NAJERIYA A YAU: Ladan Da Mai Aikin Ƙarfi Yake Samu A Lokacin Azumi
Published: 10th, March 2025 GMT
More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba
Watan azumi lokaci ne da akan samu wasu ma’aikatu sun sassauta wa ma’aikata ta hanyar yi musu rangwame kamar rage musu yawan sa’o’in aiki.
Sai dai a lokacin da waɗannan mutane suke samun rangwame, akwai waɗanda suke ayyuka ko sana’o’in da suka dogara da su ciyar da iyalansu.
Sau da dama irin waɗannan mutane sai sun fita sun yi aiki a rana, duk da suna azumi, suke samun abin da za su saka a bakin salati.
NAJERIYA A YAU: Falalar Buɗa-baki Cikin Iyali A Lokacin Azumi DAGA LARABA: Yadda Zawarawa Suke Ɗanɗana Kuɗa A Watan RamadanaShirin Najeriya a Yau na wannan lokaci zai yi duba ne kan irin ladan da masu aikin ƙarfi suke samu yayin da suke azumi.
Domin sauke shirin, latsa nan
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Aikin karfi Watan Azumi
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar da Wutar Lantarki a Yankunan Kananan Hukumomin Jihar
Daga Usman Muhammad Zaria
Gwamnatin Jihar Jigawa ta gudanar da bikin bude tayin bada kwangilar samar da wutar lantarki a wasu garuruwa dake kananan hukumomin Jihar.
A lokacin da yake jawabi a yayin gudanar da bikin daya gudana a sakatariyar Jihar dake Dutse, Shugaban hukumar, Injiniya Zubairu Musa ya bayyana cewar tayin bada kwangilar samar da wutar da gyara da fadadawa gami da kammala wasu ayyukan za a yi sune a garuruwa 17.
Kazalika, Injiniya Zubairu Musa, yace wannan na daga cikin kudirori 12 na Gwamna Umar Namadi na hada wutar lantarki a kanana da matsakaitan garuruwan jihar da basu da wuta.
A cewar sa, garuruwan da za’a samar da wutar lantarkin a Dutse sun hada da Sabuwar Takur da sabuwar hanyar rukunin gidajen gwamnati na Godiya Miyetti da rukunin gidaje na Bulori da kuma makaranta ta musamman ta Mega.
Shugaban hukumar wanda ya samu wakilcin Sakataren hukumar, Barrista Auwalu Yakubu, yace sauran su ne garin Wurno a karamar hukumar Birnin Kudu da samar da wutar lantarkin a sabbin rukunin gidajen gwamnati na Birnin Kudu da Dutse da Ringim da Babura tare da Kazaure da kuma Gumel.
Sai samar da wutar lantarkin a garin Tsamiyar kwance a karamar hukumar Babura da samar da wutar lantarki a hanyar Nguru da Biranen Hadejia da Kafin Hausa a kananan hukumomin Hadejia da Kafin Hausa.
Ya kara da cewar sai gyara wutar lantarki a garuruwan Addani da Ruruma da Ringim a karamar hukumar Yankwashi da kammala aikin samar da wutar lantarki a garuruwan Tage, Siga, Garin-Wakili, Fandum, Gauta, Ona, Baturiya da Barma-Guwa a karamar hukumar Kirikasamma.
Injiniya Zubairu yace sai kuma samar da wutar lantarki a garin Gwari a Miga da kuma garin Agura a karamar Kafin Hausa.
Sauran sun hada da kammala aikin samar da wutar lantarki a Dandidi a Gagarawa da Matsa a karamar hukumar Malam-Madori da kuma aikin fadada samar da wutar lantarki a Jami’ar Khadija dake garin Majia a karamar hukumar Taura.
A nasa jawabin, wakilin hukumar tantance ayyukan kwangila ta jihar Jigawa, ya ja hankalin ‘yan kwangilar da suka nuna sha’awarsu ta gudanar da aikin da su gudanar da aiki mai inganci, tare da bin dokoki da ka’idojin gudanar da ayyukan kwangila na hukumar.