Hare-hare: ’Yan bindiga sun raba mutum 5,000 da muhallansu a Katsina
Published: 31st, July 2025 GMT
Sama da mutum 5,000 ne suka tsere daga gidajensu a Jihar Katsina, sakamakon sabbin hare-haren da ’yan bindiga suka kai a Ƙananan Hukumomin Bakori da Faskari.
Mutane daga ƙauyuka sama da 10 sun nemi mafaka a garin Bakori, inda da dama ke zaune wajen ’yan uwansu, yayin da wasu ke kwana a waje ba tare da masauki ko abinci ba.
Wasu daga cikin waɗanda abin ya shafa sun bayyana cewa, maharan sukan shiga ƙauyuka da yawa, inda suka dinga harbi, ƙone gidaje, sannan suka sace mutane ciki har da mata da ƙananan yara.
Hare-haren sun fi muni a auyuka irin su Guga, Anguwar Danmarka, Gidan Sule, da sauransu.
Wani dattijo mai shekara’u 68 daga ƙauyen Doma ya ce sama da mutum 250 aka kashe a yankinsa cikin shekaru biyar da suka wuce.
Ya ƙara da cewa ’yan bindigar sukan ƙone rumbunan abinci tare da sace dabbobi.
Wata mata da ta kuɓuta daga harin a Anguwar Galadima ta ce iyalinta su 17 sun tsere, inda ta ce an sace sama da mutum 20 a ƙauyen nasu.
Wani saurayi daga Anguwar Dan Marka ya bayyana yadda aka harbe shi sau biyu a ƙafa, kuma yanzu yana amfani da sanda wajen yin tafiya.
Wasu da dama har yanzu suna hannun maharan, yayin da suke neman fansar Naira miliyan 1.5 kan kowane mutum ɗaya.
Manoma ma na kuka da halin da suka tsinci kansu sakamakon hare-haren.
A wani faifan bidiyo da ya karaɗe kafafen sada zumunta, wani manomi daga Ƙaramar Hukumar Sabuwa ya koka da yadda aka lalata gonarsa.
Amma a martanin da suka bayar, shugabannin Ƙaramar Hukumar sun ce an lalata gonakin da ke kusa da manyan tituna ne domin hana ’yan bindiga amfani da su wajen ɓuya da kuma kai wa matafiya hari.
Amma manoman suna kallon wannan a matsayin wata matsala a gare su.
Shugabannin ƙauyuka da hukumomin gwamnati sun tabbatar da cewa mutane suna ƙara zuwa Bakori kowace rana don neman mafaka.
Shugaban Ƙaramar Hukumar Bakori, ya ce akwai sama da mutum 3,500 da ke zaune a Bakori, yayin da wasu sama da 2,000 ke zaune a ƙauyen Guga.
An fara raba wa waɗanda suka rasa matsugunansu abinci da kayan masarufi, amma ana buƙatar samum ƙarin taimako.
Ƙungiya ta buƙaci a ayyana dokar ta-ɓaci a BakoriAn buƙaci Gwamnatin Tarayya da ta jiha da kuma ƙungiyoyin agaji su kai wa waɗanda lamarin ya shafa ɗauki cikin gaggawa.
Wata ƙungiya mai zaman kanta mai suna ‘Grassroots Advocates for Peace’ ta nemi Gwamnatin Tarayya ta ayyana Bakori a matsayin yanki mai hatsari.
Sun buƙaci ƙarin jami’an tsaro, da ɗaukar mataki cikin gaggawa.
Sun kuma buƙaci a kula da lafiyar kwakwalwar waɗanda suka kuɓuta daga hare-haren da kuma hukunta masu kai hare-haren.
Gwamnatin Katsina na ƙoƙarin magance matsalarA nata ɓangaren, Gwamnatin Jihar Katsina, ta ce tana ƙoƙarin wajen magance matsalar.
Kwamishinan Tsaron Cikin Gida na Jihar, Nasir Muazu, ya ce suna ƙoƙarin magance matsalolin da Ƙaramar Hukumar ke fama da su.
Ya ce akwai wasu mutane da ke ƙoƙarin yada ƙarya a kafafen sada zumunta don haifar da tsoro da ruɗani a zukatan jama’a.
Ya kuma ce an samu sauƙin kai hare-hare a wasu yankuna kamar Jibia da Batsari.
Kwamishinan, ya bayyana cewa an kafa rundunar ‘Katsina Community Watch Corps’ domin taimaka wa sojoji, ’yan sanda da ’yan sa-kai wajen shiga dazuka da ke da wuyar shiga.
Sai dai ya buƙaci jama’a da su ci gaba da jajircewa da kuma bayar da rahoton duk wani abu da su yarda da shi ba.
An samu sauƙin kai hare-hare cikin shekara 2 — RibaduA yayin da gwamnati ke cewa ana samun ci gaba, Mai Bai Wa Shugaban Ƙasa Shawara Kan Harkar Tsaro, Nuhu Ribadu, ya ce Najeriya ta fi samun zaman lafiya a yanzu sama da shekaru biyu da suka wuce.
Ya ce an ceto da mutum sama da 11,000 da aka sace, kuma an kashe wasu daga cikin manyan shugabannin ’yan bindiga.
Ya yaba wa Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu, bisa jagoranci da tsare-tsaren tsaro da suka haifar da wannan sauyi.
Sai dai waɗanda ke zaune a matsuguni na wucin gadi a Bakori da wasu yankuna, rayuwa cikin tsaka mai wuya.
Wasu sun ce har yanzu ba su da ƙwarin gwiwar komawa gidajensu.
Sun tabbatar da cewar sai gwamnati ta samar da tsaro mai ɗorewa, sannan za su koma muhallansu, saɓanin haka za su ci gaba da zama a inda suke a yanzu.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Bindiga Batsari Ɗauki Gwamnatin Katsina Gwamnatin tarayya hare hare Tsaro Ƙaramar Hukumar yan bindiga
এছাড়াও পড়ুন:
Dalilin Gwamnatin Jihar Kuros Riba Na Raba Wa Manoma Taraktoci
Taron kaddamar da rabar da taraktocin noman, ya gudana ne a Shalkwatar Ma’aikatar Kula da Aikin noma da kuma yin Noman Rani da ke garin Kalaba.
Kazalika, taron ya samu halartar ‘yan Majalisa da Sarakunan Gargajiya da kungiyoyin manoma mata da masu ruwa da tsaki a fannin aikin noma da ke jihar da abokan hadaka.
Daukacinsu, sun jinjina wa wannan kokari na gwamna Bassey, kan wannan hangen nesa da gwamnatinsa ta yi, na kaddamar da taraktocin noman, musamman domin ciyar da fannin aikin noman jihar gaba, duba da cewa; fannin ne kinshikin tattalin arzikin jihar.
Har ila yau, gwamna Bassey, ya nanata kudurin gwamnatinsa wajen ci gaba da bai wa fannin aikin noma muhimmanci a matsayin fannin da ke kara habaka tattalin arzikin jihar.
“A lokacin da na karbi jan ragamar shugabancin jihar, mun samar da dabaru da kuma daukar matakai daban-daban, domin kara habaka fannin,“ in ji gwamna Bassey.
“Biyo bayan wata ganawa da muka yi da manoman da ke daukacin kananan hukumominmu, mun gano cewa; kalubalen da suke fuskanta sama da kashi 70 cikin dari, na shiye-shiyen share gonakansu ne, domin fara noma su; saboda kudaden da suke kashewa masu yawa, wajen gyaran gonakin nasu, muna da yakinin wannan shirin zai magance wadannan matsaloi,” a cewar gwamnan.
Kazalika, gwamnan ya bayyana cewa; wannan rabar da taraktocin noma, wadanda ba sa shan man sosai, an tsara su ne kan yadda manoma za su yi gyaran gonakinsu cikin sauki tare kuma da rage musu kashe kudade masu yawa da kuma kara habaka fannin na aikin noma.
“Kashi 108 na kashin farko na shirin, an raba wa manoman jihar jimillar taraktocin noma 324, wadanda kuma aka rabar da su a daukacin fadin jihar,“ a cewar gwamnan.
Gwamna Bassey ya ci gaba da cewa, za a ci gaba da kula da taraktocin ne a karkashin tsarin kungiyoyin manoma na jihar.
“Hakan zai bai wa wadanda suka amfana da taraktocin damar daukar nauyin ci gaba da kula da su, wanda kuma sauran manoman da ke karkara a jihar, su ma za su samu damar samun taraktocin,” in ji shi.
“Ta wannan hanyar, za mu samu damar cin gajiyar da ke fannin noma na jihar, wanda hakan zai kuma bai wa manoman jihar kara dagewa, domin yin noma da samun kudaden shiga da kuma kara samar da wadataccen abinci a jihar,” a cewar tasa.
Kazalika, gwamnan ya kuma zayyano wasu ayyukan noma da gwamnatinsa ta kaddamar da su da suka hada da na samar da Irin noman Rogo, aikin noman Masara da na Waken Soya da sauransu.
Ya bayyana cewa, gwamnatin na kuma ci gaba da habaka samar da Irin Farin Wake da rabar da kayan aikin noma ga kananan manoma tare da kuma shirye-shiyen noman Koko (Cocoa) da Ganyen Shayi, wanda za gudanar ta hanyar yin hadaka da gwamnatin da kuma ‘yan kasuwa.
“Kaddamar da rabar da wadannan taraktocin noman, na daya daga cikin kason farko na kudurin gwamnatinmu na bunkasa fannin aikin noma na jihar, musamman ta hanyar yin amfani da kayan aikin noma na zamani,” in ji gwamnan.
Shi ma, shugaban kamfanin da ya yi kwangilar kawo taraktocin, Femi Odeshirin, ya yaba wa shirin, wanda ya ce; hakan zai kara bunkasa fannin aikin noma na jihar.
“Ba wai kawai rabar da wadannan taraktocin noma ga manoman jihar ba ne da gwamnan ya yi ba, hakan zai kuma kara inganta rayuwar manoman da suka amfana,” in ji Odeleye.
Ya bayyana cewa, kamfanin na kuma kan shirin kafa masana’antar da ake hada taraktocin noma a garin Kalaba da ke jihar, inda masana’antar za ta samar da ayyukan yi sama da 2,000.
Shi kuwa, shugaban kungiyar manoma ta kasa (AFAN) reshen jihar, Ojikpong Nyiam Bisong, danganta salon shugabancin gwamna Bassey ya yi da na marigayi tsohon Firimiyan Kudancin Nijeriya, Dakta Michael Okpara.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA