Minista Ya Gargaɗi Jami’an Gwamnati Kan Rashin Sanin Ilimin Tantance Ingantattun Labarai
Published: 16th, April 2025 GMT
A cewar Ministan, samun wannan ƙwarewar ya zama wajibi a wannan zamani da kowa da kowa – wato daga masana hulɗa da jama’a zuwa shugabannin kamfanoni – yake taka rawa a matsayin mai magana da yawun wani.
Idris ya ce: “Yau a wannan zamani da kowa ke zama mai magana da yawu – ko ɗan hulɗa da jama’a ne ko shugaban kamfani a ɓangaren gwamnati da masu zaman kan su – wajabcin samun ilimi kan kafofin watsa labarai ya zama abu mai matuƙar muhimmanci, domin yana ba da damar fahimta, nazari da tantance sahihancin saƙonnin da ke yawo a kafafen watsa labarai, wanda hakan zai ba da damar yanke sahihin hukunci da mu’amala da labarai yadda ya kamata.
“A ‘yan kwanakin nan, saboda rashin wannan ilimi – wato rashin iya nazarin abin da ke cikin kafafen labarai da tantance sahihancin sa – jami’an gwamnati da ma al’umma gaba ɗaya sun fara faɗawa tarkon labaran ƙarya da yaɗa bayanan da ba su da tushe.”
Ya ce samun wannan ilimi zai ba da dama ga masu magana da yawun hukumomi su inganta dabarun su wajen tantance sahihancin labarai, gano son zuciya ko ɓangaranci a cikin su, da kuma amfani da hanyoyin bincike da tantance gaskiya.
Domin cimma wannan buri, Ministan ya bayyana cewa ma’aikatar sa ta kusa kammala shiri domin buɗe Cibiyar Ilimin Kafofin Watsa Labarai ta UNESCO – wacce za ta kasance ta farko a duniya – a Buɗaɗɗiyar Jami’ar Ƙasa ta Nijeriya (NOUN) da ke Abuja.
Ya ce: “Na dawo daga Paris, a ƙasar Faransa, kwanan nan inda na gana da manyan jami’an UNESCO, kuma buɗe wannan cibiyar ya kasance babban maudu’i a tattaunawar.”
Ministan ya kuma bayyana cewa ma’aikatar sa ta samu gagarumar nasara a bara, inda aka samar da sabon matsayi na “public relations” a cikin tsarin aikin Gwamnatin Tarayya.
“Abin da wannan ke nufi shi ne, ‘Public Relations’ yanzu yana da nasa hanyar aikin kai-tsaye a cikin aikin gwamnati tun daga watan Disamba 2023.
“Haka nan, tsohuwar muƙamin ‘Information Officer’ yanzu an sake masa suna zuwa ‘Information and Public Relations Officer’, da kuma ‘Executive Officer (Information and Public Relations)’.
“Ina kuma so in ƙara da cewa NIPR ce ta taka rawar gani wajen ganin wannan cigaba ya samu.”
Idris ya kuma jaddada cewa gwamnatin Tinubu za ta ci gaba da goyon bayan ‘yancin faɗar albarkacin baki da kuma ƙarfafa kafafen watsa labarai masu zaman kansu.
Ya ce: “A ɓangaren mu, za mu ci gaba da faɗaɗa hanyoyin sadarwa a ƙasar nan da kuma bunƙasa damar zuba jari da tattalin arziki da ke cikin ta.”
Har ila yau, Ministan ya yaba wa shugaban NIPR, Dakta Ike Neliaku, saboda ƙara sabon ɓangare mai muhimmanci a wannan taro, wato ‘Information Ministerial Clinic’, inda tsofaffin ministocin yaɗa labarai suka raba gogewar da suka samu da abubuwan da suka fuskanta yayin gudanar da aikin su.
Tsofaffin ministocin da suka halarci buɗaɗɗen taron sun haɗa da Farfesa Jerry Gana, Cif John Nwodo, Mista Frank Nweke (Jnr), Mista Labaran Maku, da Alhaji Lai Mohammed.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Wacce Kasa Ce Za Ta Lashe Gasar Kofin Afirka
A gaban al’ummar kasarta, tawagar Morocco na da burin samun makoma irin ta Ibory Coast, wato nasara a gida amma ba tare da fargabar da ta fuskanta a zagayen farko ba.
Amma karbar bakuncin gasar ba lallai ba ne ya zame riba ba. A cikin karo 34 da aka gudanar da gasar tun daga shekarar 1957 (ciki har da gasar farko), sau 12 ne kacal kasar da ta karbi bakuncin gasar ta yi nasara, wato kusan kashi 35% cikin dari. Tun daga 2000, Tunisia (2004), da Masar (2006) da Ibory Coast (2024) ne kawai suka yi nasara a gida.
Kasar da ta fi fice a Afirka na da burin lashe kambu na takwas don kawar da bakin cikin kashin da ta sha a hannun Senegal a wasan karshen gasar 2022. ‘Yan wasan tawagar Masar na da ta hadin matasa da kuma gogaggu. Wannan garwayen ‘yan wasan na ba ta damar taka muhimmiyar rawa a wasannin nahiyoyi a kusan kodayaushe. Karkashin jagorancin Hossam Hassan, Masar tana wasa da sauri, yayin da ta ci gaba da amfani da dabarun wasa da aka san ta da su.
Omar Marmoush da Mostafa Mohamed su ne misalan ‘sabbin jini’ a tawagar, yayin da suke daukar darasi daga tauraron tawagar Mohamed Salah wanda ake hasashen zai taka muhimmiyar rawa a gasar bana a Morocco.
Bayan da ta lashe gasar cin kofin nahiyar Afirka a gida a shekarar 2024, tawagar Elepahants ta shiga gasar bana a matsayin mai rike da kambun gasar. Nan da nan wannan ya sanya ta zama cikin jerin wadanda ake kyautatawa zaton lashe gasar, wadda ta taba lashewa sau uku, ciki har da sau biyu a gasanni biyar na baya bayan nan.
A karkashin jagorancin Emerse Faé, tawagar Elephants ta isa Morocco da burin ci gaba da rike kambunta. Amma akwai alamun za ta fuskanci kalubale da dama daga wasu kasashen.
Tun lokacin da aka fara gasar cin kofin nahiyar Afirka (AFCON) a shekarar 1957, kasashe uku ne kawai suka iya kare kambunsu. Masar ta yi haka a shekarar 1957 da 1959, sannan kuma ta sake yi a 2006, 2008, da 2010. Ghana ta yi nasara a 1963 da 1965, Kamaru a 2000 da 2002.
Senegal, wadda ta lashe kambunta na farko shekara hudu da suka gabata bayan dogon jira da kuma rashin nasara biyu a matakin wasan karshe (2002 da 2019), ta kasance ‘yar takarar da za ta taka muhimmiyar rawa a gasar.
Bayan lashe gasar AFCON 2021, amma an fidda ta da wuri shekara biyu bayan haka, da alama ta fara samun daidaito a karkashin jagorancin Pape Thiaw, wanda ya gaji Aliou Cissé.
Yayin da tawagar ke dauke gogaggun ‘yan wasa kamar Sadio Mane da Kalidou Koulibaly da Idrissa Gueye, Lions na Teranga za su iya yin la’akari da cewa ta na da matasan ‘yan wasa masu hazaka da ke da gogewar yin nisa na gasar nahiyar.
Tawagar Senegal, da ta Morocco, su ne manyan tawagogin Afirka biyu a saman jadawalin FIFA, a matsayi na 18 da 12 bi da bi. Senegal, wadda ta mamaye rukuninta na neman tikitin shiga gasar cin kofin duniya ta 2026, za ta dogara kan ci gaban da ta ke samu ta fannin ‘yan wasa da don maimaita nasarar da ta samu a 2022.
Bayan rashin nasara sau biyu a gasar AFCON na 2021 da 2023 inda aka fitar da ita a matakin rukuni, tawagar Fennecs na son bude wani sabon babi a tarihinta na gasar. Bayan zamanin Belmadi, inda ta yi farin cikin nasara a 2019 sannan kuma ta yi rashin nasara biyu (CAN 2021 da Gasar Cin Kofin Duniya 2022), Algeria ta tunkari CAN 2025 da babban burin: sake kasancewa tawagar kwallon kafa da ke kololuwar wasa a nahiyar.
Domin cimma wannan burin, hukumar kwallon kafar kasar ta dogara ga koci Bladimir Petkobić, da kasar Serbia wanda ya yi suna bayan da ya horas da tawagar Switzerland da ta yi gogayya da manyan kasashen Turai. ‘Yan wasan da suka lashe gasar cin kofin Afrika a 2019 sannu a hankali sun dusashwewa, suna ba da dama ga sabbin matasan ‘yan wasa da suka hada da Fares Chaïbi da Houssem Aouar da Rayan Aït Nouri, da Badredine Bouanani.
Aljeriya ta kasance babbar abokiyar hamayya ga tawagogin ‘yan wasan nahiyar da dama, wadda za ta iya tabuka abin kirki a kowace gasa. Idan Petkobic ya sami nasarar daidaita tawagarsa, Fennecs na iya sake zama kamar tawagar da ta mamaye fagen wasan kwallon kafan Afirka a 2019.
Ko Nijeriya Za Ta Iya Taka Rawar Gani?
Tawagar Super Eagles ta Nijeriya ta tsinci kanta a rukunnin C a gasar bana inda za ta fafata da Tunisia da Uganda da kuma Tanzania. Super Eagles dai za ta nemi kawar da bakin cikin da ta fuskanta a wasan karshen gasar da ta gabata inda ta yi rashin nasara a hannun Ibory Coast a wasan karshe duk da cewa ita ta fara jefa kwallo a raga a wasan.
Nijeriya wadda ta ke da kambun AFCON guda uku, a shekarun 1980, 1994, da 2013, wanda hakan ya sanya ta zama daya daga cikin kasashen da suka fi samun nasara a gasar ta Afirka.
Kasancewa tana da manyan ‘yan wasa kamar su Bictor Osimhen da Ademola Lookman da ke buga wasa a manyan kungiyoyin kasashen Turai ana ganin cewa kasar za ta iya tabuka abin a zo a gani a gasar bana, duk da cewa dai rashin nasarar da ta yi a yunkurinta na samun gurbi a gasar cin kofin duniya na 2026 na sanya alamar tambaya kan rawar da za ta iya takawa.
Kociyan tawagar ta Nijeriya, Eric Chelle, na shirin kara inganta tawagar tasa da wasu sabbin ‘yan wasa guda hudu ko biyar domin tabbatar da cewa Super Eagles din ta kai bantanta a Moroko.
Wasu daga cikin sababbin ‘yan wasan da za a iya kira shi ne dan wasan baya na Blackburn Robers Ryan Alebiosu, wanda tsohon dan wasan bangaren matasa na Arsenal ne kuma a halin yanzu yana taka rawar gani a gasar Championship ta Ingila. Wani sabon dan wasan da aka sanya wa ido shi ne dan wasan tsakiya Ebenezer Akinsanmiro da ke zaman aro a kungiyar Pisa daga Inter a gasar Serie A ta Italiya.
Rauni zai hana dan wasan Nottingham Forest Ola Aina buga gasar, yayin da Bright Osayi-Samuel ke fama da rashin tagomashi a kungiyarsa ta Birmingham City ta Ingila.
Amma duk da haka ba za a iya cire rai cewa Super Eagles za ta taka rawar gani a gasar ba, saboda dimbin tarihin da ta ke da ita a gasar, kuma ana ganin ‘yan wasan za su zo da niyyar huce fushin rashin samun gurbi a gasar cin kofin duniya ta 2026.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA