Hizbullah Ta Yi Allawadai Da Keta Hurumin Masallacin Kudus Da ‘Yan Sahayoniya Su Ka Yi
Published: 16th, April 2025 GMT
Kungiyar Hizbullah ta kasar Lebanon ta fitar da bayani da ya kunshi yin Allawadai da keta hurumin masallacin kudus da ‘yan sahayoniya su ka yi a cikin kwanaki uku a jere.
“Yan sahayoniyar dai sun rika shiga cikin harabar masallacin na Kudus, suna yin ibadunsu na yahudanci, tare da kariyar ‘yan sandan HKI.
Kungiyar ta Hizbullah ta kuma ce; Abinda ‘yan sahayoniyar suke yi nuna kiyayya ne, da keta hurumin masallacin kudus.
Bugu da kari sanarwar ta kara da cewa; Abinda ;yan sahayoniyar suke yi, ya isa bakantawa musulmi al’ummunsu da gwmanatocinsu, ya kuma sa su yunkurawa domin hana ci gaba da abinda yake faruwa.
Hizbullah ta kuma ce; Al’ummarmu ta larabawa da musulmi tana da cikakkiyar masaniya akan bukatar a daga murya da karfi da kuma yin dukkanin abinda ya kamata domin fuskantar wannan keta hurumin, saboda yin shiru yana kara karfafa abokan gaba akan abinda suke yi a cikin Kudus, yammacin kogin Jordan, Syria da kuma Yemen.
Bayanin na kungiyar Hizbullah ya kuma yi kira ga kungiyoyin kasashen musulmi da na larabawa da kuma cibiyoyin addini da malamai ma ‘yantattu a duk duniya da su yunkura da sauri, su kuma dauki nauyin da ya rataya a wuyansu na tarihi.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Najeriya ta shigo da tataccen man fetur na tiriliyan 12.8 cikin watanni 15
Najeriya ta shigo da tataccen man fetur na Naira tiriliyan 12.8 daga watan Agustan 2024 zuwa Oktoba 2025, bisa ga bayanan da Hukumar Kula da Rarraba Man Fetur ta Najeriya (NMDPRA) ta fitar.
Hakan na zuwa ne a daidai lokacin da kasar ke ƙoƙarin ƙara samar da man fetur a cikin gida, duk kuma da aikin da matatar Dangote ke yi.
An kashe matashi yayin rikici a wajen raɗin suna a Bauchi Amurka za ta hana ’yan Najeriyar da ake zargi da yi wa Kiristoci kisan kiyashi bizaBisa amfani da matsakaicin farashin lita ɗaya na ₦829.77, an ƙididdige jimillar lita 15,435,000,000 da aka shigo da su a wannan lokaci.
Bincike ya nuna cewa mafi yawan shigo da man fetur ya kasance ne a watan Satumban 2024 lokacin da ba a samar da man ba a cikin gida, inda aka shigo da lita biliyan 1.52, sai Agusta 2024 da lita biliyan 1.38, sannan Disamba 2024 da lita biliyan 1.31.
A Oktoba 2025, an shigo da lita biliyan 1.17, sai Nuwamba da lita biliyan 1.12. Amma a Janairu 2025, adadin ya ragu sosai zuwa lita miliyan 765.7, kafin ya ɗan ƙaru zuwa lita miliyan 770 a Fabrairu, sannan miliyan 889.7 a Maris.
A Afrilu, an samu lita miliyan 861, sai kuma Mayu da ya haura zuwa 1.19 biliyan, kafin ya ragu zuwa 978 miliyan a Yuni, sannan ya ƙaru zuwa 1.11 biliyan a Yuli, kafin ya sauka zuwa 818.4 miliyan a Agusta, 663 miliyan a Satumba, da 855.6 miliyan a Oktoba.
Samarwa da mai a cikin gidaA ɓangaren samarwa a cikin gida, jimillar lita biliyan 7.2 aka samar a wannan lokaci, dukkansu daga matatar man Dangote.
Bayanan sun nuna cewa ba a samu gudunmawar samarwa daga cikin gida ba a watan Agusta 2024, amma a Satumba 2024, Dangote ya samar da lita miliyan 102, wanda ya ƙaru zuwa miliyan 300.7 a Oktoba 2024, sannan miliyan 558 a Nuwamba 2024.
Bayanan sun nuna cewa har yanzu ƙasar na dogaro sosai da shigo da man fetur duk da ƙoƙarin kawo ƙarshen shigo da shi domin tallafa wa samarwa a cikin gida.
Dangote ya sha bayyana cewa matatar man shi karfin tace ganga 650,000 a kullum na iya wadatar da Najeriya.
Sai dai masana a fannin sun ce haramta shigo da man fetur zai iya haifar da babakere a fannin, wanda suka ce bai dace da kasuwar man fetur ba a kasar.