NAJERIYA A YAU: Ladan Da Mai Aikin Ƙarfi Yake Samu A Lokacin Azumi
Published: 10th, March 2025 GMT
More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba
Watan azumi lokaci ne da akan samu wasu ma’aikatu sun sassauta wa ma’aikata ta hanyar yi musu rangwame kamar rage musu yawan sa’o’in aiki.
Sai dai a lokacin da waɗannan mutane suke samun rangwame, akwai waɗanda suke ayyuka ko sana’o’in da suka dogara da su ciyar da iyalansu.
Sau da dama irin waɗannan mutane sai sun fita sun yi aiki a rana, duk da suna azumi, suke samun abin da za su saka a bakin salati.
NAJERIYA A YAU: Falalar Buɗa-baki Cikin Iyali A Lokacin Azumi DAGA LARABA: Yadda Zawarawa Suke Ɗanɗana Kuɗa A Watan RamadanaShirin Najeriya a Yau na wannan lokaci zai yi duba ne kan irin ladan da masu aikin ƙarfi suke samu yayin da suke azumi.
Domin sauke shirin, latsa nan
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Aikin karfi Watan Azumi
এছাড়াও পড়ুন:
Farfesa na Farko a fannin Ilimi a Arewa, Adamu Baikie, ya rasu yana da shekara 94
Allah Ya yi wa Farfesa Adamu Baikie, wanda ya kasance Farfesa na farko a fannin Ilimi daga Arewacin Najeriya, rasuwa.
Farfesa Adamu Bakie ya rasu yana da shekaru 94 ne a daren Jumma’a a gidansa da ke Zariya, Jihar Kaduna.
Babban ɗansa, Manjo Muhammad Adamu (Ritaya), ya tabbatar da rasuwar, inda ya ce za a sanar da jama’a cikakkun bayanai da lokacin da za a gudanar da jana’izarsa daga baya.
Baikie ya shahara sosai wajen gina fannin ilimi a Najeriya, inda ya yi aiki a manyan makarantu da dama.
Kotu ta sa ranar yanke hukunci a Shari’ar Abba Kyari da NDLEA Gwamnatin Kano ta haramta kafa hukumar Hisbah mai zaman kantaYa taɓa zama Shugaban Jami’a a wasu jami’o’in Najeriya, kuma ya jagoranci wata jami’a a Kudancin Afirka a lokacin aikinsa.
An haifi Farfesa Adamu Baikie ne a Wusasa, Zariya a 1931 saidai ya girma ne Sabon garin Kano, inda ya yi karatun firamare kafin daga baya ya dawo makarantar middle a Zaria a shekarar 1948.
Ya zama farfesa na farko a ɓangaren ilmi daga Arewacin Najeriya a 1971.
Ana kallon da a matsayin jigo wajen kafa tsare-tsaren koyar da malamai, tare da samar da gudummawar da ta ɗore a bangaren ilimi na Najeriya.
Ya rasu ya bar ’ya’ya biyar.