Zulum Ya Gana Da Yaron Da Aka Ci Zarafi, Ya Ba Shi Gida, Tallafin Karatu
Published: 13th, April 2025 GMT
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp.কীওয়ার্ড: Boko Haram
এছাড়াও পড়ুন:
An ba da tallafin N2m ga iyalan jami’in NSCDC da aka kashe a Jigawa
Gwamnatin Jihar Jigawa ta bayar da tallafin Naira miliyan biyu ga iyalan SC Bashir Adamu Jibrin, jami’in hukumar sibil difens (NSCDC) da ya rasu a bakin aiki a kasuwar Shuwarin da ke ƙaramar hukumar Kiyawa.
Sakataren Gwamnatin Jihar, Malam Bala Ibrahim, ne ya miƙa tallafin ga matar marigayin a ofishinsa, inda ya ce wannan taimako na nufin tallafa wa iyalan marigayin tare da taimaka musu wajen kula da tarbiyyar ’ya’yansu.
Boko Haram na amfani da jirage marasa matuƙa wajen kai hare-hare — Zulum ABU ta musanta zargin ƙera makamin nukiliya a ɓoyeYa shawarci matar marigayin da ta yi amfani da kuɗaɗen wajen kula da ilimi da walwalar ’ya’yanta, tare da jaddada cewa gwamnatin Jigawa za ta ci gaba da girmama sadaukarwar jami’an tsaro da ke bayar da rayukansu don kare al’umma.
Da yake martani, Kwamandan NSCDC na Jihar Jigawa, Muhammad Kabir Ingawa, ya gode wa gwamnatin jihar bisa wannan alheri, yana mai roƙon Allah ya jiƙan marigayin.
Ita ma a nata ɓangaren, matar marigayin, Zainab Muhammad Ahmed, ta bayyana godiyarta ga gwamnatin jihar bisa wannan taimako, tare da tabbatar da cewa za ta yi amfani da kuɗaɗen yadda ya dace.