A wani taron manema Labarai a nan birninTehran, kakakin sojojin kasa na dakarun IRGC a nan JMI,  Burgediya Janar Ali Muhammad Naeini ya fadawa yan jaridu cewa, tsaron JMI da kuma makamanta baa bin tattaunawa ne da makiya ba. Ya kuma kara da cewa, tsaron kasar Iran jan layi ne,  haka ma, karfin sojojin kasar.

Janar Naeini ya ka ra da cewa, rawar dajin da sojojin IRGC suka yi a baya-bayan nan ya na tabbatar da hakan.

Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya bayyana cewa, Burgediya Janar Naeini yana maida martani ne ga gwamnatin Amurka wace ta fara maganar cewa, zata tattauna da kasar ta Iran ne a kan shirinta na makamai masu linzami, da kuma shirin ta na makamashin nukliya.

Kakakin sojojin ya bayyana cewa a dai dai lokacinda JMI take amfani da diblomasiyya a dayan bangaren kuma ta na da makamanta a kan teburi idan har diblomasiyya ta kasa kai kasar ga zaman lafiya da makiya zata yi amfani da su.

Kafin haka dai jakadan Amurka na musamman a gabas ta tsakiya, Steve Witkoff ya fadawa tashar talabijin ta Fox news ta kasar Amurkan kan cewa a tattaunawar da ya fara da jami’an gwamnatin kasar Iran, yana fatan  zasu tattauna kan shirinta na makamashin Uranium da kuma, yiyuwar ta kera makaman nukliya,  har’ila yau da kuma tarin makamai masu linzami da take da su.

Kakakin dakarun na IRGC ya ce hare-haren wa’adus Sadik na daya da na biyu, kekyawar misali ne na nuna karfin makaman linzami na kasar, sannan  mutanen kasar suna goyon bayan gwamnati a kan mallakar wadannan makamai.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Ministan Tsaro Na Kasar Iran ya bada Labarin Gwajin Wani Sabom Makami Mai Limzami Mai Daukar abubuwan Fashewa Har Ton Biyu

Ministan tsaro na kasar Iran ya bayyana cewa sojojin kasar sun yi gwajin wani makami mai linzami wanda yake iya daukar abubuwan fashewa hart un biyu.

Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto Burgediya Janar Amir Nasirzade yana fadar haka. Ya kuma kara da cewa . wannan gwajin sako ne ga gwamnatin Amurka da kawayenta. Idan wani ya dora mana yaki sai sun fi mu shan wahali. Don tare da wadannan shirye shiryen da kuke na kare kammu sai mun kori amurka daga yankin nan.

Yace iran tana cikin fushi kan abinda yake faruwa a Gaza don haka duk wata dama da ta samu zata maida martanin da ya dace. Ministan ya bayyana haka ne a jiya Laraba bayan taron Majalisar ministoci tare da shugaban kasa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Arakci: Babu Wani Dalili Na Ci Gaba Da Tattaunawa Tsakanin Iran Da Amurka
  • Jami’in Hamas Ya Jinjinawa Iran Kan Kakkausan Martanin Da Ta Mayar Kan Haramtacciyar Kasar Isra’ila
  • Iran, ta yi wa Isra’ila ruwan makamai masu linzami
  • Jagora: Sojojin Iran ba zasu sararawa Isra’ila ba
  • IRGC : Iran a shirye take na tunkarar duk wani yanayi
  • Ranar Tattaunawa Tsakanin Wayewar Kan Kasa Da Kasa: Sabon Tunani Don Wanzar Da Zaman Lafiya Da Daidaito A Duniya
  • Salami: Babu Inda Ba Za Mu Iya Kai Wa Hari Ba A Fadin HKI
  •   Bokoharam Ta Kashe Sojojin Kamaru Ta Hanyar Amfani Da Jirgin Sama Maras Matuki
  • Ministan Tsaro Na Kasar Iran ya bada Labarin Gwajin Wani Sabom Makami Mai Limzami Mai Daukar abubuwan Fashewa Har Ton Biyu
  • Ministan man Fetur na Kasar Iran Yace Amurka Ta Kasa Hana Iran Saida Danyen Man Fetur Na Kasar