Aminiya:
2025-11-25@06:52:05 GMT

’Yan bindiga sun sace gwarzon gasar karatun Alƙur’ani a Katsina

Published: 13th, March 2025 GMT

’Yan bindiga sun sace gwarzon gasar karatun Alƙur’ani, Abdulsalam Rabi’u Faskari, tare da mahaifinsa da ’yan uwansa a Jihar Katsina.

Lamarin ya faru ne da yammacin ranar Talata a kusa da Labin Bangori, yayin da suke dawowa Faskari bayan Abdulsalam ya samu lambar yabo wadda Gwamna Dikko Radda ya ba shi saboda nasarar da ya samu a gasar karatun Alƙur’ani ta ƙasa karo na 39 da aka gudanar a Birnin Kebbi, a Jihar Kebbi.

NAJERIYA A YAU: Ko Sulhu Da ’Yan Ta’adda Zai Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Arewa? Hanyoyi 6 da mutum zai kare kansa daga tsananin zafi

Wani jami’in gwamnati a Faskari, wanda ya nemi a sakaya sunansa, ya tabbatar da sace su.

“Malam Rabe da ’ya’yansa biyar, ciki har da Abdulsalam, wanda aka sace su a Bangori a kan titin Yankara. Har yanzu ba mu ji komai daga gare su ba.”

Abdulsalam, wanda ɗalibi ne a sashen likitanci na Jami’ar Ahmadu Bello (ABU), Zariya, ya samu matsayi na farko a gasar a ɓangaren maza bayan ya haddace Alƙur’ani.

Har yanzu ’yan sanda a Katsina ba su fitar da wata sanarwa kan lamarin ba.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Bindiga Gasar Karatu Gwarzo hari

এছাড়াও পড়ুন:

’Yan bindiga sun kashe ’yan sanda 5 a Bauchi

Rundunar ’Yan Sandan Jihar Bauchi, ta tabbatar da mutuwar wasu jami’anta guda biyar a ƙauyen Sabon Sara da ke Ƙaramar Hukumar Darazo, sakamakon harin da wasu ’yan bindiga suka kai.

Kakakin rundunar, CSP Ahmed Wakil ne, ya bayyana hakan cikin wata sanarwa a ranae Lahadi.

An ceto mutum 38 da aka sace a cocin Kwara — Tinubu Ɗalibai 50 da aka sace a Neja sun kuɓuta — CAN

“‘Yan sanda biyar sun rasu, biyu sun jikkata, amma an yi nasarar kashe wasu daga cikin ’yan bindigar a ƙauyen Sabon Sara, Ƙaramar Hukumar Darazo, a jihar Bauchi.”

Wakil, ya ƙara da cewa, “Ma’aikatanmu suna jajircewa kuma sun samu nasarar kashe wasu daga cikin ’yan bindigar yayin musayar wuta.”

Ya bayyana ’yan sanda suna aikin sintiri lokacin da aka kai musu harin.

Wakil, ya bayyana sunayen ’yan sandan da suka rasa rayukansu; DSP Ahmad Muhammad (SID), ASP Mustapha Muhammad (10 PMF), Amarhel Yunusa (10 PMF), Idris Ahmed (10 PMF), da Kofur Isah Muazu (AKU).

’Yan sandan da suka ji rauni sun haɗa da Isah Musa (SID) da Insifekta Yusuf Gambo (SID).

Ya ƙara da cewa, “Bayan samun rahoton, Shugaban ’yan sandan Ƙaramar Hukumar, SP Auwalu Ilu, ya jagoranci tawaga tare da ceto waɗanda suka jikkata.

“Sun kai waɗanda suka rasu Babban Asibitin Darazo, inda aka ajiye gawarwakin a ɗakin ajiyar gawa.

“Ana ƙokarin kama waɗanda suka aikata wannan mummunan laifi tare da hukunta su,” in ji Wakil.

Kwamishinan ’Yan Sandan jihar, CP Sani-Omolori Aliyu, ya ziyarci wajen da lamarin ya faru, sannan miƙa ta’aziyyarsa ga iyalan waɗanda suka rasu.

“Aikin nan ba abu ne mai sauƙi ba. Duk da haka, bisa doka, za mu ci gaba da jajircewa ba dare ba rana don tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyin jama’a.”

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sace ɗalibai: Idan Tinubu ba zai iya ba ya sauka kawai — PDP
  • Slot na fuskantar matsin lamba saboda rashin kataɓus a Liverpool
  • Sace ɗalibai: Ba rufe makarantu ba ne mafita — PDP
  • Najeriya: Kungiyar Yan Ta’adda Ta ISWAP Ta Sace Yan Mata 13 A Jihar Borno
  • ’Yan bindiga sun kashe ɗan kasuwa, sun sace matarsa a Bauchi
  • ’Yan bindiga sun kashe ’yan sanda 5 a Bauchi
  • Najeriya : An sako mutum 38 da ‘yan bindiga suka sace a jihar Kwara_Tinubu
  • An gano wurin da ’yan bindiga ke tsare da ɗalibai 25 da aka sace a Kebbi
  • Gwamnatin Katsina Ta Umurci a Gaggauta Rufe Dukkan Makarantun Jihar
  • Sace ɗalibai: An rufe makarantu a Katsina da Taraba