Kungiyar Hizbullah ta kasar Lebanon ta fitar da bayani da ya kunshi yin Allawadai da keta hurumin masallacin kudus da ‘yan sahayoniya su ka yi a cikin kwanaki uku a jere.

“Yan sahayoniyar dai sun rika shiga cikin  harabar masallacin na Kudus, suna yin ibadunsu na yahudanci, tare da kariyar ‘yan sandan HKI.

Kungiyar ta Hizbullah ta kuma ce; Abinda ‘yan sahayoniyar suke yi nuna kiyayya ne, da keta hurumin masallacin kudus.

Bugu da kari sanarwar ta kara da cewa; Abinda ;yan sahayoniyar suke yi, ya  isa bakantawa musulmi al’ummunsu da gwmanatocinsu, ya kuma sa su yunkurawa domin hana ci gaba da abinda yake faruwa.

Hizbullah ta kuma ce; Al’ummarmu ta larabawa da musulmi tana da cikakkiyar masaniya akan bukatar a daga murya da karfi  da kuma yin dukkanin abinda ya kamata domin fuskantar wannan keta hurumin, saboda yin shiru yana kara karfafa abokan gaba akan abinda suke yi a cikin Kudus, yammacin kogin Jordan, Syria da kuma Yemen.

Bayanin na kungiyar Hizbullah ya kuma yi kira ga kungiyoyin kasashen musulmi da na larabawa da kuma cibiyoyin addini da malamai ma ‘yantattu a duk duniya da su yunkura da sauri, su kuma dauki nauyin da ya rataya a wuyansu na tarihi.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

An kashe mutum 11 da jikkata wasu 29 a bikin Yahudawa a Ostireliya 

Akalla mutanen 11 ne suka mutu, wasu 29 suka jikkata, a yayin wani hari da aka kai a bakin tekun  Bondi Beach da ke birnin Sydney na ƙasar Ostireliya. 

’Yan bindiga sun kai harin ne a yayin da dubban jama’a ne suka taru a bakin teku domin halartar wani biki mai suna ‘Chanukah by the Sea’, wanda ke nuna fara shagulgulan Yahudawa na Hanukkah.

Rahotanni sun ce wani mutum da ake zargin ɗaya daga cikin masu harin ya mutu, yayin da wani kuma ke cikin mawuyacin hali a asibiti. ’Yan sanda biyu na cikin mutanen da suka jikkata.

Hukumomin Ostireliya sun bayyana lamarin a matsayin harin ta’addanci, tare da jaddada cewa an shirya shi ne domin kai wa al’ummar Yahudawa hari a ranar farko ta bukukuwan Hanukkah.

Taɓarɓarewar rashin tsaro ya nuna rashin shugabanci na gari — Obi Akwai fargaba kan noman ranin bana

Firaministan Ostireliya, Anthony Albanese, ya yi Allah-wadai da harin, tare da cewa mummunan ta’addanci da aka aikata ya wuce tunanin ɗan adam.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Masu Tsatsauran Ra’yi Suna Kokarin Kaiwa Masu Hijira Da Musulmi A Ingila
  • Sudan: Makaman ‘Drones’ Sun Kashe Ma’aikatan MDD 6 A Kadugli Na Kurdufan Ta Kudu
  • An kashe mutum 11 da jikkata wasu 29 a bikin Yahudawa a Ostireliya 
  • Sheikh Na’im Kassim: Idan Duniya Baki Daya Za Ta Taru, Ba Wanda Zai Iya Kwace Makaman Hizbullah
  • Syria: Sojojin “Isra’ila” Sun Kutsa Cikin Yankin Qunaidhara
  • Abubuwan Da Ba Ku Ji Ba Kan Rasuwar Sheikh Dahiru Bauchi
  • Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan(a) 171
  • Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan(a) 170
  • Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan(a) 169
  • Isra’ila Ta Kai Hari A Kudancin Labanon  A Ci Gaba Da Keta Yarjejeniyar Tsagaita Bude Wuta