Aminiya:
2025-12-01@11:09:03 GMT

’Yan bindiga sun sace gwarzon gasar karatun Alƙur’ani a Katsina

Published: 13th, March 2025 GMT

’Yan bindiga sun sace gwarzon gasar karatun Alƙur’ani, Abdulsalam Rabi’u Faskari, tare da mahaifinsa da ’yan uwansa a Jihar Katsina.

Lamarin ya faru ne da yammacin ranar Talata a kusa da Labin Bangori, yayin da suke dawowa Faskari bayan Abdulsalam ya samu lambar yabo wadda Gwamna Dikko Radda ya ba shi saboda nasarar da ya samu a gasar karatun Alƙur’ani ta ƙasa karo na 39 da aka gudanar a Birnin Kebbi, a Jihar Kebbi.

NAJERIYA A YAU: Ko Sulhu Da ’Yan Ta’adda Zai Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Arewa? Hanyoyi 6 da mutum zai kare kansa daga tsananin zafi

Wani jami’in gwamnati a Faskari, wanda ya nemi a sakaya sunansa, ya tabbatar da sace su.

“Malam Rabe da ’ya’yansa biyar, ciki har da Abdulsalam, wanda aka sace su a Bangori a kan titin Yankara. Har yanzu ba mu ji komai daga gare su ba.”

Abdulsalam, wanda ɗalibi ne a sashen likitanci na Jami’ar Ahmadu Bello (ABU), Zariya, ya samu matsayi na farko a gasar a ɓangaren maza bayan ya haddace Alƙur’ani.

Har yanzu ’yan sanda a Katsina ba su fitar da wata sanarwa kan lamarin ba.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Bindiga Gasar Karatu Gwarzo hari

এছাড়াও পড়ুন:

CAF Tayi Watsi Da Alƙalan Wasan Nijeriya a Kofin Afrika Na 2025

Hukumar ƙwallon ƙafa ta Nahiyyar Afrika (CAF) ta fitar da jerin alƙalan wasa da masu kula da na’urar VAR a gasar cin kofin Nahiyyar Afrika ta 2025, amma babu ɗan Najeriya ko ɗaya.

A sanarwar da hukumar ta fitar, ta ayyana alƙalan wasa 28 da masu kula da VAR 14 daga ƙasashe daban-daban.

Ƙasar Japan ta fara sayar da injin da ke yi wa mutane wanka Hamɓararren Shugaban Guinea-Bissau ya gudu Senegal

Hukumar ta zaɓo alƙalan wasa biyu daga ƙasashen Maroko, Aljeriya, Masar, da kuma Mauritaniya.

Masana harkokin wasanni dai na ganin cewa matsalar cin hanci da rashawa ne dalilin yin shagulacin ɓangaro ga alƙalan wasan Najeriya, saboda karɓar na goro musamman a gasar Firimiya.

Kawo yanzu an shafe shekaru 19 rabon da wani alƙalin wasa daga Najeriya ya busa gasar cin kofin Nahiyyar Afrika.

Za a fara gasar daga ranar 21 ga watan Disamba 2025 zuwa 18 ga watan Janairun 2026.

Ƙasar Maroko ce za ta buɗe gasar da karɓar baƙuncin Comoros a birnin Rabat.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Nijar : zamu sayar da uranium dinmu ga wanda muka ga dama_ Janar Tiani
  • ’Yan bindiga sun sace fasto da matarsa  masu ibada a Kogi 
  • Sojoji sun ceto ’yan mata 12 da ISWAP suka sace a Borno
  • ’Yan bindiga sun sace amarya da ƙawenta 14 a Sakkwato
  • Sojoji sun ceto mutum 7 da ’yan bindiga suka sace a Kano
  • ’Yan bindiga sun kashe tsohuwa, sun sace mutum 3 a Kano
  • An Kammala Gasar ‘Rayan’ Na AI Ta Kasa Da Kasa A Nan Tehran
  • CAF ta ƙara yawan ’yan wasan ƙasashe zuwa 28 a gasar nahiyar Afrika
  • Portugal ta lashe Kofin Duniya na ’yan ƙasa da shekaru 17 a karon farko
  • CAF Tayi Watsi Da Alƙalan Wasan Nijeriya a Kofin Afrika Na 2025