Iran Ta Soki Kalaman Netanyahu Na Cewa A Kafa Falasdinu A Saudiyya
Published: 11th, February 2025 GMT
Iran, ta la’anci kalaman foraministan Isra’ila dake cewa a kasa kasar Falasdinu a cikin kasar Saudiyya.
Ministan harkokin wajen kasar Abbas Araghchi ya yi kakkausar suka ga kalaman na Benjamin Netanyahu da ke nuna cewa a kafa kasar Falasdinu a Saudiyya, yana mai danganta hakan da tsokana da kuma barazana ga zaman lafiya da tsaro a yankin.
Babban jami’in diflomasiyyar ya bayyana hakan ne yayin wata tattaunawa ta wayar tarho da takwaransa na Saudiyya Yarima Faisal bin Farhan a ranar Litinin yayin da ake ci gaba da cece-kuce kan shawarar Amurka da Isra’ila kan Falasdinu.
A yayin tattaunawar shi ma ministan harkokin wajen Saudiyya ya nuna adawar Saudiyya ta tilastawa Falasdinawa gudun hijira daga Gaza ko wasu yankunan.
Tunda farko dama kungiyar hadin kan kasashen musulmi ta OIC ta yi kakkausar suka kan munanan kalamai da kuma rashin da’a da firaministan Isra’ila ya yi na yin kira da a kafa kasar Falasdinu a kasar Saudiyya.
A ranar Alhamis, ne Netanyahu ya ba da shawara yayin wata hira da tashar 14 ta Isra’ila cewa “Saudiyya za ta iya kafa kasar Falasdinu a Saudiyya, suna da kasa mai girma.”
Kungiyar ta OIC ta dauki wannan a matsayin tsokana ga Saudiyya, kuma cin zarafi ne ga ’yancin kai, tsaron kasa da kuma yankinta, da kuma keta dokokin kasa da kasa da kundin tsarin mulkin Majalisar Dinkin Duniya.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: kasar Falasdinu a
এছাড়াও পড়ুন:
Xi Ya Yi Kiran Zurfafa Gyare-gyare Da Bude Kofa A Yayin Rangadin Aiki A Guangdong
Xi ya jaddada cewa, domin lardin Guangdong ya samar da sabbin damammaki da cimma sabbin nasarori, ya zama dole a ci gaba da himma wajen aiwatar da manufar yin gyare-gyare da bude kofa, da aiki da ruhin yankunan tattalin arziki na musamman, da kuma karfafa samun ci gaba mai inganci ta hanyar zurfafa gyare-gyare da bude kofa.
Ya yi kira da a yi kokarin zurfafa hadin gwiwa tsakanin Guangdong, Hong Kong da Macao, da kuma tallafa wa inganta hadewar Hong Kong da Macao da kuma hidimta wa ci gaban kasar baki daya. (Abdulrazaq Yahuza Jere)
ShareTweetSendShare MASU ALAKA