’Yan bindiga sun sace gwarzon gasar karatun Alƙur’ani a Katsina
Published: 13th, March 2025 GMT
’Yan bindiga sun sace gwarzon gasar karatun Alƙur’ani, Abdulsalam Rabi’u Faskari, tare da mahaifinsa da ’yan uwansa a Jihar Katsina.
Lamarin ya faru ne da yammacin ranar Talata a kusa da Labin Bangori, yayin da suke dawowa Faskari bayan Abdulsalam ya samu lambar yabo wadda Gwamna Dikko Radda ya ba shi saboda nasarar da ya samu a gasar karatun Alƙur’ani ta ƙasa karo na 39 da aka gudanar a Birnin Kebbi, a Jihar Kebbi.
Wani jami’in gwamnati a Faskari, wanda ya nemi a sakaya sunansa, ya tabbatar da sace su.
“Malam Rabe da ’ya’yansa biyar, ciki har da Abdulsalam, wanda aka sace su a Bangori a kan titin Yankara. Har yanzu ba mu ji komai daga gare su ba.”
Abdulsalam, wanda ɗalibi ne a sashen likitanci na Jami’ar Ahmadu Bello (ABU), Zariya, ya samu matsayi na farko a gasar a ɓangaren maza bayan ya haddace Alƙur’ani.
Har yanzu ’yan sanda a Katsina ba su fitar da wata sanarwa kan lamarin ba.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Bindiga Gasar Karatu Gwarzo hari
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamna Abba ya gabatar da kasafin 2026 na N1.36trn
Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya gabatar da kasafin 2026 na kuɗi Naira tiriliyan 1.36 tiriliyan a Majalisar Dokokin jihar.
Kasafin wanda aka yi laƙabi da “Kasafin Gine-gine, Ci Gaban Kowa da Ɗorewar Ci Gaba.”
Dukiyar sama da miliyan 500 ta kone a gobarar kasuwar katako ta Gombe Tinubu ya fasa zuwa taron G20 saboda matsalar tsaro a NajeriyaYayin jawabi da ya gabatar a zauren majalisar a ranar Laraba, gwamnan ya ce an tsara kasafin ne don samar da sauye-sauye, kammala manyan ayyuka, inganta ilimi da harkar kiwon lafiya.
Ya bayyana cewa za a kashe Naira biliyan 934.6 (kashi 68) a manyan ayyuka kamar hanyoyi, gine-gine da sauran muhimman ayyuka.
Sauran Naira biliyan 433.4 (kashi 32), za su tafi ne a ayyukan yau da kullum.
Gwamna Abba ya ce ya aiwatar da kashi 80 na alƙawuran da ya yi a lokacin yaƙin neman zaɓe.
Ya ce kasafin 2026 zai mayar da hankali ne wajen kammala ayyuka a birane, faɗaɗa gidaje da kuma tallafa wa ƙananan masana’antu.
Ya fara jawabinsa da jajanta wa iyalan hamshaƙin attajiri Alhaji Aminu Alhassan Dantata, Galadiman Kano Alhaji Abbas Sanusi, da tsohon ɗan siyasa Alhaji Ahmadu Haruna Zago, waɗanda suka rasu a wannan shekara.
Hakazalika, ya yi jimamin rasuwar tsohon Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari da ’yan wasan Kano 22 da suka rasu a hatsarin mota a watan Mayu.
Abba, ya ce an aiwatar da kashi 75 na kasafin 2025 daga Janairu zuwa Oktoban wannan shekara, wanda a cewarsa an samu ci gaba mai kyau.
Ɓangaren ilimi ya samu Naira biliyan 280.6 (kashi 31) a 2025.
Ayyukan da aka yi sun haɗa da gyaran azuzuwa, shirye-shiryen ilimi kyauta, biyan kuɗin NECO, bayar da tallafin karatu, kafa Kwalejin Kimiyya da Fasaha ta Gaya, ɗaukar malaman darasin lissafi guda 400, masu gadi 1,600 da gyaran manyan makarantun sakandare.
Ya ce wannan ya taimaka wa Kano wajen zama ta farko a sakamakon NECO na 2025 a Najeriya.
A ɓangaren lafiya kuwa, gwamnatinsa ta kashe Naira biliyan 149.7 biliyan wajen gyara asibitoci a ƙananan hukumomi, inganta inshorar lafiya.
Sauran sun haɗa da ƙaddamar da shirin Abba-Care, gyaran cibiyoyi, da samar da kayan aikin lafiya da hanyoyin samar da wuta a manyan asibitoci.
Gwamnatinsa ta sayi buhun taki 199,000, ta raba wa al’umma shinkafa, ta amince da gina ƙananan madatsun ruwa 11, sannan ta ɗauki sababbin ma’aikatan aikin gona.
Ayyukan da aka yi sun haɗa da faɗaɗa tituna, siyan na’urar lantarki, saka fitilu a kan tituna, gyara masallatai, da samar da gidaje a sassa daban-daban na jihar.
Gwamnatin ta farfaɗo da cibiyoyin ɗinka kaya a ƙananan hukumomi 44, ta gyara manyan kasuwanni, ta tallafa wa ƙananan ’yan kasuwa, sannan ta shirya bukukuwan al’adu kamar KANFEST.
Haka kuma ta aiwatar da dokar canjin yanayi, ta share magudanan ruwa, ta sayi kayan sarrafa shara, ta kuma shuka bishiyoyi sama da miliyan 5.5.
Gwamna Abba, ya ce Hukumar Kula da Tsaro ta Jihar Kano, ta horar da jami’ai 2,000, ta kuma samar da kayan sintiri 6,000.
Matasa sama da 5,384 sun amfana da shirin tallafin Naira miliyan 800; dubban mata sun samu dabbobi; ƙananan ’yan kasuwa sun samu tallafin Naira 50,000 kowannensu.
A kasafin 2026, an raba jadawalin yadda kowane ɓangare zai samu:
Ilimi: Naira biliyan 405.3 (kashi 30) Lafiya: Naira biliyan 212.2 (kashi 16) Gine-gine: Naira biliyan 346.2 biliyan (kashi 25)Sauran sassa kamar noma, tsaro, kasuwanci, ruwa, muhalli da ci gaban matasa suma sun samu kuɗi mai yawa.
Gwamnan ya roƙi majalisar da ta hanzarta amincewa da kasafin, inda ya ce kasafin zai taimaka wajen samar wa al’ummar Kano ci gaba mai tarin yawa.
Ya gode wa ma’aikata, hukumomi, da al’ummar Kano kan goyon bayan da suke bai wa gwamnatinsa.
Kakakin Majalisar Dokokin jihar, Ismail Jibril Falgore, ya tabbatar da cewa majalisar za ta hanzarta amincewa da kasafin da zarar ta kammala nazarinsa.