HausaTv:
2025-11-03@23:20:14 GMT

Euro-Med : Laifukan da Isra’ila ta aikata a Gaza sun zarce na Daesh

Published: 5th, April 2025 GMT

Kungiyar kare hakkin bil’adama ta kasa da kasa Euro-Med ta ce Laifukan da Isra’ila ta aikata a Gaza sun zarce na kungiyar Daesh.

A rahoton data fitar Euro-Med ta ce, tawagoginta sun tattara dubban laifukan da sojojin Isra’ila suka aikata, wadanda suka zama shaidu masu yawa na cin zarafi.

“Wadannan laifuffukan suna wakiltar yanayin tashin hankalin da ba a taba gani ba a baya baya nan, saboda laifuka ne da akayi da gangan, da kuma manufar kisan kiyashi.

” Dole ne a yi tir da yanayin laifukan da Isra’ila ta aikata a cikin yankunan Falasdinawa, saboda girman wadannan laifuffukan, wanda ya zarce na kungiyar Daesh.

Har ila yau Euro-Med ta jaddada bukatar gaggawar daukar matakin da ya dace na kasa da kasa, da kawo karshen rashin hukunta Isra’ila da kuma matakin da ya dace na hana ci gaba da aikata ta’asar.

“An aikata wadannan laifuffukan ne tare da bayyanannun niyyar kawar da al’ummar Falasdinu, da murkushe wadanda suka saura a kasarsu, da shafe su, da kawo karshen wanzuwarsu baki daya.” Inji rahoton na Euro-med.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

A Kan Wa Trump Ke Son Kaddamar Da Hari a Najeriya?

 

Duk da cewa suna da karfi a fannin aikin soja, amma harinsu zai zama tamkar amfani da igwa ne wajen kashe sauro. Duk wani fifikon da suke da shi ba zai dore ba. Saboda haka, a zahiri wannan tambayar da wani mai amfani da yanar gizo ya yi, ta nuna rashin hankali cikin kalaman shugaban Amurka.

 

Sai dai kalaman sun dace da halayya, da salon musamman na shugaba Donald Trump. Wani lokaci, da gangan ya kan yi amfani da kalmomi, da aikace-aikace marasa ma’ana wajen samar da yanayi na rashin tabbas, ta yadda zai samu damar matsawa wani lamba, don tilasta masa ya yi wani aiki. Wannan dabara ce da wasu masanan kasar Amurka ke kira da “ka’idar mahaukaci”, watakila ta dace da halayyar shugaba Trump, abun da ya sa yake ta amfani da ita wajen kula da harkokin waje.

 

Kana wannan batu na yin barazanar kai hari ya dace da halayyar kasar Amurka. Kasa ce wadda ba ta mai da hankali a kan neman gano gaskiya ba, balle ma la’akari da bayanan da Nijeriya ta gabatar dangane da zargin da aka yi mata. Kai tsaye an yi fatali da ikon mulkin kai na Najeriya, da dokokin kasa da kasa, da ra’ayoyin kasashen yankin da ake ciki. A ganin kasar Amurka, tana iya tsoma baki a duk wani aiki, da aikata yadda ta ga dama, kuma idan za ta iya yin amfani da karfin tuwo wajen tilasta wani, to ba za ta taba tattaunawa da shi ba. Kawai kasar tana kokarin aiwatar da mulkin danniya ne a duniya.

 

Amma, a cewar wasu masana, “ka’idar mahaukaci” ba ko yaushe take yin tasiri ba. Saboda idan wani ya dade yana kwaikwayon mahaukaci, to, ba za a ci gaba da tsoronsa ba. Kana mulkin danniya na kasar Amurka shi ma ba zai dore ba, idan aka yi la’akari da yadda kasashe masu tasowa ke tasowa cikin sauri a zamanin da muke ciki.

 

Ko ta yaya ya kamata Amurka ta daidaita kalamanta da ayyukanta? Kuma ta wace hanya ya kamata kasashe daban daban su yi mu’ammala da juna?

 

Na farko, ya kamata mu tabbatar da daidaito tsakanin mabambanta kasashe, da kuma bin dokokin kasa da kasa. Na biyu, ya kamata mu daukaka ra’ayin kasancewar bangarori masu fada-a-ji da yawa a duniya, da neman daidaita harkoki ta hanyar yin shawarwari, maimakon tayar da rikici. Na uku, ya kamata mu dora muhimmanci kan jin dadin jama’a, ta yadda ba za a tsaya ga kula da mutanen gida kadai ba, wato a hada da al’ummun sauran kasashe. Ya kamata a lura da hakkinsu da bukatunsu. Wadannan abubuwa suna cikin shawarar da kasar Sin ta gabatar, dangane da inganta jagorancin duniya.

 

Watakila kasar Amurka ba ta yarda da wadannan ka’idoji ba tukuna, amma tabbas wata rana za ta amince da su. (Bello Wang)

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Ra'ayi Riga Duk Da Barazanar Tattalin Arzikin Duniya, Kasar Sin Ta Sanya Tabbaci Da Kwanciyar Hankali A Duniyarmu Mai Cike Da Ruɗani October 28, 2025 Ra'ayi Riga Me Ya Sa Kasar Sin Ke Son Ganin Ci Gaban Kasashen Afirka? October 27, 2025 Ra'ayi Riga Harkokin Ciniki Da Zuba Jari Tsakanin Sin Da Afirka Sun Samu Ci Gaba Mafi Girma a Shekaru 5 Da Suka Gabata October 23, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Sami Tsaikon Sauka Da Tashin Jiragen Sama A Tanzania Saboda Rikicin Zabe
  • Isra’ila ta aikata laifuka 194 tun bayan tsagaita wuta a Gaza
  • Ƙasashen Da Ba Su Yanke Hukuncin Kisa A Duniya Ba
  • Araqchi: Da Hadin Bakin Amurka, Gwamnatin Isra’ila ta kaddamar Da Hari Kan Kasar Iran
  • Gwamnatin Isra’ila Tana Ci Gaba Da Hana Masu Jinya Zuwa Kasashen Waje Neman Magani Daga Gaza
  • A Kan Wa Trump Ke Son Kaddamar Da Hari a Najeriya?
  • Tsokaci Dangane Da Juyin Mulki A Nahiyar Afirka
  • An Kashe Mutum 3 Yayin Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Hari Kan Iyakokin Kano
  • Isra’ila Ta Kashe Mutane 4 Tare Da Jikkata Wasu Guda 3 A Kudancin Labanon
  • Iran Ta Gargadi Isra’ila Kuma Tasha Alwashin Kare Shirinta Na Nukiliya