’Yan bindiga sun sace gwarzon gasar karatun Alƙur’ani a Katsina
Published: 13th, March 2025 GMT
’Yan bindiga sun sace gwarzon gasar karatun Alƙur’ani, Abdulsalam Rabi’u Faskari, tare da mahaifinsa da ’yan uwansa a Jihar Katsina.
Lamarin ya faru ne da yammacin ranar Talata a kusa da Labin Bangori, yayin da suke dawowa Faskari bayan Abdulsalam ya samu lambar yabo wadda Gwamna Dikko Radda ya ba shi saboda nasarar da ya samu a gasar karatun Alƙur’ani ta ƙasa karo na 39 da aka gudanar a Birnin Kebbi, a Jihar Kebbi.
Wani jami’in gwamnati a Faskari, wanda ya nemi a sakaya sunansa, ya tabbatar da sace su.
“Malam Rabe da ’ya’yansa biyar, ciki har da Abdulsalam, wanda aka sace su a Bangori a kan titin Yankara. Har yanzu ba mu ji komai daga gare su ba.”
Abdulsalam, wanda ɗalibi ne a sashen likitanci na Jami’ar Ahmadu Bello (ABU), Zariya, ya samu matsayi na farko a gasar a ɓangaren maza bayan ya haddace Alƙur’ani.
Har yanzu ’yan sanda a Katsina ba su fitar da wata sanarwa kan lamarin ba.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Bindiga Gasar Karatu Gwarzo hari
এছাড়াও পড়ুন:
Jami’an tsaro sun kama masu garkuwa da mutane 7 a Gombe
Rundunar ’Yan Sandan Jihar Gombe, tare da haɗin gwiwar maharba, sun samu nasarar tarwatsa gungun masu garkuwa da mutane, tare da kama mutum bakwai da ake zargi da aikata laifuka a Jihohin Gombe, Bauchi, Yobe da Adamawa.
Rundunar ta samu nasarar ne bayan kama Abdullahi Ibrahim, mai shekaru 40 daga ƙauyen Tilde a Funakaye, a ranar 23 ga watan Nuwamba 2025.
An harbe manomi saboda rikici kan filin kiwo a Borno DSS ta kama likitan da ke duba ’yan bindiga a dazukan KwaraAn kama shi ne bayan samun bayanan sirri kan hulɗa da masu satar shanu.
Abdullahi, ya amsa cewa yana da hannu a garkuwa da mutane tare da bayyana sunayen waɗanda suke aikata laifin tare.
A cewar kakakin rundunar, DSP Buhari Abdullahi, jami’an Operation Hattara tare da maharba ne suka kai samame maɓoyarsu a ranar 28 ga watan Nuwamba 2025, inda suka kama mutum shida bayan yin artabu.
Waɗanda aka kama sun haɗa da; Usman Mohammed, Hussain Idris, Adamu Tukur, Ya’u Abdullahi, Ali Umar, Hassan Usman da Abdullahi Ibrahim.
Rundunar ta ce waɗanda ake zargin sun amsa cewa suna da hannu a garkuwa da mutane tare karɓar kuɗin fansa kusan Naira miliyan 150.
Jami’an sun shiga dajin Gadam, inda suka samu bindiga ƙirar GPMG mai jigida guda ɗaya da harsasai takwas bayan wata musayar wuta da suka yi wasu ’yan ta’adda da suka tsere.
Haka kuma an gano suna da hannu wajen garkuwa da wani mutum a ƙauyen Barderi a Akko, a ranar 15 ga watan Janairun 2025.
Sun tsare mutumin na tsawon makonni biyu kafin karɓar Naira miliyan 15 a matsayin kuɗin fansa.
DSP Buhari, ya ce ana cigaba da bincike, kuma za a gurfanar da su a kotu.
Ya roƙi jama’a da su ci gaba da bai wa rundunar sahihan bayanai domin inganta harkokin tsaro.
Rundunar ‘Yan Sandan Gombe ta ce za ta ci gaba da kare rayuka da dukiyoyin al’umma a faɗin jihar.