Aminiya:
2025-12-03@17:02:29 GMT

NAJERIYA A YAU: Ladan Da Mai Aikin Ƙarfi Yake Samu A Lokacin Azumi

Published: 10th, March 2025 GMT

More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba

Watan azumi lokaci ne da akan samu wasu ma’aikatu sun sassauta wa ma’aikata ta hanyar yi musu rangwame kamar rage musu yawan sa’o’in aiki.

Sai dai a lokacin da waɗannan mutane suke samun rangwame, akwai waɗanda suke ayyuka ko sana’o’in da suka dogara da su ciyar da iyalansu.

Sau da dama irin waɗannan mutane sai sun fita sun yi aiki a rana, duk da suna azumi, suke samun abin da za su saka a bakin salati.

NAJERIYA A YAU: Falalar Buɗa-baki Cikin Iyali A Lokacin Azumi DAGA LARABA: Yadda Zawarawa Suke Ɗanɗana Kuɗa A Watan Ramadana

Shirin Najeriya a Yau na wannan lokaci zai yi duba ne kan irin ladan da masu aikin ƙarfi suke samu yayin da suke azumi.

Domin sauke shirin, latsa nan

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Aikin karfi Watan Azumi

এছাড়াও পড়ুন:

An kama ’yan bindiga 4 a Kano

An kama wasu mutum huɗu da ake zargin ’yan bindiga ne ɗauke da makamai da ake zaton bindigogi ne a tashar mota ta Ƙofar Ruwa da ke Jihar Kano.

Tashar motar, wadda ke kusa da kasuwar kayan gini ta Ƙofar Ruwa a Ƙaramar Hukumar Dala.

MAAUN: Ƙungiyar iyaye ta musanta zargin ƙara ƙudin yaye ɗalibai a jami’ar Sarkin Musulmi ya buƙaci gwamnonin Arewa suke saurarar ƙorafin jama’a

A cewar mazauna yankin, an kama mutanen ne lokacin da suke ƙoƙarin shiga mota domin tafiya zuwa wani waje a cikin Kano.

“Mutanen da ke tashar motar ne suka lura da makaman da suke ɗauke da su. Take suka gaggauta sanar da jami’an tsaro, waɗanda suka kama su. Su huɗu ne gaba ɗaya,” in ji Musa Balarabe, wani mazaunin yankin.

Ya ce an kama su ne da misalin ƙarfe 1 na rana.

Da farko an kai su ofishin ’yan sanda na Ƙofar Ruwa, kafin daga bisani aka mayar da su ofishin Dala.

Wani mazaunin yankin, Umar Nuhu, ya ce yana cikin shagonsa da ke Kwanar Taya, kusa da ofishin ’yan sandan, lokacin da aka kawo mutanen.

Ya ce hakan ya jawo firgici, inda mutane suka fara gudu a ko’ina.

Nuhu, ya ƙara da cewa mutane da yawa sun yi dandazo a ofishin ’yan sandan, yayin da wasu matasan ke son ɗaukar doka a hannu.

Da aka tuntuɓi kakakin ’yan sandan Kano, Abdullahi Haruna Kiyawa, bai ce komai kan lamarin ba.

Ya ce har yanzu suna tattara bayanai kafin su fitar da sanarwa.

Har zuwa lokacin haɗa wannan rahoto, babu wata sabuwar sanarwa daga rundunar ’yan sandan jihar.

Tashar Kofar Ruwa, tasha ce da ke jigilar fasinjoji zuwa jihohi irin su Katsina, Jigawa, Sakkwato, Zamfara, Kebbi, har ma da Jamhuriyar Nijar.

Wannan na zuwa ne daidai lokacin da Jihar Kano ke fama da hare-haren ’yan bindiga, musamman a yankunan da ke da iyaka da Jihar Katsina.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Rikicin Kungiyoyin Asiri Ya Yi Sanadiyyar Mutuwar Wani Matashi A Jihar Kwara
  • Har yanzu ban bar yin waqa ba-Yusuf Lazio
  • DAGA LARABA: Kalubalen Dake Gaban Janar Christopher Musa A Matsayin Ministan Tsaro
  • NAJERIYA A YAU: Matsalar Kansar Mama Da Hanyoyin Magance Shi
  • ’Yan ta’adda sun kashe ɗan sanda a gidan DPO a Jigawa
  • Najeriya: Matatar Man Fetur ta Dangote Za Ta Mika Tataccen Mai Lita Biliyan 1.5 A Watan Disamba
  • Tinubu ya gana da Janar Christopher Musa bayan Ministan Tsaro ya yi murabus
  • Tinubu ya gana da Janar Christopher CG Musa bayan Ministan Tsaro ya yi murabus
  • An kama ’yan bindiga 4 a Kano
  • NAJERIYA A YAU: Halayen Da Ambasadoji Ya Kamata Su Mallaka Kafin Tura Su Wasu Kasashe