Sabon harajin Trump zai jefa tattalin arziƙin duniya cikin matsala — WTO
Published: 5th, April 2025 GMT
Shugabar Hukumar Cinikayya ta Duniya (WTO), Ngozi Okonjo-Iweala, ta bayyana damuwa kan sabon harajin da Shugaban Amurka, Donald Trump, ya saka kan kayayyakin da ke shiga da su ƙasar daga ƙasashen duniya.
Wannan haraji ya haɗa har da kashi 14 cikin 100 na kayayyakin da ake shiga da su ƙasar daga Najeriya.
A cewar sanarwar da WTO ta fitar a ranar Alhamis, hukumar na nazari da bibiyar matakin domin fahimtar yadda zai shafi cinikayya da kuma ci gaban tattalin arziƙin duniya.
Okonjo-Iweala, ta ce wasu ƙasashe mambobin WTO sun nuna damuwa kan wannan lamari, inda suka buƙaci ɗaukar matakan rage illar hakan.
Harajin da Trump ya sanar ranar 2 ga watan Afrilu ya zo ne daidai lokacin da ƙasashe da dama ke ƙoƙarin farfaɗo da tattalin arziƙinsu daga tasirin rikicin Rasha da Ukraine, da kuma tasirin hauhawar farashi da ake fama da shi a duniya.
Me ƙasashe ke cewa kan sabon harajin?Ƙasashe irin su China da Turai sun nuna rashin jin daɗinsu kan harajin Trump, inda China ta mayar da martani da nata sabon harajin.
A Najeriya kuwa, masana tattalin arziƙi sun fara fargabar cewa ƙarin harajin zai ƙara tsadar kayayyaki da kuma rage damar fitar da kaya zuwa ƙasashen waje.
Ƙungiyoyin cinikayya sun fara kira ga Amurka da ta janye harajin, domin gudun jefa ƙasashe masu tasowa cikin mawuyacin hali.
Wannan lamari na faruwa ne a daidai lokacin da Amurka ke cikin yanayin siyasa mai zafi, tun bayan da Trump ya sake ɗarewa karagar mulki a karo na biyu.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnan Kaduna ya bai wa sabon Sarkin Moro’a sandar mulki
Gwamnan Jihar Kaduna, Uba Sani, ya bai wa sabon Sarkin Moro’a, Mai Martaba Isiaku Tagwai Sambo sandar mulki, a wani biki da aka gudanar a garin Manchok da ke Ƙaramar Hukumar Kaura.
Gwamna Sani, ya bayyana cewa sarakunan gargajiya na taka muhimmiyar rawa wajen zaman lafiya, haɗin kai da kuma ci gaban al’umma.
Ya kamata Isra’ila da Iran su kawo ƙarshen rikicin da ke tsakaninsu — Gwamnatin Tarayya Mahara sun kashe mutum 26 a sabon hari a BinuwaiYa ce gwamnatinsa na bai wa sarakunan gargajiya cikakken goyon baya saboda irin rawar da suke takawa a harkar mulki da ci gaban jama’a.
“Mun jajirce wajen haɗa kan al’umma a faɗin Jihar Kaduna, ba tare da nuna bambanci ba.
“Yanzu Jihar Kaduna ta fi samun tsaro da kwanciyar hankali fiye da da. Wannan nasara ta samuwa ne sakamakon gudunmawar sarakunan gargajiya,” in ji Gwamnan.
Ya kuma buƙaci al’ummar jihar da su zauna lafiya da juna tare da yin aiki tare domin ciyar da jihar gaba.
Haka kuma, ya roƙi sarakunan da su ci gaba da jagorantar al’ummominsu cikin adalci da riƙon amana.
Bikin naɗin sarautar ya samu halartar baƙi daga sassa daban-daban, bayan rasuwar tsohon Sarkin Moro’a, Malam Tagwai Sambo, wanda ya rasu ranar 14 ga watan Yuni 2024.
Tsohon Sarkin ya rasu yana da shekaru 88, bayan mulkin shekaru 58.
Sabon Sarkin, Mai Martaba Isiaku Tagwai Sambo, ya gode wa gwamnati da al’ummar Moro’a bisa amincewar da suka yi masa.
Ya yi alƙawarin mulki cikin gaskiya da riƙon amana tare da bin doka da oda.
“Zamu haɗa kai da majalisar masarauta da kuma ɗaukacin al’umma domin tafiyar da wannan mulki yadda ya kamata,” in ji shi.