Leadership News Hausa:
2025-11-02@11:28:57 GMT

Wutar Lantarki: Badaƙala Da Cin Zalin ‘Yan Nijeriya

Published: 5th, April 2025 GMT

Wutar Lantarki: Badaƙala Da Cin Zalin ‘Yan Nijeriya

A Afrilun 2018, Hukumar Hadin Kan Kasa da Kasa ta Japan (JICA) ta ba da tallafin Yen na Japan biliyan 1.317 kwatankwacin Dalar Amurka miliyan 12.4 (kimanin Naira biliyna 4.5) don shigar da na’urorin wutar lantarki (power capacitors da switchgears)

TCN a watan Satumbar 2019 ta ce ta samu lamuni na Dalar Amurka biliyan 1.

661 (kimanin Naira biliyan 601.3bn) daga hukumomi biyar don saye da sanya ayyuka a karkashin shirinta na ‘Rehabilitation and Edpansion Program’ (TREP).

Bankin Duniya shi ne ya fi bayar da gudunmawar inda ya bayara da Dalar Amurka miliyan 486 don sabon aikin isar da wutar lantarki ta Nijeriya mai taken (NETAP), da kuma Dalar Amurka miliyan 27 na aikin watsawa mai taken (North Core).

Bankin Raya Afirka (AfDB) ya ba da Dalar Amurka miliyan 410 don ayyukan fadada rarraba wutar lantarki, Hukumar Raya Kasashe ta Faransa (AFD) da Tarayyar Turai (EU) sun ba da Dalar Amurka miliyan 330 don aikin wutar lantarki mai taken (Northern Corridor Transmission Project).

A halin da ake ciki Nijeriya na da GENCOs 25, amma babban layukan wutar lantarki ta Nijeriya (National Power Grid) ta durkushe sau 206 daga shekarar 2010 zuwa 2019, kamar yadda Cibiyar Bincike ta Duniya (ICIR) ta ruwaito.  Kalubale ne samun alkaluma na  shekarun 2005 zuwa 2009 da kuma daga 2020 zuwa yau.

Duk da durkushewar layukan wutar lantarkin da ke faruwa, Hukumar Kula da Wutar Lantarki ta Nijeriya (NERC), ta bayyana cewa za ta cire Naira biliyan 10.5 daga cikin ribar kudaden da aka amince kuma aka ba da izini  na shekara-shekara ga DISCOs guda 11, a matsayin wani vangare na takunkumi kan rashin bin ka’idojin lissafin kudi da za su caja  abokan cinikin su da ba su da mitoci.

Rahoton 2019 na Ofishin Kididdiga na Kasa (NBS) – Rahoton Sashen Makamashi da aka samu kuma aka tura (Energy Generated and Sent Out and Consumed and Load Allocation). Ya nuna:

Jimillar makamashin da GENCOs suka samar kuma aka aika, shi ne 33,448,633 MWh, kamar haka:

a.      GENCOs masu zaman kansu – 19,692,683 MWh. b.      Masu Samar da Wutar Lantarki (IPP) – 7,798,253 MWh. c.       Hadakar Wutar Lantarki ta Kasa (National Integrated Power Project (NIPP) – 5,957,697 MWh.

Ba ri muyi lissafi gwari-gwari: Matsakaicin Kirkirar Makamashi na Kullum =Jimlar Kirkirar Makamashi na Shekara-shekara / Yawan Kwanaki a cikin Shekara.

A.     Matsakaicin Karfafa Makamashi na Kullum = MWh 33,448,633 kwanaki 365. B.     Matsakaicin Karfafa Makamashi na Kullum = MWh /91,642.28  kowace rana.

A halin yanzu matsakaicin Rarraba Wutar Lantarki (MW) dangane da bayanan NERC kamar yadda ta sanar a shekarar 2021 ya kasance MW 4,094.09.

Tambaya a nan,

Na farko – Me ya faru da kiyasin makamashin MWh 87,000 (91,642.28 – 4,094.09) da ake samarwa a rana?

Na biyu – Me ya sa CBN da sauran cibiyoyin hada-hadar kudi za su ci gaba da fitar da biliyoyin Naira don samar da makamashin da ba ya isa wajen masu bukatarsa?

Na uku – Menene kuma ya faru da makudan kudade na kasafin kudin shekara-shekara (National Budget) da suka shiga harkar wutar lantarki ba tare da samar da ingantacciyar wutar lantarki ga jama’a ba?

 

Cin Zali da Rana Tsaka

A lokacin da aka ruguza NEPA/PHCN, akwai ma’aikata kusan 15,000 da aka sallame su, sannan aka mayar da al’amuransu zuwa kamfanin kula da al’amura, da basususka da kuma sauran ababen da suka shafi  wutar lantarki  na Nijeriya, wato (NELMCO) wanda aka kirkira domin gudanar da ayyukan da ya shafe wa’anan ababe na rusasshiyar PHCN.

To wane wainar aka toya a wannan vangaren?

A cewar Bankin Lamuni (IMF), an kiyasta cewa Nijeriya ta na yin asarar kusan Dalar Amurka biliyan 29 a kowace shekara saboda rashin samar da wutar lantarki isasshe. Bugu da kari, an ruwaito ‘yan Nijeriya na kashe kudade  Dalar Amurka biliyan 14  kowace shekara akan janareta da mai don shawo kan karancin wutar lantarki.

Ba makawa rufe Kamfanin Mitar Wutar Lantarki na Nijeriya (EMCON) da take Zariya na Jihar Kaduna tare da asarar ayyukan yi da kuma fitar da makudan kudaden waje zuwa kasashen waje don sayen mitoci savanin sanya hannun jari a cikin gida.

NELMCO ce ke da alhakin rikewa da sarrafa kaddarorin PHCN da Yarjejeniyar Sayen Wutar Lantarki, tare da ikon siyarwa, ko mu’amala da wadannan kaddarorin don biyan basussuka ko wasu batutuwa masu alaka.

An dora wa NELMCO alhakin karva da gudanar da basussukan da suka makale, kuma ita aka daurawa alhakin sauran alamura da ke da alaka da albashi ko alawus na ma’aikatan rusasshiyar Kamfanin Power Holding Company of Nigeria (PHCN). wannan ya hada da:

Rashin biyan kudin Fansho da Garatuti na vangaren  gudummawar kamfanin NEPA/PHCN saboda kashi 7.5% kawai da ma’aikatan ke bayarwa ko wane wata su ne a cikin asusunsu na PFA.

Rashin biyan albashi da alawus-alawus da fakitin sallama na yawancin tsofaffin ma’aikatan kamfanin NEPA/PHCN.

Batu mai ban haushi da ya kunshi kaso 10% na hannun jarin kafanin PHCN na ma’aikatan da aka sallama wanda har yanzu ba a basu ba.

Wani batun kuma da aka kasa warware shi, shi ne horon salama (training) na gida da na waje da kuma bita ga ma’aikatan da aka sallama, wanda ya kasance sharadi ne na sallama ko biyan  alawus a madadinsa, har yanzu ba a biya su wannan kudade ba.

Rashin biyan asalin alawus da kuma bashin da suke bi na albashin watanni 16 daga 2012. (Daga lokacin ruguza kamfanin PHCN zuwa kammala mika su ga mutanen da wai su ne ’’Core Investors’’).

Rashin biyan  kuɗin inshoran  ma’aikatan NEPA/PHCN.

Rashin biyan kudin rangwamen wutar lantarki ga ma’aikatan NEPA/PHCN da aka sallama.

Halin da aka jefa wadanda aka sallama a lokacin wasoson NEPA/PHCN ya kara wani rashin adalci ga labarin, yayin da kuma aka bar su a cikin rudani, da kuma hana su hakkokinsu na hakika. Bayan haka, wadannan sallamammun ma’aikatan an bar su cikin wani yanayi na fargaba da rashin sanin makomarsu game da makudan kudadensu da ya haura kimanin Naira bilyyan 25 ko fiye, bisa ga ikirarinsu.

Bari mu nunfasa haka kada mu samu hawan jinni domin kuwa akwai saura.

Za mu ci gaba mako mai zuwa idan Allah ya kai mu.

 

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Lantarki Dalar Amurka miliyan wutar lantarki ta Wutar Lantarki ta da Wutar Lantarki da wutar lantarki Rashin biyan

এছাড়াও পড়ুন:

Sin Da Amurka Suna Taimaka Wa Juna Da Samun Wadata Tare

A ranar 30 ga wata ne shugabannin kasashen Sin da Amurka suka gana da juna a birnin Busan na kasar Koriya ta Kudu, lamarin da ya jawo hankulan kasa da kasa, inda shugabannin 2 suka yi musayar ra’ayoyi dangane da huldar da ke tsakanin kasashen 2 da al’amuran da suka jawo hankulansu. Sun amince da inganta hadin gwiwar kasashen 2 a fannonin tattalin arziki da cinikayya da makamashi da kyautata mu’amalar al’adu.

A yayin ganawar, shugaba Xi Jinping na kasar Sin ya jaddada cewa, yana son hada kai da shugaba Donald Trump na Amurka wajen aza harsashi mai kyau na raya huldar da ke tsakanin kasashen 2, tare da samar wa juna kyakkyawan yanayin samun ci gaba. A nasa bangaren, shugaba Trump ya ce, kasar Sin, abokiyar Amurka ce mafi girma. Kasashen 2 za su hada kansu wajen samun nasarar gudanar da manyan ayyuka da dama a duniya. Nan gaba Amurka da Sin za su kara samun nasara a hadin gwiwarsu. Shugabannin 2 sun amince su rika yin mu’amala da juna. Shugaba Trump yana sa ran kai ziyara a kasar Sin a farkon shekara mai zuwa, ya kuma gayyaci shugaba Xi ya ziyarci Amurka.

Masharhanta sun yi nuni da cewa, ganawar shugabannin 2 ta sanya tagomashi kan kyautatuwar huldar da ke tsakanin Sin da Amurka, ta kuma tsara manufar raya huldar kasashen 2 a nan gaba, tare da kwantar da hankulan kasashen duniya.

Abubuwan tarihi da kuma hakikanin abubuwa sun nuna cewa, wajibi ne Sin da Amurka su zama abokan juna. A wannan muhimmin lokaci, ganawar da shugabannin kasashen 2 suka yi ta sake tsara manufar kyautata da raya huldar da ke tsakanin kasashen 2. Muddin kasashen 2 suka aiwatar da muhimman daidaito da shugabannin 2 suka cimma, da mutunta ruhin adalci, tare da martaba juna da samun moriyar juna, to, za a raya huldar da ke tsakanin kasashen 2 ba tare da wata matsala ba, da kuma kara samar da kwanciyar hankali da tabbaci a duniya. (Tasallah Yuan)

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin Xi Jinping Ya Halarci Kwarya-Kwaryan Taron Shugabannin APEC Na 32 Tare Da Gabatar Da Jawabi October 31, 2025 Daga Birnin Sin An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Kirkire-kirkire Da Bude Kofa Da Raba Damar Samun Ci Gaba A Colombo October 30, 2025 Daga Birnin Sin Sin Ta Fitar Da Jerin Sakamakon Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Tawagar Kasar Da Ta Amurka Suka Cimma  October 30, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tinubu zai gana da Trump kan zargin kisan Kiristoci a Nijeriya 
  • Kisan Kiristoci: Za mu kai hari Najeriya — Trump
  • Shugaban Kasar Najeriya Ya Mayar Da Martani Ga Takwaransa Na Amurka Akan Rikicin Addini
  • An Cafke Ma’aikatan Gidan Marayu Da Suka Sayar Da Yara 4 A Kan Naira Miliyan 3
  • Jerin Gwarazan Taurarinmu
  • Ya Kamata Sin Da Amurka Su Zama Kawayen Juna Ba Abokan Gaba Ba
  • Zaben 2027 Zai Kasance Ne Tsakanin Mulkin Tinubu Da Zabin Ƴan Nijeriya —Atiku Abubakar
  • Sin Da Amurka Suna Taimaka Wa Juna Da Samun Wadata Tare
  • Sin Ta Fitar Da Jerin Sakamakon Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Tawagar Kasar Da Ta Amurka Suka Cimma 
  • Babu wani uzuri da za a yi wa sabbin hafsoshi kan matsalar tsaron Nijeriya — Tinubu