Leadership News Hausa:
2025-12-12@10:07:32 GMT

Rashford Ya Koma Tawagar Ingila Bayan Shekara Ɗaya

Published: 14th, March 2025 GMT

Rashford Ya Koma Tawagar Ingila Bayan Shekara Ɗaya

Rashford, mai shekaru 27, ya buga wa Ingila wasanni 60 tare da cin ƙwallaye takwas.

Amma bai samu dama a hannun tsohon koci Gareth Southgate ba, inda aka cire shi daga gasar Euro 2024 da kuma Nations League ta 2024-25.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku.

Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Ɗan Wasa Rashford

এছাড়াও পড়ুন:

Farashin Kayan Abinci Na Sauka Yayin Da Bikin Kirsimeti Da Sabuwar Shekara Ke Matsowa

 

A Legas farashin shinkafa ya fadi sosai

A kasuwannin Mushin da Daleko, farashin buhun shinkafa kilo 50 da ake sayar da shi a da Naira N75,000 cikin Nuwamba, a yanzu ya dawo Naira 54,000.

 

Jihar Delta

A Jihar Delta, musamman a Asaba, farashin kayan abinci ya daidaita a manyan kasuwanni irin su Kasuwar Oko (Hausa), Midwifery Market da Ogbogonogo Market, sai dai a kasuwannin mako-mako na kauyuka.

Bincike a babban birnin jihar ya nuna cewa farashin muhimman kayan abinci ya dan daidaita, amma ‘yan kasuwa da masu sayayya sun nuna damuwa kan karancin kudin da ake da shi don sayayya.

Kwandon tumatir da ake sayarwa Naira 5,000 a wasu watanni da suka gabata, yanzu ya sakko Naira 4,000. Farashin doya ya tsaya a tsakanin Naira 1,800 zuwa Naira 2,000 kowace guda, yayin da garri yake kan Naira 3,000 gwangwani, ba tare da sauyi ba duk da lokacin girbi.

A Kasuwar Ogbogonogo, wata mai girki, Mrs Beatrice Nnamdi, ta ce wasu kayan abinci har yanzu suna da tsada duk da zuwan sabbin kayan abinci.

“Talon shinkafa yanzu yana tsakanin Naira 60,000 zuwa Naira 65,000. A da yana tsakanin Naira 90,000 zuwa Naira120,000. Buhun wake yanzu Naira 50,000. Mun taba sayarwa a nan tsakanin Naira70,000 zuwa Naira 90,000,” in ji ta.

“A lokacin girbi, idan doya, masara da dankali suka fara fitowa, ya kamata garri ya yi sauki. Tumatir yanzu yana tsakanin Naira 7,500 zuwa Naira 8,000, gwangwani Wake da shinkafa sun sauka kadan daga Naira 6,000 zuwa Naira 5,500 gwangwani,” a cewarta.

 

Jihar Yobe

Manoma a wasu sassan Jihar Yobe, musamman a cikin da kewaye da Damaturu, babban birnin jihar, na fama da mummunan tasirin fari wanda ya busar da amfanin gona saboda karancin ruwan sama.

Da dama daga cikin manoma da mazauna yankunan da abin ya shafa sun bayyana fargaba matuka game da karancin ruwan sama a bana, wanda suka ce ya rage girbinsu kuma ya kara tsananta yanayin rayuwarsu.

Wasu daga cikin manoman sun shaida wa LEADERSHIP Weekend cewa karancin ruwan sama a wannan yanki, idan aka kwatanta da wasu sassan jihar da suka samu isasshen ruwan sama, ya sa amfanin gona irin su masara, gero da shinkafa suka bushe, kuma hakan na iya jawo karancin abinci a gaba.

Daya daga cikin manoman, Mallam Bukar Abba, mazaunin Damaturu, ya ce fari da ya biyo bayan karancin ruwan sama ya bar amfanin gona suna bushewa.

Bukar ya ce ruwan sama ya tsaya da wuri, kuma lokutan da ya yi, zuba yayyafi ne kawai ba wanda zai wadatar don ciyar da amfanin gona ba.

Ya kara da cewa ruwan saman bana ya bar manoma da fargabar tsaro a fannin abinci, inda ya nuna cewa da dama daga cikin manoma sun yi asarar miliyoyin naira saboda amfanin gonar bai kai lokacin girma ba kafin ya bushe.

Wani manomin da ke kuka da halin fari, Mohammed Salisu, mazaunin Karamar Hukumar Gashua, ya ce karancin ruwan saman ya yi mummunan tasiri sosai domin ya lalata hanyar samun rayuwarsu.

 

Jihar Kaduna

A Kaduna, wani mai sayar da kayan abinci na Kasuwar Sabon Tasha, Elias Samson, ya ce farashin kayan abinci ya ci gaba da daidaituwa tun bayan da gwamnatin tarayya ta rage farashin abinci.

“Farashin abinci yana fara tashi ne a watan Disamba, kusa da Kirsimeti, amma a halin yanzu farashin yana nan yadda yake. Ka san manoma har yanzu suna girbe masara, wake, shi ya sa ake da tsoffin kayan abinci da sababbi a kasuwa yanzu. A lokacin girbi farashi ba ya tashi haka kawai,” in ji shi.

Wata mai sayen kayan abinci, Laadi Onoja, ta ce: “Farashin abinci har yanzu yana da kyau idan aka kwatanta da yadda muke saya wasu watanni da suka gabata. Lokacin cunkoso shi ne watan Disamba, kuma a wancan lokacin wasu dillalai kan kara kudi domin samun karin riba.

Na sayi mudu daya na shinkafa mai tsabta Naira 1,800 kuma wasu wurare suna sayarwa Naira 1,700 musamman a kasuwannin kauye.”

 

Jihar Kogi

An samu daidaituwar farashin kayan abinci a Lokoja, babban birnin Jihar Kogi, matuka, ban da naman Sa wanda ya rika tashi a ‘yan watannin nan.

Lokacin da LEADERSHIP Weekend ta ziyarci sabuwar kasuwa a Lokoja, ana sayar da shinkafa Naira 7,000 maimakon farashin da ya kai Naira 14,500 a da.

Wata ‘yar kasuwa mai sayar da shinkafa da wake, Hajiya Lami Sule, ta ce babu wani tashin farashi da aka samu kan kayan abinci.

Sai dai a wajen sayar da nama, lamari ya bambanta domin farashin kilo daya na nama yana kara tashi kullum.

Wani mutum mai matsakaicin shekaru, Ismail Jegede, ya ce: “Ban da farashin nama, farashin sauran kayan abinci ya yi tsaya dai-dai a kasuwannin baya guda biyar. Kilo daya na nama da muke saya tsakaninNaira 3,500 zuwa Naira 4,500 yanzu ana sayar da shi Naira 6,000.”

Shi ma wani mai sayar da nama a sabuwar kasuwar Lokoja, Mallam Danladi Abu, ya danganta tashin farashin namansa ga kudin sufuri da kuma matsalar tsaro.

“Dole mu je wurare masu nisa domin samun shanu saboda rashin tsaro. Mafi nisan wurin da muka tafi, shi ne mafi tsadar jigilar dabbar,” in ji shi.

 

Jihar Akwa Ibom

A yayin haka, farashin yawancin kayan abinci na yau da kullum, kamar garri, wake, shinkafa, albasa, barkono da sauran su, ya kasance daidai, a cewar binciken da aka gudanar a manyan kasuwanni a Uyo, da kuma Kananan Hukumomin Itu da Etinan.

Kodayake har yanzu ya yi wuri a yi hasashen abin da zai faru domin har yanzu jihar ba ta fuskanci cunkoson jama’ar bukukuwan shekara ba, farashin kayayyaki ya kasance a daidaitacce a kasuwannin Akpan Andem Market (Uyo), Itam International Market (Itu) da Okpokpo Market (Etinan).

Garri, wanda a baya ake sayar da kofi 5 zuwa 6 kan Naira 1,000 bayan shugaba Tinubu ya hau mulki, yanzu ana samun kofuna 12 zuwa 13 akan farashi guda.

Buhun shinkafa, da a baya yake tsakanin Naira 70,000 zuwa Naira 80,000, yanzu yana tsakanin Naira 38,000, Naira 47,000 zuwa Naira 60,000 gwargwadon inganci da nau’in hatsi.

Farashin wake ya sauka daga Naira 450 zuwa Naira 500 zuwa Naira 250 zuwa Naira 300.

Naman Sa kuwa ya ci gaba da kasancewa mai tsada tsakanin Naira 3,000 zuwa Naira 3,200 kowane kilo, yayin da farashin kaji ya sauka daga Naira 10,000 zuwa Naira 15,000 zuwa Naira 6,000.

Wani dillalin hatsi daga Sokoto, Adamu Isa, ya danganta saukar farashin da matakin da gwamnatin Jihar Akwa Ibom ta dauka na rusa kungiyoyin kasuwa a manyan kasuwanni.

Wani dillalin dabbobi, Abubakar Garba, ya bayyana cewa matakin Gwamnonin Nijeriya (NGF) na kawar da harajin kan tituna toll points “shima babban dalili ne da ya taimaka wajen rage farashin muhimman kayan masarufi.”

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Ƴan Bindigar Daji: Jihohin Arewa 7 Sun Kaddamar Da Rundunar Fatattakar Su December 12, 2025 Manyan Labarai Gwamnonin Arewa Sun Yi Rawar Gani A Kafa Gidauniyar Fuskantar Matsalar Tsaro December 12, 2025 Manyan Labarai Katsina Ta Amince Da Bayar Da Alawus Na Naira 30,000 Duk Wata Ga Malaman Karkara December 11, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Farashin Kayan Abinci Na Sauka Yayin Da Bikin Kirsimeti Da Sabuwar Shekara Ke Matsowa
  • Annabi SAW Ya Zarce Duk Sauran Annabawa Yawan Mu’uzijoji
  • ‘Sojojin Najeriya da na Ivory Coast 200 sun shiga domin tsaftace Jamhuriyar Benin’
  • Manchester United ta shiga zawarcin Sergio Ramos
  • Zanga-zanga ta ɓarke bayan haɗarin tirela ta kashe mutum a Yobe
  • Ma’aikatar Mata da Walwalar Jama’a ta Jihar Jigawa ta Kare Kasafin Kudinta a Gaban Majalisa
  • Borkina Faso Ta Saki Sojojin Sama Na Najeriya 11 Da ta Kama Bayan Jirginsu Yayi Saukar Gaggawa.
  • DAGA LARABA: Ko Ziyarar Tawagar Amurka Za Ta Kawo Karshen Matsalar Tsaro A Najeriya?
  • Kamfanin Mangal ya kori direba kan dauko yara 21 da aka kama a Kogi