UEFA: Mbappe Zai Jagoranci Real Madrid Yayin Da Ta Ke Fatan Kafa Sabon Tarihi A Santiago
Published: 16th, April 2025 GMT
Don su wuce zuwa zagaye na gaba, Real Madrid na buƙatar ta zura ƙwallaye huɗu ba tare da ta bari Arsenal ta zura ƙwallo ko ɗaya ba.
Idan kuma suka ci ƙwallo uku, kamar yadda Arsenal ta ci su, za a ƙara lokaci domin a fidda wanda yi nasara.
Fitaccen ɗan wasan Faransa, Kylian Mbappe, wanda bai taɓa lashe gasar Zakarun Turai ba, yana fatan ya lashe kofin karo na farko tare da Real Madrid.
Wannan wasa zai ba shi damar jan ragamar ƙungiyar don yin nasara a gaban dubban magoya bayanta.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: Arsenal ƙwallo Tarihi Wasa
এছাড়াও পড়ুন:
Tuƙin ganganci: KASTELEA Ƙaddamar Da gangamin wayar da kai a Zariya
Hukumar Kula da Tsaftace Muhalli da Ababen Hawa ta Jihar Kaduna (KASTELEA) ta ƙaddamar da yaƙin wayar da kan jama’a na watannin ƙarshen shekara na shekarar 2025 a Tashar Motoci ta Malam Nasiru El-Rufa’i da ke ’Yan Ƙarfe, Sabon Gari, Zariya.
Taron yaƙin wayar da kan jama’a na ‘Watannin Ember’ na shekarar 2025 mai taken: “Tafiyar aminci ana cimma ta ta hanyar tuƙi cikin tsaro,” ya samu halartar hukumomin tsaro daban-daban da ke da ƙudirin rage haɗurra a kan manyan hanyoyin jihar
A wajen taron, Sarkin Zazzau, Malam Ahmad Nuhu Bamalli, ya jaddada muhimmancin rawar da kowa a cikin al’umma zai taka wajen tabbatar da tsaron hanya da kuma tuƙi cikin natsuwa.
Wakilin Sarkin a taron, Injiniya Ibrahim Balarabe Musa, ya bayyana cewa harkar kula da zirga-zirgar ababen hawa aiki ne da ya haɗa hukumomi da dama.
Mutane 315 ne suka ɓace bayan hari a makaranta Neja Sace ɗalibai: An rufe makarantu a Katsina da Taraba“Batun zirga-zirga ba na hukuma ɗaya ba ne. Rundunar ’yan sanda, ma’aikatan kashe gobara, Sibil Difens Hukumar Kiyaye Haɗurra ta Ƙasa (FRSC) duk suna da rawar da za su taka wajen cimma manufa ɗaya — tsaro,” in ji shi.
Ya ƙara da cewa wayar da kan jama’a kan tsaro a hanya aiki ne na kullum, tare da yaba wa jajircewar ma’aikatan tsaro.
‘Watannin Ember’ da cunkoson hanyaA nata jawabin, Shugabar KASTELEA, Karla AbdulMalik, ta bayyana cewa Watannin Ember — daga Satumba zuwa Disamba — sukan fi fuskantar cunkoso sakamakon tafiye-tafiyen al’umma domin bukukuwan ƙarshen shekara.
Ta ce yawan zirga-zirgar ababen hawa a wannan lokaci kan haifar da cunkoso, tuƙin ganganci fa kuma karuwar hadurra, lamarin da ke janyo asarar rayuka da dukiya.
“Mun zo ne domin wayar da kan jama’a su bi ƙa’idojin hanya, tare da ƙarfafa wa fasinjoji gwiwa su tsawatar idan suka ga direba na tuƙi cikin hatsari. Kauce wa haɗurra nauyi ne da ya rataya a kan kowa,” in ji ta.
Ta buƙaci direbobi da ke cikin jihar ko masu wucewa su kiyaye dokokin hanya, su kuma rinƙa tuƙi cikin natsuwa don tsira da rayuwar al’umma.
Kiran FRSC da ƙungiyoyin sufuriA nasa ɓangaren, Kwamandan Shiyyar Zariya na Hukumar FRSC, Nasiru Abdullahi Falgore, wanda SRC Kabiru Kabiru Mado ya wakilta, ya bayyana wannan lokaci a matsayin na tsananin taka-tsantsan.
Ya nuna damuwa kan yawaitar mutuwar mutane da asarar dukiya, tare da kira ga direbobi su bi doka su kuma ɗauki matakan rage haɗurra.
Daga ɓangaren kungiyoyin sufuri, Mataimakin Shugaban NARTO na Jihar Kaduna, Sa’idu Mustapha Basawa, ya bayyana kyakkyawar hulɗar da ke tsakaninsu da hukumomin tsaro.
Ya kuma buƙaci gwamnati ta ƙara sanya alamun hanya a wurare masu muhimmanci, tare da jaddada buƙatar direbobi su riƙa bin ƙa’idojin hanya.