Hizbullah Ta Yi Allawadai Da Keta Hurumin Masallacin Kudus Da ‘Yan Sahayoniya Su Ka Yi
Published: 16th, April 2025 GMT
Kungiyar Hizbullah ta kasar Lebanon ta fitar da bayani da ya kunshi yin Allawadai da keta hurumin masallacin kudus da ‘yan sahayoniya su ka yi a cikin kwanaki uku a jere.
“Yan sahayoniyar dai sun rika shiga cikin harabar masallacin na Kudus, suna yin ibadunsu na yahudanci, tare da kariyar ‘yan sandan HKI.
Kungiyar ta Hizbullah ta kuma ce; Abinda ‘yan sahayoniyar suke yi nuna kiyayya ne, da keta hurumin masallacin kudus.
Bugu da kari sanarwar ta kara da cewa; Abinda ;yan sahayoniyar suke yi, ya isa bakantawa musulmi al’ummunsu da gwmanatocinsu, ya kuma sa su yunkurawa domin hana ci gaba da abinda yake faruwa.
Hizbullah ta kuma ce; Al’ummarmu ta larabawa da musulmi tana da cikakkiyar masaniya akan bukatar a daga murya da karfi da kuma yin dukkanin abinda ya kamata domin fuskantar wannan keta hurumin, saboda yin shiru yana kara karfafa abokan gaba akan abinda suke yi a cikin Kudus, yammacin kogin Jordan, Syria da kuma Yemen.
Bayanin na kungiyar Hizbullah ya kuma yi kira ga kungiyoyin kasashen musulmi da na larabawa da kuma cibiyoyin addini da malamai ma ‘yantattu a duk duniya da su yunkura da sauri, su kuma dauki nauyin da ya rataya a wuyansu na tarihi.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Ministan Harkokin Wajen Mali: Ba Abu Ne Mai Yiwawa Ba ‘Yan Tawaye Su Mamaye Mali
Ministan Harkokin Wajen Mali Abdoulaye Diop ya yi watsi da ra’ayin cewa kungiyoyi masu dauke da makamai za su kwace babban birnin nan ba da jimawa ba, yana mai cewa “ba za a iya tunanin hakan ba.”
A ranar Lahadi ne Tarayyar Afirka ta yi kira da a dauki matakin gaggawa na kasa da kasa kan tabarbarewar yanayin tsaro, kuma kasashen Yamma, ciki har da Amurka, Faransa, Birtaniya, da Italiya, sun bukaci ‘yan kasarsu da su fice.
Da yake jawabi a wani taron manema labarai a wurin baje kolin a daren Laraba, Diop ya ce “Mali ta yi nasarar rage tasirin toshewar man fetur” kuma kungiyar Jama’at Nusrat al-Islam wal-Muslimin (JNIM) ba ta dace da jami’an tsaro ba. “Ba mu da nisa da yanayin da ake gaya muku a wajen kasarmu, wanda ke cewa ‘yan ta’adda suna nan, suna Bamako, kuma za su aiwatar da wannan da wancan,” in ji shi. “Ba mu cikin wannan yanayin kwata-kwata.”
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label Name* Email* Website Label Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Ramaphosa Ya Caccaki Trump Kan Kauracewa Taron G20 A Johannesburg November 14, 2025 MDD ta nuna damuwa game da rahotannin kisan gilla a El Fasher November 14, 2025 Rasha Ta yi Gargadin Mayar Da Martani Mai Tsanani Kan Amurka November 13, 2025 Iran Da Qatar Sun Tattauna Kan Dangantakar Dake Tsakaninsu November 13, 2025 Yahudawa Yan Share Wuri Zauna Sun Kona Masallaci A Yammacin Kogin Jodan November 13, 2025 Gwamnatin Najeriya Ta Dakatar Da Fara Karbar Harajin Man Fetur November 13, 2025 Iran da china Za su Yi Bikin Cika Shekaru 55 Da Huldar Diplomasiya Tsakaninsu November 13, 2025 Faransa: An Fara Shari’ar Shugaban ‘Yan Tawayen DRC Bisa Laifuna Akan Bil’adama November 13, 2025 Almayadin Ta Sami Rahoton Hukumar Makamashin Ta Duniya ( IEA) Aka Cewa Iran Tana Aiki Da Dukkanin Ka’idoji November 13, 2025 Janar Ali Fadwi: Muna Aiki Tukuru Domin Sabunta Nisan Makamanmu Masu Linzami November 13, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci