Jinkirin Fansho: PTAD Ta Fadi Dalili, Ta Ce Za a Biya Kudaden Wannan Wata
Published: 5th, April 2025 GMT
Hukumar kula da shirye-shiryen fansho na wucin gadi, wato PTAD, ta nemi afuwar ’yan fansho a fadin Najeriya kan jinkirin biyan wasu daga cikin kudaden fansho da suka taru.
A wata tattaunawa ta waya da Shugaban Kungiyar Tsofaffin Ma’aikatan NIPOST na reshen Jihar Legas, Kwamared Mukaila Ogunbote, jami’an PTAD sun bayyana cewa jinkirin ya samo asali ne daga wasu matsaloli da suka shafi Babban Bankin Najeriya da kuma Ma’aikatar Kudi.
Sai dai hukumar ta tabbatar da cewa dukkan hakkokin da suka rage, ciki har da na wadanda aka sake rijista bayan tantancewar “Ina Raye”, za a biya su a cikin wannan watan.
Kwamared Ogunbote ya ce an tattauna batutuwa da dama da suka shafi walwalar ’yan fansho, kuma ya sha alwashin ci gaba da bibiyar lamarin har sai an warware matsalolin da ke tattare da shi.
Ya kuma roki hadin kai, fahimta da juriya daga tsofaffin ma’aikatan, domin a cimma mafita cikin ruwan sanyi, musamman ganin cewa Shugaba Bola Tinubu ya amince da sakin naira biliyan sittin da takwas domin biyan bashin.
Suleiman Kaura
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
এছাড়াও পড়ুন:
An kama ’yar Najeriya da laifin safarar ɗalibai 15 a Australia
Rundunar ’yan sandan ƙasar Australia ta kama wata ’yar asalin Najeriya da ke ƙasar Australia, Binta Abubakar bisa zarginta da safarar ɗalibai daga ƙasar Papua New Guinea tare da tilasta musu yin aikin da ba a biya a gonaki a faɗin jihar Ƙueensland da sunan bayar da tallafin karatu.
Binta mai shekara 56, an kama ta ne a ranar Laraba a filin jirgin saman Brisbane a lokacin da ta isa ƙasar Papua New Guinea, inda take zaune.
Ambaliyar Mokwa: An sake gano gawar mutum bayan kwanaki 8 Abin da muke da shi a Najeriya ba cikakkiyar dimokuraɗiyya ba ce — FayemiKamen nata ya biyo bayan wani bincike na tsawon shekaru biyu da ƙungiyar masu fataucin bil-Adama ta AFP ta yankin Arewa, wacce ta ƙaddamar da bincike kan ayyukanta a watan Yulin 2022 bayan samun bayanai daga ’yan sandan Ƙueensland.
A cewar AFP, “Wani gungun ‘yan asalin Papua New Guinea (PNG) da suka yi ƙaura zuwa Australia don yin karatu, an yi zargin cewa an tilasta musu yin aiki ba tare da son ransu ba a gonaki.”
An ba da rahoton cewa matar mai izinin zama ƙasashen biyu ta yaudari aƙalla ƴan ƙasar PNG 15, masu shekaru tsakanin 19 zuwa 35, zuwa Australia tsakanin Maris 2021 da Yuli 2023 ta hanyar kamfaninta, BIN Educational Serɓices and Consulting, da kuma ta hanyar ba da guraben karatu na bogi.
Rahoton ya bayyana cewa, shafin intanet na kamfaninta ya yi iƙirarin bayar da “daidaitaccen tsarin zamani don ilimi, horarwa da kuma aikin yi.”
Sai dai ’yan sandan sun ce gaskiyar lamarin ya sha bamban sosai.
Da zarar sun isa Australia, an yi zargin cewa an tilasta wa ɗaliban su sanya hannu kan jerin takaddun doka da ke tilasta su su biya kuɗin da ke da alaƙa da karatun, kuɗin jirgi, aikace-aikacen samar da biza, inshora da kuma kuɗaɗen doka.”