Leadership News Hausa:
2025-09-24@17:19:04 GMT

Xi Jinping Ya Aika Da Sakon Taya Murna Ga Taron AU Karo Na 38

Published: 15th, February 2025 GMT

Xi Jinping Ya Aika Da Sakon Taya Murna Ga Taron AU Karo Na 38

A yau Asabar ne aka bude taron shugabannin kasashe da gwamnatocin AU a hedkwatar kungiyar dake birnin Addis Ababa na Habasha. (Mai fassara: Fa’iza Mustapha)

.

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Taron Canada: Haɗin Gwiwa Afirka Ke Buƙata Ba Agaji Ba – Gwamnan Zamfara 

Sanarwar ta ƙara da cewa, Gwamna Lawal ya jaddada cewa tsarin dimokuraɗiyyar Kanada, ƙarfafan tattalin arziƙi, hakar ma’adinai ta hanyar da ta dace, da kuma harkokin kasuwanci masu zaman kansu masu kirkire-kirkire sun sanya ta zama abokiyar haɗin guiwar da ta ta dace ga Afrika.

 

Ya ce, “Idan Afrika za ta cika burinta gaba ɗaya, dole ne mu gane cewa ci gaba ba wai kawai batun manufofin ƙasa bane; yana kuma buƙatar aikace-aikacen matakan jihohi da ƙananan hukumomi.

 

“Yayin da Gwamnatocin Tarayya ke ba da jagorar manufofi, a matakin Jihohi, larduna, da Ƙananan Hukumomi ake fassara alƙawuran kasuwanci, zuba jari da ci gaba zuwa ainihin gaskiya.

 

“Matakan jihohi sune inda manoma ke noma abincin da ke ciyar da ƙasashe, inda aikin haƙar ma’adinai ke yin nasara ko faɗuwa, inda matasa ke neman dama, da inda masu zuba jari ke bukatar tsari mai bayyana, kwanciyar hankali, da dawowa mai adalci. Wannan shi ya sa kasancewata a nan a matsayin Gwamnan Zamfara ba da gangan bane, illa da nufin ƙarfafawa. Yana nuna cewa tashin hankali na Afrika zai samo asali ne daga jihohi da larduna kamar yadda zai fito daga manyan birane.”

 

Gwamnan ya ƙara da cewa gwamnatinsa na canza tsarin mulki a Zamfara da yanayin saka jari don jawo hankalin abokan hulɗa masu gaskiya waɗanda ke da darajar gaskiya, rikon amana, da ci gaba mai ɗorewa.

 

“Noma shi ne ginshiƙin tattalin arziƙinmu. Fiye da kashi 70 na ƙasar mu tana da filin noma, Zamfara na iya zama amfanin gona ga Nijeriya da ma nahiyar Afrika. Muna neman haɗin kai a fannonin injina, ban ruwa, kula da amfanin gona bayan girbi, ajiya, da sarrafa kayan gona. Kwarewar Kanada, haɗe da jajircewar manomanmu, na iya samar da sabon tsarin tsaron abinci ga Afrika.

 

“Baya ga noma, Zamfara na da ma’adinai masu daraja kamar zinariya, lithium, manganese, da granite waɗanda suke da muhimmanci ga sauyin makamashi. Muna ƙoƙarin koyon darasi daga kurakurai na baya, domin tabbatar da cewa arzikin albarkatu ya fassaru zuwa ci gaba, ba wai fitarwa kawai ba. Muna ƙarfafa dokoki, inganta hakar ma’adinai na gaskiya, da tabbatar da amfanin al’umma.”

 

“Ina kira ga abokanmu na Kanada da su duba bayan manyan biranen Afrika zuwa yankuna, gonaki, makarantun, masana’antu, da al’ummomi, inda ainihin haɗin kai zai bunƙasa. Ku ƙarfafa shugabannin Afrika, ciki har da ni, wajen yin garambawul, ƙarfafa mulki, tsayawa kan gaskiya, da gina muhalli mai kyau ga haɗin kai.”

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Firaministan Sin Ya Isa New York Don Halartar Babban Taron Mahawara Na MDD Karo Na 80
  • Sauye-Sauyen Siriya A hannun Amurka Da Aika’ida
  • Xi Jinping Zai Halarci Bikin Murnar Cika Shekaru 70 Da Kafuwar Yankin Xinjiang Na Uygur Mai Cin Gashin Kansa
  • Taron Canada: Haɗin Gwiwa Afirka Ke Buƙata Ba Agaji Ba – Gwamnan Zamfara 
  • NEF za ta ƙaddamar da taron zuba jari don bunƙasa Arewa
  • Kasar Sin Za Ta Shirya Taron Mata Na Duniya A Beijing Yayin Cika Shekaru 30 Da Taron Mata Na 1995
  • Xi Jinping Ya Mika Gaisuwar “Bikin Girbi Na Manoman Kasar Sin” Na Takwas
  • Kashim Shettima Ya Isa New York Halartar Taron UNGA Na 80
  • Masana Sun Yaba Da Shawarar GGI Da Kasar Sin Ta Gabatar A Taron Kara Wa Juna Sani Na CMG 
  • Shettima ya tafi New York don halartar taron Majalisar Ɗinkin Duniya