƙasar har zuwa lokacin da za a bayar da sanarwa ta gaba.

Sojojin sun kuma kama shugaban kasar Umaro Embalo, wanda ake ganin zai iya lashe zaben na ranar Lahadi.

Kwana ɗaya bayan juyin mulkin, sojojin sun nada shugaban hafsoshin rundunar sojoji, Janar Horta N’Tam, a matsayin sabon shugaban ƙasar na na riƙon ƙwarya.

Zai jagoranci ƙasar na tsawon shekara guda.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Zanga zanga Ta Barke A Isra’ila Yayin Da Natanyaho Ke Neman Afuwa Kan Batun Cin Hanci Da Rashawa
  • An sake zabar Eto’o a matsayin Shugaban Hukumar kwallon kafa ta Kamaru  
  • Likitoci sun gindaya sabon sharaɗi bayan janye yajin aiki
  • Muna buƙatar taimakon ƙasashen waje kan tsaro a Najeriya — Obasanjo
  • Yadda aka horar da mata 100 sana’o’in dogaro da kai a Gombe
  • Portugal ta lashe Kofin Duniya na ’yan ƙasa da shekaru 17 a karon farko
  • An Rantsar Da Sabon Shugaban Mulkin Soja Na kasar Guinea-Bissau
  • Jonathan ya dawo Najeriya bayan juyin mulki ya ritsa da shi a Guinea-Bissau