Aminiya:
2025-04-30@20:33:30 GMT

Dalilin da Kwankwaso zai dawo APC — Ganduje

Published: 16th, April 2025 GMT

Shugaban jam’iyyar APC na ƙasa, Dokta Abdullahi Umar Ganduje, ya bayyana cewa ƙiris ya rage madugun jam’iyyar NNPP, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso ya dawo jam’iyyarsu ta APC.

Gamduje ya bayyana hakan ne yana mai cewa jam’iyyar NNPP ta mutu murus, kuma jana’izarta kaɗai suke jira a gudanar a nan kusa.

Gwamnatin Tarayya ta ayyana hutu ranar Juma’a da Litinin Barcelona da PSG sun tsallaka zagayen kusa da na ƙarshe a Gasar Zakarun Turai

Ganduje ya bayyana haka ne a ranar Talata yayin ziyarar da wata ƙungiya mai goyon bayan Shugaba Bola Tinubu (TSG) ta kai sakatariyar APC ta ƙasa da ke Abuja.

Ganduje ya ce APC a kodayaushe tana cikin shirin karɓar jiga-jigan ‘yan siyasa ciki har da Kwankwaso “idan har ya yanke shawarar dawowa gida.”

Ganduje ya bayyana cewa jam’iyyar NNPP ta rasa duk wani karfi da tasiri da take da shi, musamman a Jihar Kano, inda ya ce ‘yan jam’iyyar da dama sun bar ta.

Ya ce: “NNPP ta mutu. Kuma ba da jimawa ba za a birne ta. Amma abin da ya rage shi ne a haƙa kabari, kuma har an fara hakan. Muna jiran a kammala shiri ne kawai.”

A cewarsa, “Kwankwason ya fara yunƙurin dawowa APC saboda ya fahimci cewa ya rasa komai a jam’iyyar da ya tallata.”

“Ƙofa a buɗe take ga duk wanda ya shirya dawowa APC”, yana mai cewa Kwankwaso zai samu tarba mai kyau idan ya dawo gida.

“Za mu karɓe shi idan ya dawo, domin gida zai dawo,” in ji Ganduje.

Ya ƙara da cewa APC ta na ci gaba da karɓar fitattun ‘yan siyasa daga sassa daban-daban, wanda hakan ke ƙara ƙarfafa jam’iyyar a faɗin ƙasar.

Haɗakar ’yan adawa ba za ta yi tasiri ba — Ganduje

Shugaban jam’iyyar ta APC ya kuma ce haɗakar da wasu ‘yan siyasa ke ƙoƙarin yi domin ƙalubalantar Shugaba Tinubu a Zaɓen 2027 ba za ta yi tasiri ba “domin kuwa rushewa za ta yi kafin a je ko’ina.”

Ganduje ya ce: “Wannan haɗakar da ake ta surutai a kai, za ta tarwatse kafin ta gama haɗuwa. Yawancin su za su dawo cikin APC, domin sun san cewa nan ne gida.”

Ganduje ya jaddada cewa jam’iyyar APC za ta ci gaba da jan ragamar mulki a Nijeriya saboda ingantattun manufofi da kuma salon shugabancin Tinubu.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Abdullahi Umar Ganduje Sanata Rabi u Musa Kwankwaso a jam iyyar

এছাড়াও পড়ুন:

Hajjin 2025: Jihar Kwara Ta Fara Allurar Rigakafi Ga Maniyyata

Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Kwara ta fara yi wa maniyyata rigakafin cututtuka kafin gudanar da aikin Hajji na shekarar 2025.

Da yake jawabi a wajen kaddamar da shirin rigakafin da aka gudanar a harabar hukumar da ke Ilori, shugaban hukumar, Alhaji Abdulsalam Abdulkadir, ya bayyana rigakafin a matsayin wani sharadi da ya zamto wajibi ga dukkan Alhazai bisa umarnin gwamnatin Saudiyya.

Ya ce yin rigakafin yana da matuƙar muhimmanci wajen tabbatar da lafiyar Alhazai a lokacin gudanar da aikin Hajji.

A cewarsa, an shirya shirin rigakafin ne domin hana yaduwar cututtuka da kuma tabbatar da cewa Alhazai sun samu lafiya da kwanciyar hankali yayin aikin Hajjin.

Alhaji Abdulkadir ya bayyana cewa za a fara jigilar rukuni na farko na Alhazai daga jihar zuwa ƙasar Saudiyya ranar 12 ga watan Mayu.

 

Shugaban hukumar ya ƙara da cewa za a kammala aikin rigakafin ne ranar Laraba 30 ga watan Mayu, sannan kuma za a fara raba tufafi da jakunkunan tafiya nan take.

Alhaji Abdulkadir ya yi kira ga maniyyatan da su kammala duk shirye-shiryen lafiyar jiki da na tafiya cikin lokacin da aka kayyade domin samun nasarar aikin Hajjin ba tare da wata tangarda ba.

 

Ali Muhammad Rabi’u

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Dalilin da manyan ’yan siyasa ke barin NNPP — APC
  • An dawo da wutar lantarki a Sifaniya da Portugal
  • Gwamnatin Yobe Na Ƙoƙarin Inganta Tsaro – Hon. Idi Gubana
  • HOTUNA: Yadda aka dawo da ’yan Najeriya 203 daga Libya
  • NAJERIYA A YAU: Dalilin karyewar farashin shinkafa a kasuwannin Najeriya
  • Hajjin 2025: Jihar Kwara Ta Fara Allurar Rigakafi Ga Maniyyata
  • Akwai Ƙarin Gishiri A Yawan  Masu Sauyin Jam’iyya Zuwa APC – El-Rufai
  • Cibiyar Yaƙi da Ta’addanci Ta Yaba Wa Gwamna Lawal Kan Matakan Yaƙi Da ‘Yan Bindiga A Zamfara
  • NAJERIYA A YAU: “Dalilin da muke sauya sheƙa zuwa jam’iyya mai mulki”
  • Tawagar ‘Yan Sama Jannati Na Shenzhou 19 Za Su Dawo Doron Kasa A Ranar Talata