Aminiya:
2025-12-11@02:10:15 GMT

’Yan bindiga sun sace gwarzon gasar karatun Alƙur’ani a Katsina

Published: 13th, March 2025 GMT

’Yan bindiga sun sace gwarzon gasar karatun Alƙur’ani, Abdulsalam Rabi’u Faskari, tare da mahaifinsa da ’yan uwansa a Jihar Katsina.

Lamarin ya faru ne da yammacin ranar Talata a kusa da Labin Bangori, yayin da suke dawowa Faskari bayan Abdulsalam ya samu lambar yabo wadda Gwamna Dikko Radda ya ba shi saboda nasarar da ya samu a gasar karatun Alƙur’ani ta ƙasa karo na 39 da aka gudanar a Birnin Kebbi, a Jihar Kebbi.

NAJERIYA A YAU: Ko Sulhu Da ’Yan Ta’adda Zai Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Arewa? Hanyoyi 6 da mutum zai kare kansa daga tsananin zafi

Wani jami’in gwamnati a Faskari, wanda ya nemi a sakaya sunansa, ya tabbatar da sace su.

“Malam Rabe da ’ya’yansa biyar, ciki har da Abdulsalam, wanda aka sace su a Bangori a kan titin Yankara. Har yanzu ba mu ji komai daga gare su ba.”

Abdulsalam, wanda ɗalibi ne a sashen likitanci na Jami’ar Ahmadu Bello (ABU), Zariya, ya samu matsayi na farko a gasar a ɓangaren maza bayan ya haddace Alƙur’ani.

Har yanzu ’yan sanda a Katsina ba su fitar da wata sanarwa kan lamarin ba.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Bindiga Gasar Karatu Gwarzo hari

এছাড়াও পড়ুন:

An kama tsohon fursuna ya je fashi da bindiga AK-47

Jami’an Rundunar Leƙen Asiri ta musamman a Jihar Kwara sun cafke wani tsohon ɗan gidan yari mai suna Godday Agaadi da bindiga ƙirar AK-47.

An kama Emmanuel Okah ne bayan an same shi da bindigar AK-47 da harsashi guda 25 a jikinsa, a lokacin da yake sanye da kayan ’yan sanda.

Dubunsa ta cika ne yana ƙoƙarin satar talotalo a unguwar Omu Aran da ke ƙaramar hukumar Irepodun.

Kwamishinan ’Yan Sanda na jihar, Adekimi Ojo, ya bayyana a taron manema labarai a ƙarshen mako cewa binciken da jami’an suka gudanar ne ya kai ga cafke Agaadi.

An kama sojojin da suka yi yunƙurin juyin mulki a Benin An gano gawar malamin Islamiyya da ya ɓace a Neja

Ya ƙara da cewa bincike ya ci gaba har ya kai ga kama wasu mutane biyu da ake zargin abokan aikinsa, ciki har da wani boka mai shekaru 41 mai suna Oyeniyi Olabode.

Kwamishinan ya ce babban wanda ake zargi tsohon ɗan gidan yari ne da ke da tarihin aikata laifukan tashin hankali a yankin Omu Aran.

’Ya tabbatar da cewa dukkansu uku suna hannun ’yan sanda, kuma ana ci gaba da bincike domin gano sauran mambobin ƙungiyar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Najeriya za ta buga wasan sada zumunta da Masar kafin fara gasar AFCON ta 2025
  • Dalibin jami’a ya rasu a hatsarin motar murnar kammala jarabawa
  • Nasarar Da Iran Ta Samu A Yakin Kwanaki 12 Kan HKI Yana Jawo Hankalin Kasashen Duniya
  • ’Yan jaridar Daily Trust da Trust TV sun lashe kyautar binciken ƙwaƙwaf ta Wole Soyinka ta bana
  • ‘Yan Bindiga 18 Sun Muta a Wata Arangama da Rundunar Operation Fansan Yamma
  • Zaben 2027: NNPP Ta Sha Alwashin Maye Gurbin Tinubu da Radda
  • HOTUNA: Dalibai 100 da aka sace sun iso Minna
  • Sojoji sun kashe ’yan bindiga 13, sun ceto ’yan kasuwa a Sakkwato
  • Najeriya: Gwamnatin Tarayya Ta Bada Sanarwan Kubutar Da Yan Makaranta 100 Da Aka Sace
  • An kama tsohon fursuna ya je fashi da bindiga AK-47