Kungiyar Hizbullah ta kasar Lebanon ta fitar da bayani da ya kunshi yin Allawadai da keta hurumin masallacin kudus da ‘yan sahayoniya su ka yi a cikin kwanaki uku a jere.

“Yan sahayoniyar dai sun rika shiga cikin  harabar masallacin na Kudus, suna yin ibadunsu na yahudanci, tare da kariyar ‘yan sandan HKI.

Kungiyar ta Hizbullah ta kuma ce; Abinda ‘yan sahayoniyar suke yi nuna kiyayya ne, da keta hurumin masallacin kudus.

Bugu da kari sanarwar ta kara da cewa; Abinda ;yan sahayoniyar suke yi, ya  isa bakantawa musulmi al’ummunsu da gwmanatocinsu, ya kuma sa su yunkurawa domin hana ci gaba da abinda yake faruwa.

Hizbullah ta kuma ce; Al’ummarmu ta larabawa da musulmi tana da cikakkiyar masaniya akan bukatar a daga murya da karfi  da kuma yin dukkanin abinda ya kamata domin fuskantar wannan keta hurumin, saboda yin shiru yana kara karfafa abokan gaba akan abinda suke yi a cikin Kudus, yammacin kogin Jordan, Syria da kuma Yemen.

Bayanin na kungiyar Hizbullah ya kuma yi kira ga kungiyoyin kasashen musulmi da na larabawa da kuma cibiyoyin addini da malamai ma ‘yantattu a duk duniya da su yunkura da sauri, su kuma dauki nauyin da ya rataya a wuyansu na tarihi.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto

Masanan sun kuma bayyana cewa, kashi 25 cikin 100 na manya a Nijeriya na dauke da kwayar cutar Sikila.

Ana bikin ranar Sikilar ne a kowace shekara, ranar 19 ga Yuni, domin wayar da kan jama’a game da cutar da kuma yadda ake sarrafa ta.

Wasu iyayen da suka bayyana irin abubuwa na renon yara masu fama da cutar, sun bayyana cewa; ba don an yaudare su da kuskuren sakamakon gwajin da aka yi musu kafin aure ba, da sun kaucewa matsalolin da suke fuskanta a halin yanzu.

Wata uwa mai ‘ya’ya uku daga unguwar Dagbana da ke babban birnin tarayya Abuja, ta bayyana wa LEADERSHIP yadda aka ba ta takardar shaidar cewa; ita da maigidanta za su iya yin aure ba tare da fuskantar wata matsala ba, inda aka gano ainahin matsayinsu a lokacin da aka gano yaronsu na karshe na dauke da cutar.

Matar, wadda ta nemi a sakaye sunanta ta ce, “Mun yi gwajin jinsin da ake bukata a yi kafin aurenmu, kamar yadda Coci ta bukata. Kazalika, nawa sakamakon ya nuna cewa, ni AA ce; shi kuma mijina AS, saboda haka; mun yi tsammanin cewa, babu wata matsala; sai ga shi yaranmu na uku an gano yana dauke da cutar, bayan mun kai ziyara asibitoci da dama; aka ce mana yaron SS ne.

Har ila yau, ta bayyana yadda abin ya faru cikin ban tausayi, tana mai nuna cewa; ba don an samu matsala tun a farko wajen yin wannan gwaji ba, da yaron nata bai shiga wannan matsala da ya samu kansa a ciki ba.

“An yi kuskure wajen yi mana namu gwajin, yanzu kuma an bar mu cikin tsanani da wahalar rayuwa”, in ji ta.  

Madam Mary Ukaibe, wata mazauniyar Nyanya a babban birnin tarayya Abuja, ita ma ta bayyana yadda ta samu sakamakon bincikenta na karya. An fada mata cewa; AA ce ita, amma gwajin da aka yi mata kwanan nan ya nuna cewa AS ce.

“Allah ya taimake ni, mijina AA ne. Amma da a ce shi ma AS ne, dukkanin mu ba mu sani ba, da za mu buge ne da haihuwar ‘ya’ya masu dauke da wannan cuta ta Sikila mai ban tsoro”, in ji ta.

Ko shakka babu, wadannan ma’aurata na daya daga cikin da dama a Nijeriya da ke fuskanta wannan matsala sakamakon kuskure ko gwaji na karya da aka yi musu. 

Dakta Ifeanyi ya shaida wa LEADERSHIP cewa, tsarin yanayin dakunan gwaje-gwajen jini, ya yi matukar tara na bogi da ma’aikatan da ba su cancanta ba da kuma na’urori marasa inganci, wanda hakan ya haifar da karuwar sakamon jinsi na karya, musamman a tsakanin ma’auratan da ke neman gwajin kafin su yi aure.

“Matsalolin da ake samu daga masu yin gwajin na bogi daga cibiyoyi da dakunan gwaje-gwaje, na taimakawa wajen karuwar haihuwar Sikila a Nijeriya. Wannan matsala ta yadu a tsakanin manya da kuma matsakaita, wadanda kan yi gwajin jinsin halittar kafin su yi aure, amma daga karshe; sai su samu sakamakon bogi ko kuma wanda ke dauke da kuskure a ciki”, in ji shi.   

A cewar tasa, an yi kuskuren sanar da ma’aurata da yawa cewa; sun dace da jinsi, daga nan sai su kai ga yin aure, sai kuma daga bisani a gano cewa; ashe abin ba haka yake ba, watakila bayan sun fara haihuwar ‘ya’ya masu ciwon Sikilar.

Shugaban AMLSN ya ce, wannan ba wai ya takaita kadai ga dakunan gwaje-gwaje masu zaman kansu ba ne, har ma da kafatanin cibiyoyin kiwon lafiya na gwamnati da masu zaman kansu, wadanda ba a tantance ba tare da na’urorin da su ma ba a tantance su ba da na jabu da kuma rashin sa ido yadda ya kamata. 

“Ni da kaina na shiga shagunan kwanan nan, don samo kayan aiki, kuma na gano cewa; yawancin samfuran da ke cikin kasuwa na bogi ne. Idan masanin harkar kamar ni, za a iya ba ni na bogi, idan ba na lura sosai ba, ina kuma ga wadanda ba su kware sun san harkar yadda ya kamata ba?”, in ji Dakta Ifeanyi.

Har ila yau, ya yi kira ga hukumomi, musamman kungiyar kimiyyar lafiya ta Nijeriya (MLSCN), da su dauki matakin gaggawa kan daidaita wadannan al’amura tare da tabbatar ganin cewa; ana aiwatar da bin ka’idoji da dukkanin tsare-tsaren da suka kamata.

A cewarsa, dole ne dukkan masana kimiyyar gwaje-gwajen lafiya a fadin tarayyar Nijeriya, su hada karfi da karfe wajen yaki da matsalar sayar da wadannan kayayyaki da suka shafi kiwon lafiya na bogi, wanda ya bayyana hakan a matsayin wata babbar barazana ga lafiyar al’umma baki-daya.

Lokacin da LEADERSHIP ta tuntubi cibiyar MLSCN, kan kokarin da take yi na dakile wannan al’amari yayin gwaje-gwaje, ta dage cewa; sai an gabatar da takarda a hukumance kafin ta yi magana kan al’amarin. 

Dakta Ifeanyi ya kuma bukaci kungiyoyi masu zaman kansu (CSOs) da cibiyoyin addini da sarakunan gargajiya, da su kara kaimi wajen wayar da kan al’umma, kan illolin da ke tattare da auren da za a iya kamuwa da wannan cuta ta Sikila.

Yayin da yake amincewa da ci gaban da aka samu wajen tilasta yin gwaje-gwaje kafin a kai ga yin aure ya ce; ana ci gaba da samun raguwar yaduwar cutar a duk shekara.  

“Dole ne mu sake gina al’ummarmu, musamman ta hanyar wayar da kan jama’a game da kimiyya da fasaha da kuma ingantaccen tsarin gwaje-gwajen da ya kamata kowa ya yi”, in ji shi.

A nasa bangaren, mataimakin daraktan sashen kula da gwaje-gwaje a babban asibitin kasa na Abuja, Anthony Ilegogie ya gargadi ‘yan Nijeriya kan dogaro da dakunan da ba su da inganta ko na bogi, domin yin wannan gwaje-gwaje na kawayar halittar Dan’adam, yana mai jaddada cewa; yanayin halittar mutum ba ya canzawa, sannan kuma bai kamata bayan an yi gwaji na gaskiya a sake komawa ya ce za a sake yin wani ba.

A yayin da yake magana kan batun kura-kuren da ake samu dangane da sakamakon gwajin kwayar halittar, Ilegogie ya fayyace cewa; irin wannan matsala na faruwa ne sakamakon rashin horar da ma’aikata da rashin kayan aiki a dakunan gwaje-gwajen da ake da su.  

 “Mutane iri daban-daban, kan shiga wannan harka ko kasuwanci na harkar gwaje-gwajen jini, inda a karshe bayan mara lafiya ya fada hannunsu, sai su buge da ba shi sakamako na karya ko mara kyau”, kamar yadda Ilegogie ya yi gargadi.  

Sannan ya kuma kara da cewa, hanyoyin gwaji na zamani a halin yanzu, sun banbanta da wadanda ake amfani da su a da, domin kuwa yanzun an dogara ne da ingantattun na’urori na zamani da fasahohi, wadanda ke bayar da sakamakon da ake bukata daidai-wadaida. 

LEADERSHIP ta gano cewa, Nijeriya ce kasa mafi dauke da wannan cuta a duk fadin duniya, inda kashi 25 cikin 100 na manya ke dauke da kwayar cutar Sikila tare kuma da kamuwar jarirai kusan 150,000 a duk shekara, wanda hakan ke nuni da cewa; kusan kashi takwas cikin 100 na mace-macen jarirai a kasar na afkuwa.

A cewar mashawarciya ta musamman kan cutar Sikila ga ministan lafiya ta kasa, Farfesa Obiageli Nnodu, a halin yanzu kimanin ‘yan Nijeriya miliyan hudu ne ke dauke da wannan cuta ta Sikila.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ‘Yan Bindiga Sun Sake Kai Hari Kan Al’ummar Benuwe, Sun Kashe ‘Yansanda 4
  • Murabus Ɗin Ganduje: ‘Yan Kwankwasiyya Na Shirin Ɗaukar Wani Mataki
  • 2027: Ƴan Adawa Na Ƙara Ƙaimin Kawar Da Tinubu
  • Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto
  • Sheikh Na’im Kasim: Muna Da Karfin Ci Gaba Da Bugawa Da Abokan Gaba
  •   Ka’a’ni: Nasarar Da Mu Ka Samu Za Ta Ci Gaba Da Dorewa
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Jaddada Matsayin Kasarsa Na Rashin Mika Wuya Ga ‘Yan Kama Karya
  • Mummunan Hatsari Ya Lashe Rayukan ‘Yan Mata 18 A Kasar Masar Dukkaninsu ‘Yan Kasa DA Shekara 21
  • Ƙungiyar Lauyoyi Musulmi Reshen Kaduna Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Matafiya A Filato
  • Indomie Ta Kaddamar Da Shirin Gangamin Abinci Mai Gina Jiki Na ‘Ingantaccen Abinci Domin Nasara’