A cewar Ministan, samun wannan ƙwarewar ya zama wajibi a wannan zamani da kowa da kowa – wato daga masana hulɗa da jama’a zuwa shugabannin kamfanoni – yake taka rawa a matsayin mai magana da yawun wani.

 

Idris ya ce: “Yau a wannan zamani da kowa ke zama mai magana da yawu – ko ɗan hulɗa da jama’a ne ko shugaban kamfani a ɓangaren gwamnati da masu zaman kan su – wajabcin samun ilimi kan kafofin watsa labarai ya zama abu mai matuƙar muhimmanci, domin yana ba da damar fahimta, nazari da tantance sahihancin saƙonnin da ke yawo a kafafen watsa labarai, wanda hakan zai ba da damar yanke sahihin hukunci da mu’amala da labarai yadda ya kamata.

 

“A ‘yan kwanakin nan, saboda rashin wannan ilimi – wato rashin iya nazarin abin da ke cikin kafafen labarai da tantance sahihancin sa – jami’an gwamnati da ma al’umma gaba ɗaya sun fara faɗawa tarkon labaran ƙarya da yaɗa bayanan da ba su da tushe.”

 

Ya ce samun wannan ilimi zai ba da dama ga masu magana da yawun hukumomi su inganta dabarun su wajen tantance sahihancin labarai, gano son zuciya ko ɓangaranci a cikin su, da kuma amfani da hanyoyin bincike da tantance gaskiya.

 

Domin cimma wannan buri, Ministan ya bayyana cewa ma’aikatar sa ta kusa kammala shiri domin buɗe Cibiyar Ilimin Kafofin Watsa Labarai ta UNESCO – wacce za ta kasance ta farko a duniya – a Buɗaɗɗiyar Jami’ar Ƙasa ta Nijeriya (NOUN) da ke Abuja.

 

Ya ce: “Na dawo daga Paris, a ƙasar Faransa, kwanan nan inda na gana da manyan jami’an UNESCO, kuma buɗe wannan cibiyar ya kasance babban maudu’i a tattaunawar.”

 

Ministan ya kuma bayyana cewa ma’aikatar sa ta samu gagarumar nasara a bara, inda aka samar da sabon matsayi na “public relations” a cikin tsarin aikin Gwamnatin Tarayya.

 

“Abin da wannan ke nufi shi ne, ‘Public Relations’ yanzu yana da nasa hanyar aikin kai-tsaye a cikin aikin gwamnati tun daga watan Disamba 2023.

 

“Haka nan, tsohuwar muƙamin ‘Information Officer’ yanzu an sake masa suna zuwa ‘Information and Public Relations Officer’, da kuma ‘Executive Officer (Information and Public Relations)’.

 

“Ina kuma so in ƙara da cewa NIPR ce ta taka rawar gani wajen ganin wannan cigaba ya samu.”

 

Idris ya kuma jaddada cewa gwamnatin Tinubu za ta ci gaba da goyon bayan ‘yancin faɗar albarkacin baki da kuma ƙarfafa kafafen watsa labarai masu zaman kansu.

 

Ya ce: “A ɓangaren mu, za mu ci gaba da faɗaɗa hanyoyin sadarwa a ƙasar nan da kuma bunƙasa damar zuba jari da tattalin arziki da ke cikin ta.”

 

Har ila yau, Ministan ya yaba wa shugaban NIPR, Dakta Ike Neliaku, saboda ƙara sabon ɓangare mai muhimmanci a wannan taro, wato ‘Information Ministerial Clinic’, inda tsofaffin ministocin yaɗa labarai suka raba gogewar da suka samu da abubuwan da suka fuskanta yayin gudanar da aikin su.

 

Tsofaffin ministocin da suka halarci buɗaɗɗen taron sun haɗa da Farfesa Jerry Gana, Cif John Nwodo, Mista Frank Nweke (Jnr), Mista Labaran Maku, da Alhaji Lai Mohammed.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Yadda za ku cike neman aikin jami’an lafiya a Hajjin 2026 da NAHCON

Hukumar Aikin Hajji ta Ƙasa (NAHCON) ta fara ɗaukar likitoci da sauran ma’aikatan lafiya domin aikin Hajji da ke tafe a ƙasar Saudiyya.

Hukumar NAHCON ta bayyana cewa shafin neman aikin ya fara aiki daga ƙarfe 11 na dare ranar Juma’a 12 ga Nuwamba, 2025. Za a rufe shafin da ƙarfe 11.59 ranar Litinin, 15 ga watan Disamba, 2025

Latsa nan domin shiga shafin ɗaukar ma’aikatan lafiyan kai-tsaye.

NAHCON ta bayyana cewa jami’an lafiyan da za a ɗauka Su ƙunshi likitoci, masu haɗa magunguna, malaman jinya, da jami’an kula da lafiyar lafiya da ta muhalli (CHO/EHO). Su ne za su yi aikin kula da lafiyar alhazai a yayin aikin Hajjin na shekarar 2026.

NAHCON ta bayyana cewa jami’an da suka yi aiki da ita a matsayin kula da lafiyar alhazai a  shekaru uku da suka gabata (2023 zuwa 2025) ba ne kaɗai za a ɗauka domin wannan aiki na 2026.

Yadda za ku nemi aikin

Masu nema za su shiga shafinta kai-tsaye domin ganin ka’idodin da kuma cike bayanansu. Latsa nan domin lafiyan kai-tsaye.

Ko kuma su gaida babban shafinta daga nan su latsa wasu layuka huɗu da ke hannun dama daga sama.

Daga daga nan su latsa RESOURCES, sai su latsa su shiga NMT Application Portal.

A ciki za su ga ka’idodin neman aikin, su cike bayansu, da kuma sauke duk dakardun da su cike.

Hukumar NAHCON ta bayyana cewa daga bisani za a tuntuɓi duk waɗanda suka yi nasara.

Allah Ya ba da sa’a.

Ka’idodin neman aikin

NAHCON ta jaddada cewa:

– Ma’aikatan lafiya da suka cancanta ne kawai za su iya nema aikin ba Tawagar Lafiya ta Ƙasa (NMT) domin aikin Hajjin 2026

– Aikin NMT na 2026 zai gudana ne bisa tsarin sa-kai, bisa ƙa’idojin duniya da NAHCON ta amince da su.

– Bayanai da aka bayar za su taimaka wajen tantance cancanta da shirin shiga matakin gaba na tantancewa ko jarabawa.

– Duk bayanan da aka gabatar za a duba su. Duk wani kuskure. Ɓoye gaskiya, ko ƙirƙirar bayanan ƙarya zai iya jawo ƙin amincewa da aikace-aikacen ko cirewa daga jerin waɗanda cancanta.

– Wannan aikace-aikacen kyauta ne gaba ɗaya. NAHCON ba ta karɓar kuɗi kai tsaye ko a kaikaice, ko ta hannun wakilai ko hukumomi. Ku yi hattara!

– Cika fom ɗin ba ya nufin an amince da cancanta ko zaɓen ku.

 

Ƙa’idar shekaru:

– Likitoci: 27 zuwa 60 shekara

– Masu haɗa Magunguna: shekara 26 zuwa 60

– Nas da sauran rukuni: 22–60 shekara .

Sharuɗɗa

Dole masu neman shiga NMT su kasance:

1. Suna aiki a lokacin neman shiga.

2. Ba su halarci ayyukan NMT a shekara uku da suka gabata ba (2023, 2024, da 2025).

3. Su kasance a shirye su yi aiki na tsawon kwanaki 28 da kuma zama a Saudiyya har zuwa kwanaki 45 kafin dawowa Najeriya.

4. Ba za a sallame su a wurin aikinsu ba kafin su kammala aikin NMT.

5. Su nuna kyawawan halaye tare da bin ƙa’idojin aikin lafiya da na NAHCON.

6. Su gabatar da tabbacin mai tsaya musu (guarantor).

 

Sharuɗɗan Guarantor:

– Dole ya kasance mutum mai daraja: Ma’aikacin gwamnati (ba ƙasa da GL 15), basaraken gargajiya, Alƙali (Magistrate), ko Shugaban Ƙaramar Hukuma.

– Dole ya san mai neman aikin NMT tsawon aƙalla shekaru biyar kuma ya tabbatar da gaskiya, ƙwarewa, da iya aikinsa.

– Dole ya gabatar da kwafin katin shaida ko wata takardar shaida da ake amfani da ita a ofisoshin gwamnati na Najeriya.

 

Takardun da dole a haɗa da su:

– Fom ɗin Guarantor da aka cika

– Takardar shaidar ƙwarewar aiki (Basic Professional Certificate)

– Takardar NYSC (idan ta shafi mai nema)

– Lasisin aikin lafiya na wannan shekara

– Hoton fasfo (mai farin baya)

– Sanarwar mai nema (applicant’s declaration)

– Takardar izini daga wurin aiki (employer’s clearance letter) .

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Wacce Kasa Ce Za Ta Lashe Gasar Kofin Afirka
  • Yadda za ku cike neman aikin jami’an lafiya a Hajjin 2026 da NAHCON
  • Tinubu Ya Yaba Wa Jami’an Tsaro Kan Ceto Dalibai 100 Da Aka Sace A Neja
  • NLC Ta Shirya Zanga-Zangar Rashin Tsaro A Faɗin Ƙasa Ranar 17 Ga Disamba
  • Ƴan Bindigar Daji: Jihohin Arewa 7 Sun Kaddamar Da Rundunar Fatattakar Su
  • ‘Yan Siyasa Ne Ke Zagon Ƙasa Ga Ci Gaban Nijeriya — Sarki Sanusi II
  • Mahajjata 2,235 Ne Suka Yi Rijistar Aikin Hajjin 2026 A Sokoto
  • NAJERIYA A YAU: Alfanu Da Kalubalen Sabon Jadawalin Karatun Makarantu Da Gwamnati Ta Bijiro Dashi
  • Gwamnan Kano ya naɗa mace ta farko a matsayin shugabar Jami’ar Northwest
  • EFCC ta tsare tsohon ministan ƙwadago, Chris Ngige