HausaTv:
2025-07-31@14:35:14 GMT

Euro-Med : Laifukan da Isra’ila ta aikata a Gaza sun zarce na Daesh

Published: 5th, April 2025 GMT

Kungiyar kare hakkin bil’adama ta kasa da kasa Euro-Med ta ce Laifukan da Isra’ila ta aikata a Gaza sun zarce na kungiyar Daesh.

A rahoton data fitar Euro-Med ta ce, tawagoginta sun tattara dubban laifukan da sojojin Isra’ila suka aikata, wadanda suka zama shaidu masu yawa na cin zarafi.

“Wadannan laifuffukan suna wakiltar yanayin tashin hankalin da ba a taba gani ba a baya baya nan, saboda laifuka ne da akayi da gangan, da kuma manufar kisan kiyashi.

” Dole ne a yi tir da yanayin laifukan da Isra’ila ta aikata a cikin yankunan Falasdinawa, saboda girman wadannan laifuffukan, wanda ya zarce na kungiyar Daesh.

Har ila yau Euro-Med ta jaddada bukatar gaggawar daukar matakin da ya dace na kasa da kasa, da kawo karshen rashin hukunta Isra’ila da kuma matakin da ya dace na hana ci gaba da aikata ta’asar.

“An aikata wadannan laifuffukan ne tare da bayyanannun niyyar kawar da al’ummar Falasdinu, da murkushe wadanda suka saura a kasarsu, da shafe su, da kawo karshen wanzuwarsu baki daya.” Inji rahoton na Euro-med.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Sojojin HKI Sun Ci Gaba Da Kashe Kawunansu

A cikin kwanakin bayan nan ana samun karuwar sojojin HKI da suke kashe kawunansu saboda tabuwar kwakwalensu sanadiyyar yakin Gaza.

Kafafen watsa labarun HKI sun kunshi rahotanni da suke bayani akan yadda sojojin mamayar da su ka yi yaki a Gaza, suke samun tabuwar hankali, da hakan yake sa su kashe kawukansu bayan sun baro Gaza.

Wasu rahotannin sun ambaci cewa, sojojin na HKI suna rayuwa ne a cikin tsaro da ranaza saboda munanan ayyukan da su ka aikata marasa kyau.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Faransa Za Ta Fara Jefa Kayan Agaji Ta Sama A Gaza
  • Adadin Falasdinawan da Isra’ila take kashewa a Gaza yanzu ya haura 60,000
  • Amincewa Da Kasar Falasɗinu: Birtaniya Ta Gindaya Wa Isra’ila Sharuɗɗa
  • MDD Zata Aiwatar Da Hanyar Warware Rikicin Falasdinawa Da Yahudawan Sahayoniyya
  • Za mu halasta kafa ƙasar Falasɗinu muddin Isra’ila ba ta cika wasu sharuɗa ba — Birtaniya
  • Muddin Isra’ila ba ta cika wasu sharuɗa ba za mu amince da kafa ƙasar Falasɗinu — Birtaniya
  • EU Tace Zata Dakatar Da HKI Daga Cibiyar Bincikenta Saboda Gaza
  • Sojojin HKI Sun Ci Gaba Da Kashe Kawunansu
  • An fara shigar da kayan agaji a Gaza
  • Gwamna Namadi Ya Biya Sama Da Naira Biliyan Daya Ga Tsofaffin Ma’aikata