Aminiya:
2025-11-03@08:03:51 GMT

An hana tashe bana a Kano — Nalako

Published: 11th, March 2025 GMT

Kamar yadda ta riƙa kasancewa a shekarun baya bayan nan, bana ma dai jami’an tsaro sun haramta al’adar nan ta tashe da aka saba gudanarwa daga zarar an kai azumi na goma a watan Ramadana.

Auwalu Sani Nalako, Sarkin Gwagwaren Kano kuma jagoran dabbaka al’adar tashe ne ya tabbatar hakan yayin hirarsa da manema labarai a ranar Litinin.

NAJERIYA A YAU: Abubuwan Da ke Shirin Faruwa A Fagen Siyasar Najeriya ’Yan bindiga sun kashe manoma 14 a Ondo

Nalako ya ce dalilai na tsaro da rundunar ’yan sandan jihar ta bayar ne ya sanya su ma suka dakatar da wasannin tashen na bana.

A cewarsa, jami’an tsaron sun tattaro bayanan sirri da ya tabbatar musu da cewa akwai miyagu waɗanda suke shirin fakewa da tashen domin tayar da hargitsi.

A shekarun baya dai an riƙa samun wasu ɓata-gari da ke ribatar lokacin gudanar da wannan al’ada suna kai hare-hare kan waɗanda ba su ji ba ba su gani ba.

Al’adar tashe

Bisa al’ada dai ana yin wasannin tashe ga wanda ya yi aure amma ya mutu, da gidajen masu kuɗi, sarakuna, da sauransu.

Tashe wata al’ada ce da ake gudanarwa daga kwana 10 na watan Ramadan har zuwa daren sallah.

Masu tashe, yawancinsu ƙananan yara, cikin shiga ta ban dariya, sukan zaga kwararo-kwararo a unguwanni da kasuwanni suna nishadantar da mutane da abubuwan barkwanci da ba’a da dai sauransu domin debe musu gajiyar azumi.

Aminiya ta binciko muku asali da tarihi da sauran muhimman abubuwa game da wannan al’ada da ke gudana a cikin watan Ramadan mai alfarma, a kasar Hausa.

Asalin kalmar tashe

Masana sun bayyana cewa asalin tashe ana yin sa ne da dare, kuma bakuwar al’ada ce da malam Bahaushe ya samu daga baya.

Farfesa Aliyu Muhammadu Bunza malami ne a Sashen Koyar da Harsunan Najeriya a Jami’ar Usmanu Danfodio da ke Sakkwato.

Ya bayaya wa Aminiya cewa, “Kalmar tashe ta samo asali ne daga a tashi, wato a tashe su daga barci.”

Tarihin tashe

Ita dai wannan al’ada a cewar Farfesa Bunza, ba a san bahaushe da ita ba sai bayan zuwan Musulunci kasar Hausa.

Tashe “Ya samu tarihin Bahaushe ne a watan azumi na Ramdan; wannan ya nuna bakon abu ne, domin gabanin zuwan Musulunci babu,” inji shi.

Ya ce masana al’ada na ganin tashe ya samo asali ne daga Daular Andalus, “Can ne Musulmi suka kusa kusanta da al’adu, domin da kidin taushi da tashe duk daga can suka samo asali.”

Dalilin yin tashe

Farfesa Bunza ya bayyana cewa asalin makasudin yin tashe shi ne a tayar da mutane daga barci su yi sahur a watan azumin Ramadan.

“Har yanzu [a Daular Andalus] suna yin tashen, wanda za a tayar da mutane da dare domin su samu su yi sahur.”

Daga baya “Abin ya koma wasan yara na jan hankalin jama’a da faranta musu rai da debe musu gajiya da takaici da wahala.”

Tashe a al’adar Bahaushe

A ƙasar Hausa akan fara yin tashe ne a 10 na tilas, wato kwana 10 na biyu cikin watan Ramadan domin sanya wa mutane nishadi.

Bahaushe ya kasa watan azumin Ramadan zuwa gida kuna: ‘10 Na Marmari’, ‘10 Na Wuya’, da kuma ‘10 Na Ɗokin Sallah’.

Malamin ya bayyana cewa Bahaushe ya zaɓi ‘10 Na Wuya’ a matsayin lokacin fara tashe.

“A ‘10 Na Marmari Bahaushe ya ga bai ma kamata a yi tashe a lokacin ba, sai an shiga 10 Na Wuya, lokacin an ɗan fara gajiya da azumin.

“Saboda haka sai a riƙa yin tashe ana sa mutane fara’a da farin ciki, su kuma suna ba da kyauta da sadaka.”

Muhimmancin Tashe

Game da hikima da kuma amfaninsa, Farfes Bunza ya ce tashe kan nuna duk yanayi da mutane suke ciki a shekarar, kuma akwai darasi a cikinsa.

“Su yaran suna kokarin su bayyana halayya da duk wani yanayi da mutane suke ciki.

“Da za a saurari tashen yaran za a ga manyan maganganu ne da manya suka sa musu a baki.

Ya ce, “Cikin tashe ana gina wa yara kunya, kokari, kwazo, son gaskiya, son juna da sauransu.”

Tasirin tashe

“Malamai sun gaya mana cewa tashe shi ne musabbabin samuwar wasu fitattun mawakan kasar Hausa; daga wakokin tashe suka samu shahara, maza da mata.

“Saboda haka tashe wani abu ne na sada zumunci da kokarin lurar da mutane [irin] halin da ake ciki, da yadda ya kamata a fuskance su.

“Don yanzu ga shi nan na ga wata yarinya tana tashe a kan bilicin, ba mamaki a samu wata kuma tana tashe a kana ta’addanci.

“Mu nuna wa mutane cewa ta’addanci fa ba zai yiwu ba, dole mu zauna lafiya; saboda haka yaran nan karatu ne suke mana mai zurfi.”

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Jihar Kano watan Ramadan Bahaushe ya

এছাড়াও পড়ুন:

Kotu ta tsige dan majalisar da ya sauya sheka zuwa APC

Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta tsige dan majalisar wakilai, Abubakar Gummi daga kujerarsa saboda sauya sheka daga jam’iyyar PDP zuwa APC.

Gummi yana wakiltar mazabar Gummi/Bukkuyum ta Jihar Zamfara a majalisar wakilai.

An raba wa iyalan jami’an ’yan sandan da suka rasu a bakin aiki a Borno N63.4m An sake kama shi a cikin ’yan fashi kwana 5 da fitowa daga kurkuku

Mai shari’a Obiora Egwuatu ne, ya yanke hukuncin, inda ya umarci kakakin majalisar wakilai, Tajudeen Abbas, da ya daina amincewa da Gummi a matsayin dan majalisar da ke wakiltar mazabar Gummi/Bukkuyum.

Haka kuma ya umarci hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) da ta shirya sabon zabe cikin kwanaki 30 domin cike gurbin kujerar dan majalisar.

Jam’iyyar PDP tare da shugaban ta na jihar Zamfara, Jamilu Jibomagayaki, ne suka shigar da karar dan majalisar.

Sun ce bai dace Gummi ya ci gaba da zama a kujerar ba bayan barin jam’iyyar da ta tsayar da shi takara.

Gummi, ta bakin lauyansa ya ce ya fice daga PDP ne saboda rikicin cikin gida da jam’iyyar ke fama da shi a matakin kasa da kuma a mazabarsa.

Amma kotu ta yi watsi da wannan hujjar, inda ta bayyana cewa babu takaddama da za ta ba shi damar ya sauya sheka.

A hukuncin da ya yanke, Mai shari’a Egwuatu ya ce ’yan siyasa dole su mutunta zabin jama’ar da suka kada musu kuri’a a karkashin jam’iyyar da ta tsayar da su takara.

Ya ce doka ba ta yadda da dan siyasa ya bar jam’iyyar da ta taimaka masa wajen lashe zabe sannan ya koma wata jam’iyya ba tare da ajiye mukaminsa ba.

Ya kara da cewa kuri’un da aka kada don dan takarar na jam’iyya ne, ba nasa ne na kashin kansa ba.

“Idan mutum yana son sauya sheka, ka da ya dauki amanar jama’ar da ta zabe shi ya tafi da ita,”  in ji alkalin.

Kotu ta kuma umarci Gummi da ya daina karbar albashi da wasu hakkoki a matsayin dan majalisa, tare da mayar da duk kudaden da ya karba daga ranar 30 ga watan Oktoba, 2024, zuwa ranar da aka yanke hukuncin.

Haka kuma, ya gabatar da hujjar mayar da kudaden ga kotu cikin kwanaki 30.

Mai shari’a Egwuatu ya kuma ci Gummi tarar Naira N500,000, domin biyan PDP kudaden da ta kashe wajen shigar da kara.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kano Pillars Ta Koma Matsayi Na 20 Bayan Shan Kashi A Hannun Enyimba
  • 2027: Yadda Gwamnoni Suka Yi Fatali Da Mataimakansu Wajen Zaɓo Waɗanda Za Su Gaje Su
  • Gidauniyar IRM Da KADCHMA, Ta Ƙaddamar Da Inshorar Lafiya Kyauta Ga Mutane 200 A Kaduna
  • Gwamnatin Isra’ila Tana Ci Gaba Da Hana Masu Jinya Zuwa Kasashen Waje Neman Magani Daga Gaza
  • An Kashe Mutum 3 Yayin Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Hari Kan Iyakokin Kano
  • Isra’ila Ta Kashe Mutane 4 Tare Da Jikkata Wasu Guda 3 A Kudancin Labanon
  •  Gaza: Daga Tsagaita Wuta Zuwa Yanzu Fiye Da Mutane 200 Ne Su Ka Yi Shahada
  • An Tsare Wani Mutum A Gidan Yari Kan Zargin Kashe Matarsa Saboda Ƙuli-Ƙuli A Kano
  • Iran Ta Sanya  Da Ranar 30 Ga Watan Nuwamba A Matsayin Ranar Kasa Ta Tsibirai 3
  • Kotu ta tsige dan majalisar da ya sauya sheka zuwa APC