Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?
Published: 8th, October 2025 GMT
Wannan sanarwar ta baya bayan nan da kasar Sin ta yi, ya samu yabo sosai, musammam daga sakatare janar na MDD, yana jaddada cewa, shirin na Sin na da muhimmanci matuka ga tunkarar sauyin yanayi. Su ma kafafen yada labarai na kasa da kasa da manyan jami’an hukumomi da kasashe da dama, sun yaba wa shirin, wanda ya nuna cewa, ana kara ammana da irin rawar da kasar Sin ke takawa a harkokin da suka shafi duniya.
Ba alkawari da gabatar da shirin kadai take yi ba, ta kasance mai aiwatar da su a aikace kuma ana ganin nasarorin da take samu a zahiri. Zuwa yanzu, babu wata kasa da ta bayar da gudunmuwa a wannan bangare kamar kasar Sin, kuma abun takaici shi ne, maimakon a dauki haka a matsayin zaburarwa, wasu na gujewa sauke nauyin da ya rataya a wuyansu. Zuwa yanzu, kasar Sin ta zama jagora a fannin kirkirowa da amfani da makamashi mai tsafta. Ta kasance kasa mafi samar da kayayyakin sola a duniya, inda karfinta a bangaren ya zarce na duk duniya baki daya. Haka ma idan aka tabo karfin samar da lantarki daga iska da ruwa. Bugu da kari, tana kara cimma burinta na rage fitar da hayakin Carbon, inda daga 2005 zuwa 2020, yawan hayakin da take fitarwa ya ragu da kaso 48, kana tattalin arzikinta na habaka cikin sauri fiye da yawan hayakin da take fitarwa.
Kudurinta a wannan bangare ne ya sa take kai wa ga cika alkawuranta kafin ma lokacin da ta ayyana, wanda ke nuna da gaske take kuma ta amsa sunanta na babbar kasa mai sauke nauyi da ganin an samu duniya mai kyakkyawan muhallin rayuwa ga daukacin bil adama. (Fa’iza Mustapha)
ShareTweetSendShareMASU ALAKA
এছাড়াও পড়ুন:
CMG Ya Kaddamar Da Shirin “Dabarun Tallata Kayayyakin Sin” A Tafarkin Gina Kasa Bisa Hadin Gwiwa
A yau Jumma’a 10 ga watan Oktoba, an kaddamar da wani shiri na aikin hadin gwiwa mai lakabin “Dabarun Tallata Kayayyakin Sin” na rukunin gidajen rediyo da talabijin na kasar Sin (CMG) na shekarar 2026 a birnin Beijing.
Shen Haixiong, babban darektan CMG, ya gabatar da jawabi a wajen taron, inda ya bayyana cewa, CMG ya samu damar zamowa kan gaba a fagen yada labarai na kasa da kasa bisa kayayyakin aiki da ma’aikata, kuma shi ne muhimmin dandali na tallata kayayyakin kasar Sin. Kamfanin a shirye yake ya dauki shirin a matsayin wata damar yin aiki kafada da kafada da abokan kawance daga kowane bangare na rayuwa, tare da rubuta sabon babi a fagen gina kasa mai kunshe da kayayyakin kamfanonin da suka kasance a kan gaba. (Mai fassara: Abdulrazaq Yahuza Jere)
ShareTweetSendShare MASU ALAKA