NAJERIYA A YAU: Ladan Da Mai Aikin Ƙarfi Yake Samu A Lokacin Azumi
Published: 10th, March 2025 GMT
More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba
Watan azumi lokaci ne da akan samu wasu ma’aikatu sun sassauta wa ma’aikata ta hanyar yi musu rangwame kamar rage musu yawan sa’o’in aiki.
Sai dai a lokacin da waɗannan mutane suke samun rangwame, akwai waɗanda suke ayyuka ko sana’o’in da suka dogara da su ciyar da iyalansu.
Sau da dama irin waɗannan mutane sai sun fita sun yi aiki a rana, duk da suna azumi, suke samun abin da za su saka a bakin salati.
NAJERIYA A YAU: Falalar Buɗa-baki Cikin Iyali A Lokacin Azumi DAGA LARABA: Yadda Zawarawa Suke Ɗanɗana Kuɗa A Watan RamadanaShirin Najeriya a Yau na wannan lokaci zai yi duba ne kan irin ladan da masu aikin ƙarfi suke samu yayin da suke azumi.
Domin sauke shirin, latsa nan
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Aikin karfi Watan Azumi
এছাড়াও পড়ুন:
’Yan kasar Chadi 3 sun mutu a hatsarin kwalekwale a Borno
Wani kwalekwale da ke ɗauke da fasinjoji takwas ya kife yayin da yake ƙetare kogin da ke kan iyaka da garin Gamboru na Najeriya da Fotokol a ƙasar Kamaru, inda mutane uku suka mutu.
Lamarin ya faru ne da misalin qarfe 6:30 na yamma lokacin da kwalekwalen, wanda wani Mamman Nur Abbagana na Kasuwan Katako, Gamboru ke tuƙa shi ya kife a tsakiyar ruwa tare da jefa dukkan fasinjoji cikin ruwa.
Majiyoyin tsaro sun tabbatar da cewa dukkan fasinjoji takwas ’yan ƙasar Chadi ne da ke tafiya daga Jos, Jihar Filato, a kan hanyarsu ta zuwa N’Djamena, Jamhuriyar Chadi.
An ceto fasinjoji biyar, waɗanda aka tabbatar da suna raye ba su mutu ba.
Yadda za ku cike neman aikin jami’an lafiya a Hajjin 2026 da NAHCON Kotu ta sa ranar yanke hukunci a Shari’ar Abba Kyari da NDLEAWata mata mai suna Alphosine Makebu Beboroum, mai shekaru 34, da ’ya’yanta mata biyu Centich Mamajibe, mai shekaru 3, da Mamajilem Bebaroum, ‘yan watanni 10, sun nutse kuma har yanzu ba a gano su ba har zuwa Kammala wannan rahoto, duk da ana cigaba da gudanar da aikin ceto da bincike.
A halin yanzu, hukumomin ’yan sanda sun kuma tabbatar da kama mai tuƙa kwale-kwalen saboda karya umarnin gwamnatin Jihar Borno na tilasta wa duk masu aikin kwalekwale da su yi amfani da jakar ceto.
Kakakin rundunar ASP Nahum Kenneth Daso ya ce ana ci gaba da gudanar da bincike kan musabbabin faruwar lamarin.