Kungiyar Hizbullah ta kasar Lebanon ta fitar da bayani da ya kunshi yin Allawadai da keta hurumin masallacin kudus da ‘yan sahayoniya su ka yi a cikin kwanaki uku a jere.

“Yan sahayoniyar dai sun rika shiga cikin  harabar masallacin na Kudus, suna yin ibadunsu na yahudanci, tare da kariyar ‘yan sandan HKI.

Kungiyar ta Hizbullah ta kuma ce; Abinda ‘yan sahayoniyar suke yi nuna kiyayya ne, da keta hurumin masallacin kudus.

Bugu da kari sanarwar ta kara da cewa; Abinda ;yan sahayoniyar suke yi, ya  isa bakantawa musulmi al’ummunsu da gwmanatocinsu, ya kuma sa su yunkurawa domin hana ci gaba da abinda yake faruwa.

Hizbullah ta kuma ce; Al’ummarmu ta larabawa da musulmi tana da cikakkiyar masaniya akan bukatar a daga murya da karfi  da kuma yin dukkanin abinda ya kamata domin fuskantar wannan keta hurumin, saboda yin shiru yana kara karfafa abokan gaba akan abinda suke yi a cikin Kudus, yammacin kogin Jordan, Syria da kuma Yemen.

Bayanin na kungiyar Hizbullah ya kuma yi kira ga kungiyoyin kasashen musulmi da na larabawa da kuma cibiyoyin addini da malamai ma ‘yantattu a duk duniya da su yunkura da sauri, su kuma dauki nauyin da ya rataya a wuyansu na tarihi.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

’Yan Bindiga Sun Nemi Miliyan 100 Kudin Fansa Kan Kowane Mutum Ɗaya da Suka Sace a Kwara

Daga Ali Muhammad Rabi’u

‘Yan bindigar da suka sace masu ibada 38 a Cocin Christ Apostolic Church (CAC), Eruku da ke ƙaramar hukumar Ekiti a Jihar Kwara sun nemi kudin fansa na Naira miliyan 100 kan kowane mutum daya da suka sace.

Rediyon Najeriya ya ruwaito cewa masu garkuwan sun fara kiran iyalan waɗanda aka sace a cocin.

Shugaban al’umma kuma Olori Eta na Eruku, Cif Olusegun Olukotun, wanda mutane huɗu daga cikin danginsa suka kasance cikin waɗanda aka sace, ya tabbatar da hakan ga ’yan jarida.

Olukotun ya ce yana cikin coci tare da mutane biyar na danginsa lokacin da lamarin ya faru, inda ya ƙara da cewa ɗaya daga cikin yaran da yake kula da su ya tsere ta tagar cocin.

Ya tabbatar da cewa masu garkawan sun kira waya suna neman naira miliyan 100  a matsayin kudin fansa na kowanne daga cikin mutane 38 da suka sace.

Olukotun ya yi kira da a ƙara tsaro a Eruku, wanda ke kan iyaka, domin tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyin jama’a.

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ’Yan Bindiga Sun Nemi Miliyan 100 Kudin Fansa Kan Kowane Mutum Ɗaya da Suka Sace a Kwara
  • UNICEF Ta Jinjinawa Jihohin Kano, Katsina da Jigawa Bisa Inganta Rayuwar Kananan Yara
  • Shugabar Tanzania ta Naɗa ‘Yarta da Surikinta Ministoci a Ƙasar
  •  Iran Tana Cikin kasashe 10 Na Farko Da Su Ka Fi Yawan Wuraren Tarihi
  • Hizbullah: Ba Za Mu Taba Ajiye Makamanmu Ba
  • Gwamnatin Kwara ta rufe makarantu a kananan hukumomi 4 saboda matsalar tsaro
  • Wayar wutar lantarki ta kashe mutum 4 a wajen cashiya a Legas
  • Labanon Ta Bukaci Gudanar Da Taron Kwamitin Tsaro Na MDD Cikin Gaggawa
  • ‘Yadda aka harbe mijina a gabana lokacin sace daliban Kebbi’
  • Gobara ta laƙume kasuwar Katako a Gombe