Ina Da Ƙwarewar Da Zan Iya Zama Shugaban Ƙasar Nijeriya – Makinde
Published: 16th, April 2025 GMT
Ya jaddada cewa dole ne a gyara jam’iyyar PDP kafin a fara tunanin neman wani muƙami.
Ya ƙara da cewa ko da siyasarsa ta tsaya a matsayin gwamna, zai kasance cikin farin ciki da gamsuwa.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku.
এছাড়াও পড়ুন:
2027: Jam’iyyar NNPP ta rantsar da sabbin shugabanni a Gombe
Jam’iyyar NNPP ta rantsar da sabbin shugabanninta a Jihar Gombe, inda ta jaddada muhimmancin haɗin kai da farfado da jam’iyyar tun daga matakin ƙananan hukumomi zuwa jiha gabanin zaɓen 2027.
Taron ya halarta bayan zuwan wakilai daga dukkanin ƙananan hukumomin jihar.
Zaɓen 2027 ya hana ni korar wasu ma’aikata – Bago Sojoji sun kashe ’yan ta’adda 2, sun ƙwato makamai a BornoMambobin jam’iyyar sun yaba da yadda komai ya gudana cikin lumana da tsari, abin da suka ce alama ce ta daidaito a cikin jam’iyyar.
Elder Ambrose Ismail Mairungu ne, ya zama sabon shugaban NNPP na jihar, yayin da Yakubu Adamu Tela, ya zama mataimakinsa.
Abdullahi Ali Mohammed, ya samu kujerar sakataren jiha, sannan Hon. Amatiga Yila Naboth (ACG) ya zama sakataren yaɗa labarai.
Sauran da aka zaɓa sun haɗa da Musa Mohammed Gargajiga (Jagoran Matasa), Hajiya Hauwa Mohammed (Shugabar Mata), da Kabiru Mohammed Puma (Sakataren Tsara Ayyuka).
A jawabin da ya gabatar bayan rantsar da su, Mairungu, ya gode wa ’yan jam’iyyar bisa amincewa da suka nuna gare shi, inda ya bayyana cewa sabbin shugabannin za su yi aiki da adalci da tsari, tare da haɗa kowa domin ci gaban jam’iyyar.
Ya ce za su mayar da hankali wajen gina jam’iyyar daga matakin unguwanni, ƙara yawan mambobi, da ƙarfafa shiga matasa da mata a harkokin jam’iyya.
Wasu masu ruwa da tsaki da suka halarci taron sun yaba da sabbin shugabannin, inda suka ce suna da damar gyara jam’iyyar kafin tunkarar babban zaɓe.
Haka kuma, sun yi godiya ga Jagoran NNPP na ƙasa, Rabiu Musa Kwankwaso, bisa tallafi da goyon bayan da ya bai wa taron.