Hizbullah Ta Yi Allawadai Da Keta Hurumin Masallacin Kudus Da ‘Yan Sahayoniya Su Ka Yi
Published: 16th, April 2025 GMT
Kungiyar Hizbullah ta kasar Lebanon ta fitar da bayani da ya kunshi yin Allawadai da keta hurumin masallacin kudus da ‘yan sahayoniya su ka yi a cikin kwanaki uku a jere.
“Yan sahayoniyar dai sun rika shiga cikin harabar masallacin na Kudus, suna yin ibadunsu na yahudanci, tare da kariyar ‘yan sandan HKI.
Kungiyar ta Hizbullah ta kuma ce; Abinda ‘yan sahayoniyar suke yi nuna kiyayya ne, da keta hurumin masallacin kudus.
Bugu da kari sanarwar ta kara da cewa; Abinda ;yan sahayoniyar suke yi, ya isa bakantawa musulmi al’ummunsu da gwmanatocinsu, ya kuma sa su yunkurawa domin hana ci gaba da abinda yake faruwa.
Hizbullah ta kuma ce; Al’ummarmu ta larabawa da musulmi tana da cikakkiyar masaniya akan bukatar a daga murya da karfi da kuma yin dukkanin abinda ya kamata domin fuskantar wannan keta hurumin, saboda yin shiru yana kara karfafa abokan gaba akan abinda suke yi a cikin Kudus, yammacin kogin Jordan, Syria da kuma Yemen.
Bayanin na kungiyar Hizbullah ya kuma yi kira ga kungiyoyin kasashen musulmi da na larabawa da kuma cibiyoyin addini da malamai ma ‘yantattu a duk duniya da su yunkura da sauri, su kuma dauki nauyin da ya rataya a wuyansu na tarihi.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Gombe ta fara tantance ma’aikata don kawar da na bogi
Gwamnatin Jihar Gombe, ta fara aikin tantance ma’aikata sama da 7,000 ta hanyar Intanet domin tabbatar da bayanansu da kuma kawar da ma’aikatan bogi.
Shugabar Hukumar Kula da Ma’aikata ta Jihar (CSC), Hajiya Rabi Shu’aibu Jimeta, wacce ke jagorantar aikin, ta ce wannan shiri na nufin tabbatar da sahihancin bayanan ma’aikata.
An kashe mutum 2 a rikicin limancin masallacin Juma’a a Taraba An ceto jaririya ’yar mako daya da haihuwa da aka sayar a AnambraTa bayyana cewa za a kammala aikin cikin makonni takwas, kuma duk ma’aikatan da abin ya shafa za a ɗauki bayanansu domin sauƙaƙa samun bayanai.
Hajiya Jimeta, ta ce an keɓe ma’aikatan shari’a, hukumar malamai (Teachers Service Commission), da ma’aikatan lafiya, saboda hukumominsu na da tsarin tantancewa nasu.
Ta ƙara da cewa aikin na daga cikin shirin gyaran ma’aikata da gwamnatin jihar ke aiwatarwa domin gano ma’aikatan bogi da kuma waɗanda suka wuce lokacin ritaya.
“Bayan kammala aikin, za mu bai wa gwamnati shawara ta ɗauki sabbin ma’aikata da suka cancanta domin maye gurbin giɓin da ake da shi,” in ji ta.
A nasa jawabin, shugaban Ƙungiyar Ƙwadago (NLC) reshen Gombe, Kwamared Yusuf Ash Bello, ya yaba da matakin.
Ya ce aikin na da muhimmanci wajen tabbatar da gaskiya da inganta tsarin ma’aikata.
“Muna goyon bayan wannan aiki saboda zai samar da sahihin adadin ma’aikatan gwamnati. Ba za mu ci gaba da dogaro da bayanan bogi ko takardun bogi ba,” in ji Bello.
Wasu daga cikin ma’aikatan da aka riga aka tantance sun nuna farin cikinsu, inda suka bayyana cewa hakan zai taimaka wajen inganta hakkokinsu da ƙarin girma.