Don su wuce zuwa zagaye na gaba, Real Madrid na buƙatar ta zura ƙwallaye huɗu ba tare da ta bari Arsenal ta zura ƙwallo ko ɗaya ba.

Idan kuma suka ci ƙwallo uku, kamar yadda Arsenal ta ci su, za a ƙara lokaci domin a fidda wanda yi nasara.

Fitaccen ɗan wasan Faransa, Kylian Mbappe, wanda bai taɓa lashe gasar Zakarun Turai ba, yana fatan ya lashe kofin karo na farko tare da Real Madrid.

Wannan wasa zai ba shi damar jan ragamar ƙungiyar don yin nasara a gaban dubban magoya bayanta.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Arsenal ƙwallo Tarihi Wasa

এছাড়াও পড়ুন:

Shugaba Tinubu Ya Nada Janar Christopher Musa Sabon Ministan Tsaro

Daga Bello Wakili

Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya nada Janar Christopher Gwabin Musa a matsayin sabon Ministan Tsaro.

A wata wasika da ya aike wa Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio, Shugaba Tinubu ya mika sunan Janar Musa domin ya maye gurbin Alhaji Mohammed Badaru Abubakar, wanda ya yi murabus a ranar Litinin.

Janar Musa, mai shekaru 58, wanda zai cika 59 a ranar 25 ga Disamba, jajirtaccen soja ne da ya jagoranci rundunonin tsaro a matsayin Shugaban Hafsoshin Tsaro daga 2023 zuwa watan Oktoban 2025.

An haifi Janar Musa a Sakkwato a 1967, inda ya yi makarantar firamare da sakandare kafin ya tafi College of Advanced Studies a Zariya. Ya kammala a 1986 sannan ya shiga Kwalejin Horas da matsakaitan Sojoji (NDA) duk dai a wannan shekarar, inda ya samu digiri na daya a fannin kimiyya a 1991.

An daga Janar Musa zuwa matsayin babban Laftanar  (Second Lieutenant) a 1991, kuma tun daga lokacin ya yi aiki a manyan mukamai iri-iri. Daga cikin mukamansa akwai: Babban Jami’in Ma’aikata a bangaren Horaswa da Ayyuka a Hedikwatar Runduna ta 81;
Kwamandan Bataliya ta 73;
Mataimakin Darakta, Kayayyakin Aiki, Sashen Tsare-tsaren Rundunar Soja;
Wakilin Sojin Kasa a Kwamitin Horaswa na Hedikwatar Soji ta Najeriya.

A 2019, ya yi aiki a matsayin Mataimakin Babban Jami’in Ma’aikata na Horaswa da Ayyuka a Hedikwatar Cibiyar Sojin Kasa;
Kwamandan Sashe na 3 na Rundunar Lafiya Dole; da kuma Kwamandan Sashe na 3 na Rundunar Hadin Gwiwar Kasashen Yankin Tafkin Chadi (Multinational Joint Task Force).

A 2021, an nada shi Kwamandan  Operation Hadin Kai, inda daga baya ya zama Kwamandan Rundunar Sojin Kasa ta Najeriya, kafin daga bisani Shugaba Tinubu ya nada shi Shugaban Hafsoshin Tsaro a 2023.

A cikin wasikar da ya aikewa Majalisar Dattawa, Shugaba Tinubu ya bayyana cikakken kwarin gwiwa kan ƙwarewar Janar Musa wajen jagorantar Ma’aikatar Tsaro tare da ƙara inganta tsarin tsaron Najeriya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An kashe matashi yayin rikici a wajen raɗin suna a Bauchi
  • Matashi ya rasu yayin rikici a wajen radin suna a Bauchi
  • ’Yan sandan Borno sun kama matashin da ake zargi da kashe makwabciyarsa da wuƙa
  • NAPTIP ta daƙile yunƙurin safarar mutum 7 daga Kano zuwa Saudiyya
  • Yau Majalisar Dattawa za ta tantance sabon Ministan Tsaro
  • Tinubu ya naɗa Janar Christopher Musa sabon Ministan Tsaron Nijeriya
  • Shugaba Tinubu Ya Nada Janar Christopher Musa Sabon Ministan Tsaro
  • Tinubu ya naɗa Janar CG Musa sabon Ministan Tsaron Nijeriya
  • An yi garkuwa da manoma 11 a Kudancin Kaduna
  • An Bude Taron Bikin Cika Shakaru 41 Da Kafa Kungiyar Tattalin Arziki Ta ECO A nan Tehran