Aminiya:
2025-06-15@23:15:42 GMT

Ana fargabar ɓarkewar Sanƙarau a Sakkwato

Published: 11th, March 2025 GMT

An gargaɗi mazauna da su kwana cikin shirin daƙile yaɗuwa cutar Sanƙarau a yayin da cututtuka masu alaƙa da ita suka soma bayyana a wasu ƙananan hukumomin Jihar Sakkwato.

Kwamishinan Lafiya na jihar, Dakta Faruk Umar Wurno ne ya yi wannan gargaɗi haɗi da bayar da shawarar a wani jawabi da ya fitar a ranar Talata.

Lakurawa sun kashe mutum 13 a ƙauyukan Kebbi Tsohon shugaban Philippines ya faɗa komar ’yan sanda

Kwamishinan ya yi bayanin cewa ya zama wajibi duk wasu alamomi da aka gani a ɗauka a shiga da su ɗakin gwaje-gwaje a bincika domin a tabbatar ko ƙoshin lafiyar al’umma.

Dakta Faruk Umar ya ce ma’aikatarsa za ta saka ido kan jami’an lafiya na gwamnati da masu zaman kansu domin a tabbatar an daƙile yaɗuwar cutar.

Ya gargaɗi mazauna cewa a koyaushe su kasance a ankare wurin ɗaukar matakin kariya ga cututtuka na yau da kullum.

Ya buƙaci jama’a su riƙa gaggauta sanar da jami’an kiwon lafiya mafi kusa da zarar sun ga wata alama ta rashin lafiya kamar zazzaɓi ko ciwon kai mai tsanani.

Kwamishinan ya nanata muhimmancin tabbatar da tsaftar jiki da muhalli sannan jama’a su yi iya ƙoƙari wajen kaucewa shiga cunkoso da zama a wurin da iska ta wadata.

Ya buƙaci jama’a da su kai rahoton duk wata alama ta cuta ko wata rashin lafiya da ba a saba da ita ba a asibiti mafi kusa.

A kwanakin dai zafi yana tsananta a wasu jihohin ƙasar ciki har da Sakkwato, lamarin da babu shakka yana da nasaba da haddasa yaɗuwar cutar ta Sanƙarau.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Jihar Sakkwato Sanƙarau

এছাড়াও পড়ুন:

Ya kamata Isra’ila da Iran su kawo ƙarshen rikicin da ke tsakaninsu

Gwamnatin Tarayya ta roƙi ƙasashen Isra’ila da Iran da su daina rikici, su zauna lafiya su sasanta tsakaninsu.

A wata sanarwa da Ma’aikatar Harkokin Waje ta fitar, ta bayyana damuwa kan yadda rikicin ke ƙara ta’azzara, inda ta nemi ɓangarorin biyu da su kai zuciya nesa don samar da zaman lafiya a duniya baki ɗaya.

Mahara sun kashe mutum 26 a sabon hari a Binuwai Mulkin Tinubu ya fi kowane muni tun bayan dawowar mulkin farar hula — Dalung

Sanarwar ta ce faɗa da ramuwar gayya na jefa rayukan fararen hula cikin hatsari, kuma yana iya haddasa rikici mai muni a yankin Gabas ta Tsakiya, wanda hakan zai iya barazana ga tsaron duniya da kuma ci gaban tattalin arziƙi dunuya.

“Mu a matsayimmu na ƙasa mai son zaman lafiya, muna roƙon ƙasashen da ke rikici da su zauna su tattauna maimakon su ci gaba da faɗa.”

Gwamnatin Tarayya ta kuma yi kira ga ƙasashen duniya, musamman Kwamitin Tsaro na Majalisar Ɗinkin Duniya, da su ɗauki matakai don hana yaɗuwar rikicin da kuma samo hanyar warware matsalar.

Sanarwar ta ƙara da cewa amfani da ƙarfin soji ba shi da amfani matuƙa, domin faɗa ba zai kawo sauƙi ba.

Najeriya ta ce a shirye ta ke ta bayar da taimako domin hana yaɗuwar rikicin da kuma tabbatar da zaman lafiya a yankin.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Mataimakin Gwamnan Sakkwato bai karɓi shanun tallafin layya ba — Hukumar Zakka
  • Wata Sabuwa: Malaman Jami’ar Tarayya A Kano Sun ƙi Amince Wa Da Zaɓen Sabon VC
  • Ba Zai Manta Da Shawarar Mahaifinsa Ba
  • Yadda wani ɗan sanda ya rasu a hanyar zuwa ɗaurin aurensa
  • Oman ta tabbatar da soke tattaunawar Iran da Amurka zagaye na shida
  • An samu gobara a wasu matatun mai guda biyu na Iran bayan harin da Isra’ila ta kai
  • Trump ya dakatar da kamen baƙin haure a wasu wurare na Amurka
  • Isra’ila da Iran su daidaita rikicin da ke tsakaninsu — Gwamnatin Tarayya
  • Damina: NiMet ta gargaɗi jihohi 13 kan barazanar ambaliyar ruwa
  • Ya kamata Isra’ila da Iran su kawo ƙarshen rikicin da ke tsakaninsu