Aminiya:
2025-07-09@05:47:19 GMT

An hana tashe bana a Kano — Nalako

Published: 11th, March 2025 GMT

Kamar yadda ta riƙa kasancewa a shekarun baya bayan nan, bana ma dai jami’an tsaro sun haramta al’adar nan ta tashe da aka saba gudanarwa daga zarar an kai azumi na goma a watan Ramadana.

Auwalu Sani Nalako, Sarkin Gwagwaren Kano kuma jagoran dabbaka al’adar tashe ne ya tabbatar hakan yayin hirarsa da manema labarai a ranar Litinin.

NAJERIYA A YAU: Abubuwan Da ke Shirin Faruwa A Fagen Siyasar Najeriya ’Yan bindiga sun kashe manoma 14 a Ondo

Nalako ya ce dalilai na tsaro da rundunar ’yan sandan jihar ta bayar ne ya sanya su ma suka dakatar da wasannin tashen na bana.

A cewarsa, jami’an tsaron sun tattaro bayanan sirri da ya tabbatar musu da cewa akwai miyagu waɗanda suke shirin fakewa da tashen domin tayar da hargitsi.

A shekarun baya dai an riƙa samun wasu ɓata-gari da ke ribatar lokacin gudanar da wannan al’ada suna kai hare-hare kan waɗanda ba su ji ba ba su gani ba.

Al’adar tashe

Bisa al’ada dai ana yin wasannin tashe ga wanda ya yi aure amma ya mutu, da gidajen masu kuɗi, sarakuna, da sauransu.

Tashe wata al’ada ce da ake gudanarwa daga kwana 10 na watan Ramadan har zuwa daren sallah.

Masu tashe, yawancinsu ƙananan yara, cikin shiga ta ban dariya, sukan zaga kwararo-kwararo a unguwanni da kasuwanni suna nishadantar da mutane da abubuwan barkwanci da ba’a da dai sauransu domin debe musu gajiyar azumi.

Aminiya ta binciko muku asali da tarihi da sauran muhimman abubuwa game da wannan al’ada da ke gudana a cikin watan Ramadan mai alfarma, a kasar Hausa.

Asalin kalmar tashe

Masana sun bayyana cewa asalin tashe ana yin sa ne da dare, kuma bakuwar al’ada ce da malam Bahaushe ya samu daga baya.

Farfesa Aliyu Muhammadu Bunza malami ne a Sashen Koyar da Harsunan Najeriya a Jami’ar Usmanu Danfodio da ke Sakkwato.

Ya bayaya wa Aminiya cewa, “Kalmar tashe ta samo asali ne daga a tashi, wato a tashe su daga barci.”

Tarihin tashe

Ita dai wannan al’ada a cewar Farfesa Bunza, ba a san bahaushe da ita ba sai bayan zuwan Musulunci kasar Hausa.

Tashe “Ya samu tarihin Bahaushe ne a watan azumi na Ramdan; wannan ya nuna bakon abu ne, domin gabanin zuwan Musulunci babu,” inji shi.

Ya ce masana al’ada na ganin tashe ya samo asali ne daga Daular Andalus, “Can ne Musulmi suka kusa kusanta da al’adu, domin da kidin taushi da tashe duk daga can suka samo asali.”

Dalilin yin tashe

Farfesa Bunza ya bayyana cewa asalin makasudin yin tashe shi ne a tayar da mutane daga barci su yi sahur a watan azumin Ramadan.

“Har yanzu [a Daular Andalus] suna yin tashen, wanda za a tayar da mutane da dare domin su samu su yi sahur.”

Daga baya “Abin ya koma wasan yara na jan hankalin jama’a da faranta musu rai da debe musu gajiya da takaici da wahala.”

Tashe a al’adar Bahaushe

A ƙasar Hausa akan fara yin tashe ne a 10 na tilas, wato kwana 10 na biyu cikin watan Ramadan domin sanya wa mutane nishadi.

Bahaushe ya kasa watan azumin Ramadan zuwa gida kuna: ‘10 Na Marmari’, ‘10 Na Wuya’, da kuma ‘10 Na Ɗokin Sallah’.

Malamin ya bayyana cewa Bahaushe ya zaɓi ‘10 Na Wuya’ a matsayin lokacin fara tashe.

“A ‘10 Na Marmari Bahaushe ya ga bai ma kamata a yi tashe a lokacin ba, sai an shiga 10 Na Wuya, lokacin an ɗan fara gajiya da azumin.

“Saboda haka sai a riƙa yin tashe ana sa mutane fara’a da farin ciki, su kuma suna ba da kyauta da sadaka.”

Muhimmancin Tashe

Game da hikima da kuma amfaninsa, Farfes Bunza ya ce tashe kan nuna duk yanayi da mutane suke ciki a shekarar, kuma akwai darasi a cikinsa.

“Su yaran suna kokarin su bayyana halayya da duk wani yanayi da mutane suke ciki.

“Da za a saurari tashen yaran za a ga manyan maganganu ne da manya suka sa musu a baki.

Ya ce, “Cikin tashe ana gina wa yara kunya, kokari, kwazo, son gaskiya, son juna da sauransu.”

Tasirin tashe

“Malamai sun gaya mana cewa tashe shi ne musabbabin samuwar wasu fitattun mawakan kasar Hausa; daga wakokin tashe suka samu shahara, maza da mata.

“Saboda haka tashe wani abu ne na sada zumunci da kokarin lurar da mutane [irin] halin da ake ciki, da yadda ya kamata a fuskance su.

“Don yanzu ga shi nan na ga wata yarinya tana tashe a kan bilicin, ba mamaki a samu wata kuma tana tashe a kana ta’addanci.

“Mu nuna wa mutane cewa ta’addanci fa ba zai yiwu ba, dole mu zauna lafiya; saboda haka yaran nan karatu ne suke mana mai zurfi.”

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Jihar Kano watan Ramadan Bahaushe ya

এছাড়াও পড়ুন:

Hukumar Abinci Ta Duniya ( WFP) Ta Jefa Wa Mutanane Kudancin Sudan Abinci Ta Sama

Hukumar abinci ta duniya ta fara aikewa da kayan abinci zuwa kudancin Sudan, ta hanyar amfani da jiragen sama domin jefa kayan agaji ga mazauna Kudancin Sudan da sauran yankunan da suke a killace tun cikin watan Maris.

Tun watanni 4 da su ka gabata ne dai hukumar abincin ta duniya ta fara aikewa da kayan agaji a kudancin Sudan din, bayan da fada mai tsanani ya hana a iya bi ta hanyoyin kasa.

A gefe daya, shugabar kungiyar ta Abinci reshen Afirka Mary Elen macgroti ta ce, fada da ake ci gaba da yi a yankin ya haddasa karacin ab inci, tare da yin kira da a dauki matakin gaggawa domin magance wannan matsala.

Da akwi mutane kusan miliyan daya a yankin tekun Nilu  da suke fuskantar yunwa mai tsanani, wasu 34,000 daga cikinsu yanayinsu ya fi tsananta.

Tun da yaki ya barke a kasar Sudan a 2023, masu bukatuwa da taimako suke kara yawa, da hakan ya tilastawa miliyoyi yin hijira zuwa kasashen makwabta da kuma a cikin gida.

A kasar Habasha kadai da akwai ‘yan hijirar Sudan da sun kai 50,000, kamar yadda hukar ta ambata.

A cikin jahohin Nilul-A’ala, da Arewacin Junqali kadai, hukumar Abincin ta Duniya tana son kai wa mutane 470,000 taimakon abinci daga nan zuwa watan Ogusta.

Sai dai hukumar taka korafin karancin abinci, ta yadda ya zuwa yanzu yake da bukatuwa da dalar Amurka miliyan 274 daga nan zuwa karshen wannan shekara. Yunwa tana yin barazana ga rayuwar mutane miliyan 7.7 a kudancin Sudan, amma a halin yanzu, hukumar za ta iya ciyar da mutane miliyan 2.5 ne kadai.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Hukumar Abinci Ta Duniya ( WFP) Ta Jefa Wa Mutanane Kudancin Sudan Abinci Ta Sama
  • TCN Ta Wayar Da Kan Al’ummomin Kaduna Kan Illar Lalata Kayan Wuta Da Gini Karkashen Babbar Wayar Wuta 
  • Asibiti Mai Zaman Kansa A Kano Zai Fara Aikin Manyan Tiyatu Tare Da Rage Kuɗi Kaso 50%
  • Asibiti Mai Zaman Kansa A Kano Zai Fara Manya Manyan Tiyatu Tare Da Rage Kuɗi Kaso 50%
  • Mutane 21 Suka Mutu A Hatsarin Mota A Hanyar Zaria Zuwa Kano
  • An Kaddamar Da Shirin Samar Da Wutar Lantarki A Jami’ar Kashere Gombe.
  • Kano ta sami rahoton cin zarafin yara 351 – NHRC
  • Zulum ya musanta shirin ficewa daga APC
  • Majalisar Dattawa ta gindaya sharaɗin dawo da Sanata Natasha
  • Akalla Mutane 52 Suka Rasa Rayukansu Saboda Ambaliyan Ruwan Sama A Jihar Texas Na Kasar Amurka