Aminiya:
2025-11-28@13:10:35 GMT

Kamfanonin rarraba lantarki sun tafka asarar biliyan 358 a cikin wata uku – NERC

Published: 8th, October 2025 GMT

Hukumar da ke Kula da Wutar Lantarki ta Najeriya (NERC) ta ce kamfanonin rarraba wutar lantarki guda 11 sun tara Naira biliyan 546.71 daga hannun abokan cinikinsu a cikin zango na biyu na shekarar 2025.

Sai dai hukumar ta ce wannan adadi bai kai kaso 60 cikin 100 na wutar da aka tura musu daga babbar hanyar rarraba wuta ba, sakamakon matsalolin lissafin wutar da suka karɓa da kuma yadda aka raba wutar ga rukunan abokan ciniki daban-daban.

Zulum ya ba ma’aikaciyar lafiya ’yar kabilar Igbo kyautar gida, ya ba danta aiki Matar aure mai ’ya’ya huɗu ta rataye kanta a Jigawa

Hakan, a cewar hukumar, ya haifar da gibin biyan kuɗi na naira biliyan 167.25.

kazalika, NERC ta ce abokan ciniki sun gaza biyan naira biliyan 190.64 na kuɗin wutar da aka lissafa musu, wanda hakan ya sa kamfanonin suka yi asarar naira biliyan 357.89 sakamakon rashin biyan kuɗin wutar.

A cikin rahoton zango na biyu na shekarar 2025, NERC ta ce jimillar wutar da dukkan kamfanonin suka samu a zangon na biyu ta kai ta naira biliyan 909.59, yayin da jimillar wutar da aka lissafa ta kai naira biliyan 742.34.

Rahoton ya ƙara da cewa a cikin kamfanonin, na Eko ne ta yi kowa wajen lissafin kuɗin wutar da kaso 96.67 cikin 100, yayin da na Yola ne ya fi kowanne yin ƙasa da kaso 58.38 cikin 100.

Kamfanonin sun fi ba ’yan kasuwa wutar lantarki

Rahoton ya kuma nuna cewa kamfanonin rarraba lantarkin sun fi karkata wajen baiwa abokan ciniki na kasuwanci wuta a cikin zangon, inda suka fi tura wuta zuwa waɗannan rukunan fiye da masu amfani da ita a gidajensu.

Sai dai rahoton ya ce kamfanin na shiyyar Fatakwal ne kaɗai ya rarraba wutar daidai da yadda hukumar ta amince a lokacin.

Rahoton ya ce kamfanin shiyyar Eko da na Kano sun fi tura wuta zuwa layukan da ke da tsarin kasuwanci, wanda hakan na iya haifar da samun ƙarin ingancin amfani da wuta a waɗannan layukan, yayin da na Benin, Kaduna da Ibadan suka fi tura wuta zuwa layukan da ba su da riba sosai.

Gwamnatin tarayya ta bashin tallafi na Naira biliyan 514.35

Rahoton ya bayyana cewa gwamnatin tarayya ta ɗauki nauyin biyan bashin tallafi na Naira biliyan 514.35 da kamfanonin samar da wutar lantarki ke bin ta.

“Abin lura shi ne, saboda rashin farashin da ya dace da ƙimar kuɗin samar da wuta a dukkan DisCos, gwamnati ta ɗauki nauyin tallafi na naira biliyan 514.35. Wannan ya nuna raguwar tallafin da gwamnati ke bayarwa da naira biliyan 22.04 (raguwa da kaso 4.11 cikin 100) idan aka kwatanta da zangon farko na 2025 (N536.40bn).”

Duk da cewa adadin tallafin ya ragu a Naira, ya kai kaso 59.60 cikin 100 na jimillar kuɗin da kamfanonin ke bukata, wanda ya fi zangon farko na 2025 da kashi 0.44 cikin 100, inda tallafin ya kai kaso 59.16 cikin 100.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Wutar lantaki na Naira biliyan na naira biliyan wutar lantarki

এছাড়াও পড়ুন:

Reuters: Kungiyar Likitoci Ba Da Iyaka Ba Ta Fice Daga Asibitin Darfur Bayan Bude Wa Ma’aikatanta Wuta

Kungiyar ta kasa da kasa mai gudanar da a ayyukan agaji, ta sanar da janye ma’aikatanta daga asibitin Darfur, bayan da aka bude musu wuta, ya kuma kai ga kashe daya daga cikin masu aikin agaji.

Kungiyar ta yi kira ga rundunar kai daukin gaggawa RSF da ta tabbatar da tsaro da kuma kiyaye lafiyar ma’aikatan agaji.

Bugu da kari kungiyar ta ce mutumin da aka kashe  a ranar 18 ga watan nan na Nuwamba ma’aikaci ne a ma’aikatar kiwon lafiya ta Sudan.

Asibitin Zalnagi yana a jihar Darfur ta tsakiya ne da a halin yanzu ke karkashin ikon  rundunar “RSF.

A nata gefen, jami’a mai kula da tafiyar da ayyukan kungiyar ta “ Likitoci Ba Tare Da Iyaka Ba.”  Maryam Li Arusi ta ce, babu yadda za a yi ma’aikatansu su ci gaba da gudanar da ayyukansu na jin kai a halin da ake ciki, har sai idan RSF ta bayar da tabbaci da lamunin bayar da kariya ga ma’aikatan da kuma marasa lafiya.

A daya gefen,rundunar RSF ta kore cewa tana cutar da fararen hula, tana mai jaddada cewa duk wanda aka same shi da aikata laifi to za a hukunta shi.

Tun bayan da yankin Darfur ya shiga karkashin ikon rundunar RSF ne ake fito da bayanai akan yadda mayakanta su ka aikata laifukan yaki da cin zarafin mutanen yankin.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Shugaban Iran: Kasuwar jarin cikin gida sirrin nasarorin gwamnati na tattalin arziki November 26, 2025 Larijani: Hadin gwiwar Iran da Pakistan na taimaka wa zaman lafiya a yankin November 26, 2025 Al-Houthi ya yi ta’aziyyar shahadar babban kwamanda na Hizbullah November 26, 2025 UNIFIL: Isra’ila tana sabawa wa kudurorin MDD a cikin  Lebanon November 26, 2025 Matsalolin Tsaro A Yankunan Bakin Ruwa A Kasar Siriya Ya Kai Ga Zanga-Zangar Lumana November 26, 2025 Aljeriya Ta Bukaci Kasashen Duniya Su Dauki Mataki Don Kawo Karshen Ta’asan HKI A Yankin Asiya Ta Kudu November 26, 2025 Shugaban Majalisar Koli Ta Taron Kasa Iran Ya Yabawa Pakistan Saboda Goyon Bayanta November 26, 2025 EU da AU na taro kan diyya ga laifukan mulkin mallaka da cinikin bayi November 25, 2025 Hizbullah: Isra’ila na kure idan ta na tunanin kashe-kashe zai kawo karshen kungiyarmu November 25, 2025 Tashar Press TV ta kaddamar da sashen harshen Hebrew November 25, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Wata mata ta kashe ’yar shekara 7 a Ribas
  • Gwamnati Za Ta Biya Wasu Kudaden Ariyas Ga Masu Fensho Wannan Wata
  • Karamar Hukumar Birnin Kudu Ta Kashe Sama da Naira Miliyan 5 Don Tallafawa Shirin AGILE
  • HKI Tana Amfani Da Tsagaita Wuta A Gaza Don Sake Shata Kan Iyakokin Yankin
  • Yawan Falasdinawa Da Suka Yi Shahada Na Karuwa Saboka Keta Yarjeniyar Tsagaita Wuta
  • Iraki: An Dakatar Da Tura Iskar Gas Zuwa Injunan Bada Wutan Lantarki A Yankin Kurdistan
  • Juyin mulki ya rutsa da Jonathan a Guinea-Bissau
  • Tukur Mamu ya karbi N50m daga kuɗin fansar harin jirgin kasan Kaduna – DSS
  • Reuters: Kungiyar Likitoci Ba Da Iyaka Ba Ta Fice Daga Asibitin Darfur Bayan Bude Wa Ma’aikatanta Wuta
  • Gwamna Namadi Ya Gabatar da Kasafin Naira Biliyan 900 ga Majalisa