Kwamandan rundunar sojin saman Iran ya bayyana cewa: Sun kai ga nasarar cimma matakin cin gashin kai a kere-keren kayayyakin aikin soja

Kwamandan rundunar sojin saman Jamhuriyar Musulunci ta Iran Birgediya Janar Hamid Wahidi ya bayyana cewa: Sojojin saman Iran na ma’aikatar tsaro da taimakon sojojin kasar sun cimma mataki dari bisa dari a fagen gudanar da kere-keren kayayyakin da suke bukata a harkar tsaron kasa, kuma dukkanin kayan aikin wannan runduna an inganta su tare da mayar da su saffarin cikin gida.

A ranar Juma’a 7 ga watan Fabrairu, Birgediya Janar Wahidi ya sanar a gaban taron kwamandojin sojojin saman Jamhuriyar Musulunci ta Iran da Jagoran juyin juya halin Musulunci a wata hira da aka yi da shi ta gidan talabijin cewa: Sojojin sama da na tsaron sararin samaniya su ne manyan makamai biyu na sojojin kasar Iran, kuma duk da takunkumin da aka kakaba musu, sun samu nasarar kare kasar tsawon shekaru takwas a tsawon kare kai daga yakin wuce gona da iri da aka kaddamar kanta a farkon samun nasarar juyin juya halin Musulunci.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Iran Ta Ce Babu Wani Da Zai Kusanci Cibiyoyin Tashe Makamashin Uranim Na Kasar

Iran ba zata taba amincewa wata hukuma ko wata kungiyar kasa da kasa ta kusanci cibiyoyin makamashin nukliya na kasar Iran ba.

Kamfanin dillancin labaran Tasnim na kasar Iran ya nakalto shugaban kwamitin tsaron kasa da kuma al-amuran harkokin waje a majalisar dokokin kasar Iran yana fadar haka a ranar Litinin da ta gabata. Ya kuma musanta zancen da wasu suke yadawa na cewa masu sanya ido a ayyukan makamashin nukliya daga hukumar IAEA sun dawo suna ayyukansu a fordo, Natanz da kuma Esfahan.

Ebrahim Azizi shugaban kwamitin ya kara da cewa an  tsara cewa wata tawaga daga hukumar IAEA zata kawo ziyarar aiki nan Tehran don tattaunawa da jami’an gwamnatin kasar kan abubuwan da suka shafi sayasar hukumar IAEA da kuma ayyukan kanikancin tashe makamashin uranium.

Majalisar dokokin kasar Iran dai ta samar da doka, wacce ta bayyana cewa, da ko wani dalili, ba’a amincewa wani daga waje ya kusance yakayin tashe makamashin Uranium na kasar ba.

Dokar tace ko masu bincike daga hukamar IAEA ko kuma jami’an wata kungiya daga waje, basu da hurumin kusantar wadannan cibiyoyin tashe makamashin Uranium.

Azizi yace daga yanzu hulda da hukumar makamashin nukliya na kasar Iran da kuma IAEA zai takaita ne kan al-amuran sam-sama na shirin nukliyar kasar Iran wanda bai bukatar wani ya je cibiyoyin,

Kafin haka isma’ila bakae kakakin ma;aikatar harkokin wajen kasar Iran ya bayyana cewa tawagar ta IAEA zata isa nan Tehran nan da kasa da kwanaki 10.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka IRGC: Bayan yakin Kwanaki 12 Yanayi Ya Sauya Zuwa Ga Amfani Ga Iran August 6, 2025 ‘Yansanda A Iran Suna Amfani Da Kayakin Tsaro Na Zamani A Lokacin 40 August 6, 2025 Iran tana Goyon Bayan Zaman Lafiya Tsakanun Kasashen Yankin August 6, 2025 Iran: Yakin Kwanaki 12 Ya Bayyana Inganci Da Karfin Yakin Yanar Gizo Na Kasar August 6, 2025 Iran: An nada Larijani a matsayin sakataren kwamitin koli na tsaron kasa August 6, 2025 Sheikh Qassem: Tsaron Isra’ila zai rushe cikin sa’a 1 idan ta shelanta yaki a kan Lebanon   August 6, 2025 Kwamitin Sulhu na MDD ya yi zaman gaggawa kan batun Gaza August 6, 2025 Kamaru: An haramta wa babban dan hamayya tsayawa takara a zaben Oktoba August 6, 2025 Yunkurin Netanyahu na mamaye Gaza ya tayar da balli a Haramtacciyar Kasar Isra’ila August 6, 2025 Araqch: Hadin Kai Tsakanin Cibiyoyi  Na Tabbatar Da Karfi Da Ci Gaba August 5, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sojoji sun yi wa ’yan ta’adda ɓarin wuta a Borno
  • Tallafin Kammala Makarantun Share Fagen Shiga Firamare Na Gwamnatin Kasar Sin Zai Amfani Mutane Kimanin Miliyan 12
  • Abba ya yi alhinin hadiminsa da ’yan daba suka kashe a Kano
  • NAHCON ta ƙayyade N8.5m kafin alƙalami na kujerar Hajjin 2026
  • Dakarun Kare Juyin Juya Halin Musulunci Na Iran Sun Jaddada Shirinsu Na Tunkarar Duk Wata Barazana
  • Matasan Kauru Sun zargin Dan Majalisar Dokoki Barnabas Danmaigona da Rashin tabuka komai
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Taya Ali Larijani Murnar Nada Shi Sakataren Majalisar Kolin Tsaron Kasar Iran
  • Tinubu Ya Taya Nafisa, Rukayya, Hadiza Murnar Samun Nasarar Zama Gwanaye A Gasar Turanci Ta Duniya
  • Iran Ta Ce Babu Wani Da Zai Kusanci Cibiyoyin Tashe Makamashin Uranim Na Kasar
  • Iran: An nada Larijani a matsayin sakataren kwamitin koli na tsaron kasa