Aminiya:
2025-11-03@07:12:06 GMT

Sabon harajin Trump zai jefa tattalin arziƙin duniya cikin matsala — WTO

Published: 5th, April 2025 GMT

Shugabar Hukumar Cinikayya ta Duniya (WTO), Ngozi Okonjo-Iweala, ta bayyana damuwa kan sabon harajin da Shugaban Amurka, Donald Trump, ya saka kan kayayyakin da ke shiga da su ƙasar daga ƙasashen duniya.

Wannan haraji ya haɗa har da kashi 14 cikin 100 na kayayyakin da ake shiga da su ƙasar daga Najeriya.

Ɗalibai za su koma makaranta ranar Lahadi da Litinin – Gwamnatin Kano Kakakin APC na Ogun, Tunde Oladunjoye, ya rasu

A cewar sanarwar da WTO ta fitar a ranar Alhamis, hukumar na nazari da bibiyar matakin domin fahimtar yadda zai shafi cinikayya da kuma ci gaban tattalin arziƙin duniya.

Okonjo-Iweala, ta ce wasu ƙasashe mambobin WTO sun nuna damuwa kan wannan lamari, inda suka buƙaci ɗaukar matakan rage illar hakan.

Harajin da Trump ya sanar ranar 2 ga watan Afrilu ya zo ne daidai lokacin da ƙasashe da dama ke ƙoƙarin farfaɗo da tattalin arziƙinsu daga tasirin rikicin Rasha da Ukraine, da kuma tasirin hauhawar farashi da ake fama da shi a duniya.

Me ƙasashe ke cewa kan sabon harajin?

Ƙasashe irin su China da Turai sun nuna rashin jin daɗinsu kan harajin Trump, inda China ta mayar da martani da nata sabon harajin.

A Najeriya kuwa, masana tattalin arziƙi sun fara fargabar cewa ƙarin harajin zai ƙara tsadar kayayyaki da kuma rage damar fitar da kaya zuwa ƙasashen waje.

Ƙungiyoyin cinikayya sun fara kira ga Amurka da ta janye harajin, domin gudun jefa ƙasashe masu tasowa cikin mawuyacin hali.

Wannan lamari na faruwa ne a daidai lokacin da Amurka ke cikin yanayin siyasa mai zafi, tun bayan da Trump ya sake ɗarewa karagar mulki a karo na biyu.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Haraji Kayayyaki

এছাড়াও পড়ুন:

Gumi Ya Nemi Nijeriya Ta Katse Hulɗa Da Amurka Idan Trump Bai Janye Barazanar Sa Ba

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Ƙasashen Da Ba Su Yanke Hukuncin Kisa A Duniya Ba November 2, 2025 Manyan Labarai 2027: Yadda Gwamnoni Suka Yi Fatali Da Mataimakansu Wajen Zaɓo Waɗanda Za Su Gaje Su November 2, 2025 Manyan Labarai Wadi Al-Salam: Maƙabartar Musulmai Mafi Girma A Duniya November 2, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gumi Ya Nemi Nijeriya Ta Katse Hulɗa Da Amurka Idan Trump Bai Janye Barazanar Sa Ba
  • Ziyarar Shugaba Xi A Koriya Ta Kudu Ta Bude Babin Yaukaka Hadin Gwiwar Yankin Asiya Da Fasifik
  • Taron APEC Na 2026 Da Za A Shirya A Kasar Sin Zai Bude Sabon Babin Na Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik
  • Wadi Al-Salam: Maƙabartar Musulmai Mafi Girma A Duniya
  • An Bude Sabon Babin Huldar Sin Da Koriya Ta Kudu
  • Sin: Katsalandan Cikin Harkokin Kamfani Da Netherlands Ta Yi Ya Kawo Tsaiko Ga Tsarin Masana’antu Da Samar Da Kayayyaki Na Duniya
  • An Gudanar Da Taron Tattaunawa Na Duniya Kan Kirkire-Kirkire Da Bude Kofa Da Ci Gaba Na Bai Daya A Nijeriya
  • Gwamna Uba Sani Ya Bayyana Tsare-tsaren Ci Gaban Kaduna a Taron Duniya a Dubai.
  • Amurka ta sanya Najeriya cikin ƙasashen da ake yi wa Kiristoci kisan ƙare dangi
  • Ya Kamata Sin Da Amurka Su Zama Kawayen Juna Ba Abokan Gaba Ba