Aminiya:
2025-07-13@06:14:35 GMT

Dalilin da Kwankwaso zai dawo APC — Ganduje

Published: 16th, April 2025 GMT

Shugaban jam’iyyar APC na ƙasa, Dokta Abdullahi Umar Ganduje, ya bayyana cewa ƙiris ya rage madugun jam’iyyar NNPP, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso ya dawo jam’iyyarsu ta APC.

Gamduje ya bayyana hakan ne yana mai cewa jam’iyyar NNPP ta mutu murus, kuma jana’izarta kaɗai suke jira a gudanar a nan kusa.

Gwamnatin Tarayya ta ayyana hutu ranar Juma’a da Litinin Barcelona da PSG sun tsallaka zagayen kusa da na ƙarshe a Gasar Zakarun Turai

Ganduje ya bayyana haka ne a ranar Talata yayin ziyarar da wata ƙungiya mai goyon bayan Shugaba Bola Tinubu (TSG) ta kai sakatariyar APC ta ƙasa da ke Abuja.

Ganduje ya ce APC a kodayaushe tana cikin shirin karɓar jiga-jigan ‘yan siyasa ciki har da Kwankwaso “idan har ya yanke shawarar dawowa gida.”

Ganduje ya bayyana cewa jam’iyyar NNPP ta rasa duk wani karfi da tasiri da take da shi, musamman a Jihar Kano, inda ya ce ‘yan jam’iyyar da dama sun bar ta.

Ya ce: “NNPP ta mutu. Kuma ba da jimawa ba za a birne ta. Amma abin da ya rage shi ne a haƙa kabari, kuma har an fara hakan. Muna jiran a kammala shiri ne kawai.”

A cewarsa, “Kwankwason ya fara yunƙurin dawowa APC saboda ya fahimci cewa ya rasa komai a jam’iyyar da ya tallata.”

“Ƙofa a buɗe take ga duk wanda ya shirya dawowa APC”, yana mai cewa Kwankwaso zai samu tarba mai kyau idan ya dawo gida.

“Za mu karɓe shi idan ya dawo, domin gida zai dawo,” in ji Ganduje.

Ya ƙara da cewa APC ta na ci gaba da karɓar fitattun ‘yan siyasa daga sassa daban-daban, wanda hakan ke ƙara ƙarfafa jam’iyyar a faɗin ƙasar.

Haɗakar ’yan adawa ba za ta yi tasiri ba — Ganduje

Shugaban jam’iyyar ta APC ya kuma ce haɗakar da wasu ‘yan siyasa ke ƙoƙarin yi domin ƙalubalantar Shugaba Tinubu a Zaɓen 2027 ba za ta yi tasiri ba “domin kuwa rushewa za ta yi kafin a je ko’ina.”

Ganduje ya ce: “Wannan haɗakar da ake ta surutai a kai, za ta tarwatse kafin ta gama haɗuwa. Yawancin su za su dawo cikin APC, domin sun san cewa nan ne gida.”

Ganduje ya jaddada cewa jam’iyyar APC za ta ci gaba da jan ragamar mulki a Nijeriya saboda ingantattun manufofi da kuma salon shugabancin Tinubu.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Abdullahi Umar Ganduje Sanata Rabi u Musa Kwankwaso a jam iyyar

এছাড়াও পড়ুন:

Sanatar Abuja ta sauya sheƙa zuwa ADC

Sanata Ireti Kingibe, wacce ke wakiltar Babban Birnin Tarayya, ta fice daga jam’iyyar LP zuwa ADC.

Da ta ke magana da ’yan jarida a Abuja, ta ce wannan matakin nata wani shiri ne na tunkarar babban zaɓen 2027.

Abin da ya faru tsakani na da DSS bayan kama ni — Ɗan Bello DSS ta saki Ɗan Bello bayan ta kama shi a Kano

“Ni cikakkiyar mamba ce ta ADC yanzu,” inji ta.

Da aka tambaye ta ko tana da ƙwarin gwiwa game da shugabancin ADC da haɗin gwiwar da suke ƙoƙarin ginawa, ta ce jam’iyyar na ci gaba da samun tagomashi.

Tace kowace tafiya a sannu ake binta wanda daga bisani ta ke girma.

Wasu sun nuna damuwa cewa wannan sauya sheƙar na iya sawa ta rasa kujerarta a Majalisar Dattawa.

Amma Kingibe, ta ce jam’iyyar LP yanzu ta kasu gida biyu, wanda hakan ya sa ta bar jam’iyyar bisa ga kundin tsarin mulkin ƙasa.

Ta ce: “Ina roƙonku ku karanta kundin tsarin mulki. Akwai rarrabuwar kawuna a jam’iyyar LP, kuma wannan shi ne cikakken sharaɗi da kundin tsarin mulki ya bayar na yadda mutum zai iya sauya sheƙa ba tare da hukunci ba.”

“Idan kuna so na ci gaba da zama a jam’iyyar LP, wacce daga cikin ɓangarorin biyun kuke so na zauna a ciki?

“Har INEC sai da ta samu sakamakon zaɓe daga ɓangarori biyu na LP, kodayake ba su amince da kowane ba.”

Ta ƙara da cewa: “Ko da babu irin wannan rabuwar kan, kun taɓa ganin an tilasta wa wani barin kujerarsa?

“Amma ni ina bin doka. Da babu rabuwar kawuna a LP, da ba zan sauya sheƙa ba. Amma yanzu akwai, shi ya sa kundin tsarin mulki ya ba ni dama. Kuma na zaɓi ADC.”

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tinubu ya dawo Najeriya bayan ziyarar aiki a Saint Lucia da Brazil
  • Yadda Iyaye Ke Rungumar Bokaye Don Samar Wa ‘Ya’yansu Mata Mazaje Masu Kudi
  • Sanatan Abuja ta sauya sheƙa zuwa ADC
  • Sanatar Abuja ta sauya sheƙa zuwa ADC
  • 2027: Shugabannin Hamayya Sun Bazama Neman Goyon Baya A Yankunansu
  • Dalilin Ware Naira Biliyan 19.5 Da Asusun Bunkasa Aikin Noma Ya Yi
  • Rashin Ganin Shugabannin APC Yayin Ziyarar Shettima A Kano Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara
  • Dalilin da ya sa muka gayyaci Sheikh Lawal Triumph – ’Yan sanda
  • Amurka Ta Rage Wa’adin Bizar ‘Yan Nijeriya Zuwa Wata Uku
  • Shirin Sabunta Fata Na Tinubu Yana Samar da Damarmakin Cigaba — Minista