Aminiya:
2025-12-11@18:31:42 GMT

’Yan bindiga sun sace gwarzon gasar karatun Alƙur’ani a Katsina

Published: 13th, March 2025 GMT

’Yan bindiga sun sace gwarzon gasar karatun Alƙur’ani, Abdulsalam Rabi’u Faskari, tare da mahaifinsa da ’yan uwansa a Jihar Katsina.

Lamarin ya faru ne da yammacin ranar Talata a kusa da Labin Bangori, yayin da suke dawowa Faskari bayan Abdulsalam ya samu lambar yabo wadda Gwamna Dikko Radda ya ba shi saboda nasarar da ya samu a gasar karatun Alƙur’ani ta ƙasa karo na 39 da aka gudanar a Birnin Kebbi, a Jihar Kebbi.

NAJERIYA A YAU: Ko Sulhu Da ’Yan Ta’adda Zai Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Arewa? Hanyoyi 6 da mutum zai kare kansa daga tsananin zafi

Wani jami’in gwamnati a Faskari, wanda ya nemi a sakaya sunansa, ya tabbatar da sace su.

“Malam Rabe da ’ya’yansa biyar, ciki har da Abdulsalam, wanda aka sace su a Bangori a kan titin Yankara. Har yanzu ba mu ji komai daga gare su ba.”

Abdulsalam, wanda ɗalibi ne a sashen likitanci na Jami’ar Ahmadu Bello (ABU), Zariya, ya samu matsayi na farko a gasar a ɓangaren maza bayan ya haddace Alƙur’ani.

Har yanzu ’yan sanda a Katsina ba su fitar da wata sanarwa kan lamarin ba.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Bindiga Gasar Karatu Gwarzo hari

এছাড়াও পড়ুন:

Sakkwatawa na murnar kisan da sojoji suka yi wa mataimakin Bello Turji

Al’ummar ƙaramar hukumar Sabon Birni da ke jihar Sakkwato sun bayyana farin ciki bayan samun labarin kashe fitaccen ɗan bindiga da ya dade yana addabar yankin gabashin jihar, Kacalla Kallamu.

Rundunar Sojoji ta 8 ta hallaka jagoran ’yan bindiga, Kachalla Kallamu, a wani samamen haɗin gwiwa da aka kaddamar a ƙaramar hukumar Sabon Birni.

Dalibin jami’a ya rasu a hatsarin motar murnar kammala jarabawa Iya sojojin da ke tsaron Seyi Tinubu sun isa su samar da tsaro a Benin – Soyinka

Wata majiyar soja da ta tabbatar da lamarin ga manema labarai a ranar Talata ta bayyana samamen a matsayin “babbar asara ga cibiyar ’yan bindigar Bello Turji,” tana mai cewa Kallamu shi ne babban na hannun daman Turji.

A cewar majiyar, an kashe Kallamu tare da wani daga cikin manyan masu samar wa Turji kayayyakin aiki a lokacin samamen da aka gudanar da safe a kauyen Kurawa ranar Litinin.

Majiyar ta ƙara da cewa aikin ya samu muhimmiyar gudunmuwar kungiyoyin sa‑kai na yankin.

“Mun dade muna bibiyar Kallamu. Kashe shi wata babbar nasara ce wajen raunana karfin ’yan bindigar da ke Sabon Birni da kewaye,” in ji majiyar.

Mamacin, wanda asalin ɗan Garin Idi ne a Sabon Birni, ya dade yana addabar al’ummar yankin.

Ana zargin ya gudu zuwa Jihar Kogi bayan ya tsere wa luguden wutar sojoji a watan Yuni 2025, amma ya sake shigowa yankin kwanan nan ba tare da an sani ba.

Majiyar ta yaba da ƙarin bayanan sirri da ake samu daga al’ummomin yankin, tana mai cewa haɗin kai tsakanin mazauna yankin da jami’an tsaro ya taka muhimmiyar rawa wajen nasarorin baya‑bayan nan.

Manema labarai sun ruwaito cewa an ci gaba da murnar labarin a Sabon Birni, yayin da mashawarcin musamman ga Gwamna Ahmad Aliyu kan harkokin tsaro, Kanal Ahmed Usman (mai ritaya), ya yaba wa dakarun bisa “ci gaba da jajircewa da ƙwarewa” wajen yaƙi da ’yan bindiga.

Mutanen garin Sabon Birni sun fito maza da mata suna murnar nasarar da aka samu, har suna cewa suna jin wannan rana kamar ta Sallah.

Sun yi fatan a ci gaba da samun nasarori irin wannan domin kawar da ’yan bindiga a yankin, a jihar, da kuma Arewacin Najeriya gaba ɗaya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Katsina Ta Amince Da Bayar Da Alawus Na Naira 30,000 Duk Wata Ga Malaman Karkara
  • NAJERIYA A YAU: Alfanu Da Kalubalen Sabon Jadawalin Karatun Makarantu Da Gwamnati Ta Bijiro Dashi
  • Najeriya za ta buga wasan sada zumunta da Masar kafin fara gasar AFCON ta 2025
  • An kama wani mutum a Abuja yana ƙoƙarin kai harsasai ga ’yan bindiga a Zamfara
  • Sakkwatawa na murnar kisan da sojoji suka yi wa mataimakin Bello Turji
  • Dalibin jami’a ya rasu a hatsarin motar murnar kammala jarabawa
  • Nasarar Da Iran Ta Samu A Yakin Kwanaki 12 Kan HKI Yana Jawo Hankalin Kasashen Duniya
  • ’Yan jaridar Daily Trust da Trust TV sun lashe kyautar binciken ƙwaƙwaf ta Wole Soyinka ta bana
  • ‘Yan Bindiga 18 Sun Muta a Wata Arangama da Rundunar Operation Fansan Yamma
  • Zaben 2027: NNPP Ta Sha Alwashin Maye Gurbin Tinubu da Radda