UEFA: Mbappe Zai Jagoranci Real Madrid Yayin Da Ta Ke Fatan Kafa Sabon Tarihi A Santiago
Published: 16th, April 2025 GMT
Don su wuce zuwa zagaye na gaba, Real Madrid na buƙatar ta zura ƙwallaye huɗu ba tare da ta bari Arsenal ta zura ƙwallo ko ɗaya ba.
Idan kuma suka ci ƙwallo uku, kamar yadda Arsenal ta ci su, za a ƙara lokaci domin a fidda wanda yi nasara.
Fitaccen ɗan wasan Faransa, Kylian Mbappe, wanda bai taɓa lashe gasar Zakarun Turai ba, yana fatan ya lashe kofin karo na farko tare da Real Madrid.
Wannan wasa zai ba shi damar jan ragamar ƙungiyar don yin nasara a gaban dubban magoya bayanta.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: Arsenal ƙwallo Tarihi Wasa
এছাড়াও পড়ুন:
H-JRBDA ta yi alƙawarin magance ambaliyar ruwa a Jigawa
Hukumar Raya Kogunan Hadejia da Jama’are (H-JRBDA) ta yi alƙawarin ɗaukar matakan gaggawa don magance matsalar ambaliyar ruwan da ke addabar al’ummar Ƙaramar Hukumar Jahun a Jihar Jigawa.
Manajan Daraktan Hukumar, Injiniya Rabi’u Sulaiman Bichi, ya bayyana hakan bayan karɓar roƙon da jama’ar yankin suka miƙa ta hannun Shugaban Ƙaramar Hukumar, Jamilu Ɗan Malam Mai Rice, kan yawaitar ambaliya a yankin.
Gwamnatin Yobe ta ba da umarnin rufe makarantun kwana a jihar Gwamnatin Tarayya ta musanta jita-jitar rufe dukkanin makarantu a faɗin NajeriyaA cewar Injiniya Bichi, “Mun karɓi kokenku hannu biyu. Matakin da shugabancin Jahun ya ɗauka ya yi dai-dai. Za mu tura ƙwararrun injiniyoyi su yi aikin da ya kamata domin daƙile ambaliyar, tare da inganta noman yankin ta hanyar gina madatsar ruwa domin ruwan sha da na aikin gona.”
A nasa bangaren, Shugaban Ƙaramar Hukumar Jahun, Hon. Jamilu Ɗan Malam Mai Rice, ya ce sun gabatar da koken ne saboda matsalar ambaliyar ta daɗe tana addabar su ba tare da samun mafita ba.
Ya ce, “Muna godiya bisa yadda kuka amsa kiranmu. Kun zo kun duba matattarar ruwan Akama da ta Fande tare da ƙwararrun injiniyoyinku. Wannan ya nuna ku na da niyyar magance matsalar da ta dade tana damunmu.”
Tawagar hukumar da ta kai ziyarar ta haɗa da Daraktan Kuɗi da Mulki, Musa Iliyasu Kwankwaso; Daraktan Tsare-tsare, Alhaji Tijjani Musa Isah; Daraktan Na’urori, Injiniya Dan Baffa Abdulƙadir; da Injiniya Sabi’u Ɗan Malan, tare da sauran manyan jami’an hukumar.