Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya umarci daukacin masarautun Jihar hudu da su fara shirye-shiryen Bikin Sallah Daba domin ganin jama’a da maziyarta sun ji dadin bukukuwan Sallah.

 

Wannan umarni na kunshe ne a cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sanusi Bature Dawakin Tofa ya fitar, bayan wani taron buda baki da suka yi da sarakunan gargajiya a dakin taro dake gidan gwamnatin Kano.

 

A cewar sanarwar, gwamna Yusuf ya jaddada cewa al’ummar jihar na zurfafa kallon al’adar sanya sabbin tufafi a ranar Sallah, tare da yin jerin gwano don shaida wa sarakunan su a kan doki, da kuma yin musabaha.

 

Don haka, Gwamna Yusuf ya bayyana cewa gwamnatinsa ba za ta yi kasa a gwiwa ba, kuma ba za ta bari wani makiya su tauye wa ‘yan kasa wannan hakki da suke da shi ba.

 

Ya kuma tabbatar wa da jama’a cewa dukkanin hukumomin tsaro a jihar za su ba da himma wajen samar da kariya ga jama’a a yayin bikin.

 

Gwamna Yusuf ya kuma bayyana cewa za a kaddamar da Majalisar Masarautar Jihar Kano a watan Afrilun bana domin samun damar gudanar da ayyukanta yadda ya kamata.

 

Gwamnan ya ci gaba da bayyana cewa za a sanar da ka’idojin majalisar,  da sauran muhimman abubuwan da suka shafi majalisar a ranar kaddamarwar.

 

Ya yabawa sarakunan bisa irin balaga da kyakkyawar alaka da suka nuna tun bayan nada su, inda ya ce wannan shi ne karo na farko a tarihin jihar da ake samun kwakkwarar alaka tsakanin sarakunan musamman ta fuskar matsayi.

 

Da yake mayar da jawabi, Shugaban Majalisar Masarautar Kano, Malam Muhammadu Sanusi II, ya tabbatar da cewa alakar da ke tsakaninsa da sarakunan masu daraja ta biyu abu ne na musamman.

 

Ya yi kira ga Gwamna Yusuf da ya yi amfani da cibiyoyin gargajiya don yada manufofi da tsare-tsare yadda ya kamata ga al’umma, tare da tabbatar da aiwatar da su cikin inganci.

 

A nasu bangaren, Sarkin Karaye, Muhammad Muhammad Maharaz; Sarkin Rano, Amb. Muhammad Isa Umaru; da mai martaba Sarkin Gaya Dr. Aliyu Ibrahim Abdulkadir a madadin jama’arsu, sun nuna jin dadinsu ga Gwamna Yusuf bisa samar da takin zamani da samar da ababen more rayuwa a fannonin ilimi, lafiya da hanyoyin sadarwa a yankunansu.

 

 

ABDULLAHI JALALUDDEEN KANO

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Sarakuna Gwamna Yusuf

এছাড়াও পড়ুন:

Masu ƙwacen waya sun kashe ma’aikacin Jami’ar Northwest a Kano

Rahotanni sun bayyana cewa wasu masu ƙwacen waya sun kashe wani ma’aikacin Jami’ar Northwest da ke Kano, Buhari Imam, ta hanyar daba masa wuta.

Bayanai sun nuna cewa barayin sun ritsa shi ne a yankin unguwar Sheka da ke karamar hukumar Kumbotso, inda suka sossoke shi da wuka a ciki kuma suka kwace wayarsa, a ranar Laraba.

BBC ya ruwaito mutumin ya rasu bayan da aka garzaya da shi Asibitin Koyarwa na Malam Aminu Kano, a ranar Juma’a.

Shugaban ƙungiyar ma’aikatan jami’ar (NASU), Kwamared Bashir Muhammad, wanda ya tabbatar da aukuwar lamarin ya yi kira ga gwamnatin Jihar Kano da sauran hukumomi da su ɗauki tsattsauran mataki a kan kisan.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sojojin Kasar Iran Sun Ce Bazasu Dakatar Da Yaki ba Har Zuwa Samun Nasara A kan HKI
  • Masu ƙwacen waya sun kashe ma’aikacin Jami’ar Northwest a Kano
  • Oman ta tabbatar da soke tattaunawar Iran da Amurka zagaye na shida
  • Miliyoyin Mutane Sun Gudanar  Da Bukukuwan “Idin Gadir” A Tehran Da Sauran Garuruwan Iran
  • Gwamnan Kaduna ya bai wa sabon Sarkin Moro’a sandar mulki
  • DA ƊUMI-ƊUMI: Gwamnati Ta Janye Taron Addu’ar Neman Wadatar Abinci
  • Jagora: Sojojin Iran ba zasu sararawa Isra’ila ba
  • Gwamnatin Kano Ta Ƙaryata Karɓo Bashin Dala Miliyan 6.6
  • Gwamnan Gombe Ya Yi Allah Wadai Da Kisan Da ‘Yan Daba Suka Yi Wa Amadi Kasiran
  • Yadda mota ta kashe mutum 8 ’yan gida daya bayan dawowa daga yawon Sallah a Kaduna