A wani taron manema Labarai a nan birninTehran, kakakin sojojin kasa na dakarun IRGC a nan JMI,  Burgediya Janar Ali Muhammad Naeini ya fadawa yan jaridu cewa, tsaron JMI da kuma makamanta baa bin tattaunawa ne da makiya ba. Ya kuma kara da cewa, tsaron kasar Iran jan layi ne,  haka ma, karfin sojojin kasar.

Janar Naeini ya ka ra da cewa, rawar dajin da sojojin IRGC suka yi a baya-bayan nan ya na tabbatar da hakan.

Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya bayyana cewa, Burgediya Janar Naeini yana maida martani ne ga gwamnatin Amurka wace ta fara maganar cewa, zata tattauna da kasar ta Iran ne a kan shirinta na makamai masu linzami, da kuma shirin ta na makamashin nukliya.

Kakakin sojojin ya bayyana cewa a dai dai lokacinda JMI take amfani da diblomasiyya a dayan bangaren kuma ta na da makamanta a kan teburi idan har diblomasiyya ta kasa kai kasar ga zaman lafiya da makiya zata yi amfani da su.

Kafin haka dai jakadan Amurka na musamman a gabas ta tsakiya, Steve Witkoff ya fadawa tashar talabijin ta Fox news ta kasar Amurkan kan cewa a tattaunawar da ya fara da jami’an gwamnatin kasar Iran, yana fatan  zasu tattauna kan shirinta na makamashin Uranium da kuma, yiyuwar ta kera makaman nukliya,  har’ila yau da kuma tarin makamai masu linzami da take da su.

Kakakin dakarun na IRGC ya ce hare-haren wa’adus Sadik na daya da na biyu, kekyawar misali ne na nuna karfin makaman linzami na kasar, sannan  mutanen kasar suna goyon bayan gwamnati a kan mallakar wadannan makamai.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Za’a Gudanar Da Tattaunawa Zagaye Na 5 Tsakanin Amurka Da Iran A Ranar 23-Afrilu A Roma

Ministan Harkokin wajen kasar Omman ya bada sanarwan cew za’a gudanar da tattaunawa zagaye na 5 tsakanin Iran da Amurka kan shirin Iran na makamshin nukliya a ranar 23 gawatan Mayun da muke ciki a birnin Roma nakasar Italiay.

Tashar talabijin ta Presstv a nnan Tehran ta ce Har yanzun ba’a ji tabakin kasashen biyu ba bayan wannan sanarwan.

Sai dai kafin haka Iran tace tana tunanin dakatar da halattan taron saboda yadda jami’an gwamnatin kasar Amurka suka bayyana cewa duk wata yarjeniya da Iran sai ta hada da hana ta tace Uranium.

Amma iran ta dage kan cewa ba zata bar hakkinta wanda yarjeniyar NPT ta bata ba na tashe Uranium karkashin kula na hukumar IAEA ba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Za’a Gudanar Da Tattaunawa Zagaye Na 5 Tsakanin Amurka Da Iran A Ranar 23-Afrilu A Roma
  • An Tattauna Hanyar Zamanantar Da Kasa A Dandalin Tattaunawa Na Masanan Sin Da Afirka
  • Sharhin Bayan Labarai: Iran Zata Ci Gaba Da Tashe Uranium Tare Da Yarjeniya Ko Babu Ita
  • Sojojin Sudan Sun Gama Tsarkaka Birnin Khartoum Daga ‘Yan Tawayen Rapid Support Forces
  • Sojojin Sudan Sun Sanar Da Kammala “Tsarkake” Birnin Kahartum Daga Dakarun  RSF
  • Ana Kara Samun Karuwar Sojojin HKI Da Suke Kashe Kansu
  • ‘Yan Gwagwarmayar Falasdinawa Sun Halaka Sojojin Sahayoniyya Tare Da Jikkata Wasu A Beit Lahiya
  • Tattalin Arzikin Kasar Sin Ya Bunkasa Duk Da Matsaloli Da Dama
  • Shugaba Kasar Lebanon Ya Ce Kungiyar Hizbullah Bata Da Zabi Sai Abinda Gwamnati Ta fada
  • Sharhin Bayan Labarai: Dandalin Tattaunawa Na Tehran