A Kalla Mutane 9 Ne Su Ka Yi Shahada A Gaza
Published: 16th, April 2025 GMT
HKI tana ci gaba da kai wa yankunan Gaza mabanbanta hare-hare da hakan ya yi sanadiyyar samun shahidai a yau Laraba.
Tun da safiyar yau Laraba ne HKI ta kai hari akan wani gida dake unguwar “al-Tuffah” dake cikin birnin Gaza da hakan ya sa mutane 6 su ka yi shahada.
A yankin Jabaliya kuwa jiragen yakin HKI sun kai hari akan wani gida da ya yi sanadiyyar shahadar mutane 3.
A wani labarin kungiyar ” Likitoci Ba Tare Da Iyaka Ba” ta bayyana cewa; Isra’ila ta mayar da yankin Gaza zuwa Makabarta.
Kungiyar ta bayyana cewa; Yadda Isra’ila take fadada wuraren da take kai wa hare-hare ta sama, kasa da ruwa a yankin Gaza , tana korar mazauna yankin ta hanyar amfani da karfi da kuma hana shigar da kayan agaji zuwa yankin.
Kungiyar ta kara da cewa; Abinda Isra’ilan take yi ya sa rayuwa ta yi tsanani a cikin yankin da kuma mayar da shi zuwa babbar makabarta.
Jami’a mai kula da ayyukan kungiyar a Gaza, Amandi Barirol ya bayyana cewa; A halin yanzu Falasinawa ba su da wanda zai taimaka musu.”
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Shugaba Xi Ya Jaddada Bukatar Gina Ingantaccen Yankin Ciniki Cikin ’Yanci Na Tashar Ruwa Ta Hainan
A yau Alhamis, shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya jaddada bukatar gina ingantaccen yankin ciniki cikin ’yanci na tashar ruwa ta Hainan ko FTP a takaice. Shugaba Xi ya bayyana bukatar ne yayin dake sauraron rahoton aiki game gina yankin na FTP a birnin Sanya na lardin Hainan dake kudancin kasar Sin.
A cewarsa, gina yankin FTP na Hainan muhimmiyar manufa ce ta kwamitin kolin JKS, wadda aka tsara domin zurfafa cikakkun sauye-sauye, da bude kofa ga waje a sabon zamani.
Shugaban na Sin ya kara jaddada bukatar kyautata nazari, da aiwatar da ka’idojin aiki na cikakken zama karo na hudu na kwamitin kolin JKS na 20, tare da kokarin cimma burikan da aka sanya gaba, dangane da bunkasa yankin FTP na Hainan a dukkanin fannoni, ta hanyar lura da tsare-tsare, da aiki tukuru da wanzar da kwazon aiki.
A ranar 18 ga watan Disamban bana ne yankin FTP na Hainan, zai kaddamar da ayyukan kwastam na musamman na daukacin tsibirin, matakin da shugaba Xi ya ce zai kasance jigon matakai da kasar Sin za ta aiwatar, don fadada bude kofa mai inganci, da ingiza gina budadden tattalin arzikin duniya. (Saminu Alhassan)
ShareTweetSendShare MASU ALAKA