Aminiya:
2025-11-22@19:13:28 GMT

’Yan bindiga sun sace gwarzon gasar karatun Alƙur’ani a Katsina

Published: 13th, March 2025 GMT

’Yan bindiga sun sace gwarzon gasar karatun Alƙur’ani, Abdulsalam Rabi’u Faskari, tare da mahaifinsa da ’yan uwansa a Jihar Katsina.

Lamarin ya faru ne da yammacin ranar Talata a kusa da Labin Bangori, yayin da suke dawowa Faskari bayan Abdulsalam ya samu lambar yabo wadda Gwamna Dikko Radda ya ba shi saboda nasarar da ya samu a gasar karatun Alƙur’ani ta ƙasa karo na 39 da aka gudanar a Birnin Kebbi, a Jihar Kebbi.

NAJERIYA A YAU: Ko Sulhu Da ’Yan Ta’adda Zai Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Arewa? Hanyoyi 6 da mutum zai kare kansa daga tsananin zafi

Wani jami’in gwamnati a Faskari, wanda ya nemi a sakaya sunansa, ya tabbatar da sace su.

“Malam Rabe da ’ya’yansa biyar, ciki har da Abdulsalam, wanda aka sace su a Bangori a kan titin Yankara. Har yanzu ba mu ji komai daga gare su ba.”

Abdulsalam, wanda ɗalibi ne a sashen likitanci na Jami’ar Ahmadu Bello (ABU), Zariya, ya samu matsayi na farko a gasar a ɓangaren maza bayan ya haddace Alƙur’ani.

Har yanzu ’yan sanda a Katsina ba su fitar da wata sanarwa kan lamarin ba.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Bindiga Gasar Karatu Gwarzo hari

এছাড়াও পড়ুন:

Ƴan Bindiga Sun Sace Dalibai Mata 25 a Jihar Kebbi 

Rundunar ‘Yan Sandan Nijeriya reshen Jihar Kebbi ta tabbatar da sace dalibai ashirin da biyar daga Makarantar Sakandare ta ’Yan Mata ta Gwamnati da ke Maga a Ƙaramar Hukumar Danko/Wasagu.

Lamarin ya faru ne a daren Litinin da misalin ƙarfe 4 na safe a lokacin da ƴan bindiga suka mamaye makarantar, inda suka kashe wani ma’aikaci ɗaya tare da jikkata wani.

A cewar wata sanarwa da Jami’in Hulɗa da Jama’a na Rundunar ‘Yan Sandan, CSP Nafi’u Abubakar Kotarkoshi ya sanya wa hannu, maharan ɗauke da makamai masu ƙarfi sun kutsa makarantar inda suka yi musayar wuta da jami’an tsaro da ke bakin aiki. Duk da ƙoƙarin jami’an, an ruwaito cewa maharan sun haye katangar makarantar suka kuma yi awon gaba da ɗaliban daga ɗakunan kwanan su.

Jami’in ya tabbatar da cewa Hassan Makuku wanda rahotanni suka ce shi ne mataimakin shugaban makarantar ya rasa ransa yayin harin, yayin da wani Ali Shehu ya samu rauni sakamakon harbinsa da bindiga a hannunsa na dama.

Bayan faruwar lamarin, sanarwar ta ce Kwamishinan ‘Yan Sanda, Bello Muhammad Sani, ya tura jami’an ‘yan sanda na musamman tare da jami’an soji da ƙungiyoyin ‘yan bijilanti zuwa yankin.

Tawagar haɗin gwiwa na ci gaba da bincike a hanyoyin da ake zargin maharan sun bi da dazuzzukan da ke kewaye domin gudanar da aikin ceto da kuma kama waɗanda suka aikata laifin.

Kwamishinan ya yi kira ga mazauna yankin da su kwantar da hankalinsu tare da kasancewa masu lura da muhallinsu, yana tabbatar musu da cewa rundunar za ta ci gaba da tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyi a fadin jihar.

Sani Haruna Dutsinma

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sace ɗalibai: An rufe makarantu a Katsina da Taraba
  • Gwamnati ta ba da umarnin rufe makarantun kwana 47 a faɗin Najeriya
  • Atiku ya nemi a ayyana dokar ta-ɓaci kan satar ɗalibai a Najeriya
  • Sojoji sun bar makarantar Maga kafin ’yan bindiga su kai hari — Gwamna Kebbi 
  • An kama Faston da ake zargi da yi wa mambobin cocinsa 3 fyade
  • ’Yan bindiga sun sace dalibai a wata makarantar Neja
  • Sace ɗalibai: Tinubu ya bai wa Ministan Tsaro umarnin tarewa a Kebbi
  • Ƴan Bindiga Sun Sace Dalibai da Malamai a Jihar Neja
  • ’Yan Bindiga Sun Nemi Miliyan 100 Kudin Fansa Kan Kowane Mutum Ɗaya da Suka Sace a Kwara
  • Ƴan Bindiga Sun Sace Dalibai Mata 25 a Jihar Kebbi