Minista Ya Gargaɗi Jami’an Gwamnati Kan Rashin Sanin Ilimin Tantance Ingantattun Labarai
Published: 16th, April 2025 GMT
A cewar Ministan, samun wannan ƙwarewar ya zama wajibi a wannan zamani da kowa da kowa – wato daga masana hulɗa da jama’a zuwa shugabannin kamfanoni – yake taka rawa a matsayin mai magana da yawun wani.
Idris ya ce: “Yau a wannan zamani da kowa ke zama mai magana da yawu – ko ɗan hulɗa da jama’a ne ko shugaban kamfani a ɓangaren gwamnati da masu zaman kan su – wajabcin samun ilimi kan kafofin watsa labarai ya zama abu mai matuƙar muhimmanci, domin yana ba da damar fahimta, nazari da tantance sahihancin saƙonnin da ke yawo a kafafen watsa labarai, wanda hakan zai ba da damar yanke sahihin hukunci da mu’amala da labarai yadda ya kamata.
“A ‘yan kwanakin nan, saboda rashin wannan ilimi – wato rashin iya nazarin abin da ke cikin kafafen labarai da tantance sahihancin sa – jami’an gwamnati da ma al’umma gaba ɗaya sun fara faɗawa tarkon labaran ƙarya da yaɗa bayanan da ba su da tushe.”
Ya ce samun wannan ilimi zai ba da dama ga masu magana da yawun hukumomi su inganta dabarun su wajen tantance sahihancin labarai, gano son zuciya ko ɓangaranci a cikin su, da kuma amfani da hanyoyin bincike da tantance gaskiya.
Domin cimma wannan buri, Ministan ya bayyana cewa ma’aikatar sa ta kusa kammala shiri domin buɗe Cibiyar Ilimin Kafofin Watsa Labarai ta UNESCO – wacce za ta kasance ta farko a duniya – a Buɗaɗɗiyar Jami’ar Ƙasa ta Nijeriya (NOUN) da ke Abuja.
Ya ce: “Na dawo daga Paris, a ƙasar Faransa, kwanan nan inda na gana da manyan jami’an UNESCO, kuma buɗe wannan cibiyar ya kasance babban maudu’i a tattaunawar.”
Ministan ya kuma bayyana cewa ma’aikatar sa ta samu gagarumar nasara a bara, inda aka samar da sabon matsayi na “public relations” a cikin tsarin aikin Gwamnatin Tarayya.
“Abin da wannan ke nufi shi ne, ‘Public Relations’ yanzu yana da nasa hanyar aikin kai-tsaye a cikin aikin gwamnati tun daga watan Disamba 2023.
“Haka nan, tsohuwar muƙamin ‘Information Officer’ yanzu an sake masa suna zuwa ‘Information and Public Relations Officer’, da kuma ‘Executive Officer (Information and Public Relations)’.
“Ina kuma so in ƙara da cewa NIPR ce ta taka rawar gani wajen ganin wannan cigaba ya samu.”
Idris ya kuma jaddada cewa gwamnatin Tinubu za ta ci gaba da goyon bayan ‘yancin faɗar albarkacin baki da kuma ƙarfafa kafafen watsa labarai masu zaman kansu.
Ya ce: “A ɓangaren mu, za mu ci gaba da faɗaɗa hanyoyin sadarwa a ƙasar nan da kuma bunƙasa damar zuba jari da tattalin arziki da ke cikin ta.”
Har ila yau, Ministan ya yaba wa shugaban NIPR, Dakta Ike Neliaku, saboda ƙara sabon ɓangare mai muhimmanci a wannan taro, wato ‘Information Ministerial Clinic’, inda tsofaffin ministocin yaɗa labarai suka raba gogewar da suka samu da abubuwan da suka fuskanta yayin gudanar da aikin su.
Tsofaffin ministocin da suka halarci buɗaɗɗen taron sun haɗa da Farfesa Jerry Gana, Cif John Nwodo, Mista Frank Nweke (Jnr), Mista Labaran Maku, da Alhaji Lai Mohammed.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Shirye-shiryen Shugaba Tinubu Suna Buɗe Hanyar Farfaɗowar Tattalin Arzikin Nijeriya – Minista
Ya ƙara da cewa, “Kuma wajibi ne a gare mu, a matsayin mu na ƙwararrun ma’aikatan hulɗa da jama’a, mu daidaita da wannan lokaci ta hanyar amfani da dabarun sadarwa masu ɗauke da ƙwarewa, ƙima, da haɗin kai, domin ƙarfafa gwiwar al’ummar mu, a gida da waje, su shiga cikin farfaɗo da tattalin arzikin wannan babbar ƙasa.”
Idris ya bayyana cewa aikin sake fasalin tattalin arziki ya faro ne tun daga ranar farko da Shugaban Ƙasa Tinubu ya hau mulki, lokacin da aka cire tallafin man fetur da kuma daidaita farashin musayar kuɗi — matakan da ya bayyana a matsayin “tushen farfaɗowar tattalin arzikin ƙasar nan.”
Ya haƙƙaƙe da cewa waɗannan matakai sun haifar da wahalhalu da farko, amma yanzu an fara ganin alfanun su, ciki kuwa har da daidaituwar musayar kuɗi, da ƙaruwar kuɗaɗen shiga ga jihohi, da farfaɗowar masana’antun tace mai, da kuma ƙarfafa matsayin kuɗin gwamnati.
Yayin da gwamnatin Tinubu take da da cika shekara biyu, ministan ya bayyana cewa ‘yan Nijeriya suna ganin gagarumin zuba jari da ake yi a harkar ababen more rayuwa, noma, tsaro, da bunƙasa rayuwar ɗan’adam.
A cewar sa, an ware naira tiriliyan 2.5 don ayyukan gina manyan hanyoyi a 2025 — adadin da ya fi na kowanne lokaci a tarihin Nijeriya.
Ya kuma bayyana ƙirƙirar sababbin ma’aikatu na bunƙasa yankuna da na kiwon dabbobi, domin ƙara bunƙasa arzikin ƙasa da noma da aka yi, da kuma ƙaddamar da shirin lamuni na NELFUND wanda ya taimaka wa ɗaliban Nijeriya sama da 300,000 da kuɗin karatu da gudanar da rayuwar su.
Daga cikin sauran muhimman ayyuka da ministan ya lissafa akwai shirin Shugaban Ƙasa na amfani da iskar gas ta CNG a motoci wanda ya jawo zuba jari kai-tsaye na fiye da dalar Amurka miliyan 450; da kafa CreditCorp domin bai wa ‘yan Nijeriya damar samun rance don gina gidajen su da kula da lafiyar su; da kuma ware naira biliyan 200 don tallafa wa ƙananan ‘yan kasuwa, ƙananan sana’o’i (SMEs) da manyan masana’antu.
Ya ƙara da cewa: “Yanzu haka Nijeriya ta zama wani gagarumin wurin gine-gine, inda aka kasafta sama da naira tiriliyan 2.5 don gudanar da ayyukan hanyoyi a wannan shekara kaɗai — wanda hakan bai taɓa faruwa ba a tarihin ƙasar nan.
“Gwamnati tana haɗa birane ta hanyar manyan ayyuka irin su hanyar Legas zuwa Kalaba da wata hanyar daga Badagry zuwa Sakkwato, da sauran sassa na ƙasa.
“Akwai sauran ayyuka da dama da ke gudana yanzu haka. Daga farfaɗowar matatun mai na Fatakwal da Warri, zuwa amincewa da a kashe naira biliyan 80 don sake gina dam ɗin Alau da ke Jihar Borno, zuwa ci gaban aikin gina layin dogo na zamani daga Kano zuwa Kaduna — babu wani yanki na ƙasar da aka bari a baya a cikin wannan babban zuba jari a ababen more rayuwa ƙarƙashin Shugaban Ƙasa Tinubu, wanda yanzu ake kira ‘The Road Master.’”
Ministan ya kuma nuna wasu alamomin da ke nuna bunƙasar tattalin arziki inda ya ce, “Ma’aunin Canjin Farashin Kayayyaki (CPI) na watan Afrilu 2025, wanda Hukumar Ƙididdiga ta Ƙasa ta fitar kwanan nan, ya nuna cewa hauhawar farashi ya tsaya a kashi 23.71, wanda an samu raguwar kashi 0.52 daga kashi 24.23 da aka samu a watan Maris. Wannan bai faru ba sai saboda tsare-tsaren Shugaban Ƙasa, waɗanda yanzu haka sun fara bayyana kuma suna haifar da ɗa mai ido.”
Idris ya buƙaci ƙwararrun masanan hulɗar jama’a da su taka rawar gani wajen gina da kuma nuna sabuwar martabar tattalin arzikin Nijeriya ga duniya.
“Nijeriya tana bunƙasa!” inji shi. “Nijeriya ta jawo fiye da dalar Amurka biliyan 50 na sababbin hannun jari kai-tsaye daga ƙasashen waje, kuɗin da ‘yan Nijeriya suke turowa daga ƙetare sun kai dala biliyan 21.9, kuma masana’antar finafinai (Nollywood) ta bayar da gudunmawar fiye da naira biliyan 730 ga haɓakar tattalin arziki (GDP).
“Waɗannan ba ƙididdiga ba ne kawai — su ne labarai da suke buƙatar a bada su ta hanya mai kyau, bisa ƙwarewa, kuma cikin ƙaunar ƙasa.”
Idris ya jaddada cewa ma’aikatar sa za ta ci gaba da inganta saƙonnin ƙasa ta hanyar sabon tsarin sadarwa na ƙasa mai suna National Strategic Communication Framework (NSCF).
Ya kuma taya Shugaban Hukumar NIPR, Dakta Ike Neliaku, murna bisa zaɓen sa a matsayin Wakilin Lardi na Musamman (Regional Delegate-at-Large) na ƙungiyar Global Alliance for PR and Communication Management.
Ya ce: “Ina taya ka murna, ya Shugaban mu, bisa wannan gagarumar nasara. A ƙarƙashin jagorancin ka, aikin hulɗar jama’a ya samu ƙarin daraja sosai a gida da wajen Nijeriya.”
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp