Leadership News Hausa:
2025-10-13@14:53:55 GMT

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

Published: 8th, October 2025 GMT

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

 

Wannan sanarwar ta baya bayan nan da kasar Sin ta yi, ya samu yabo sosai, musammam daga sakatare janar na MDD, yana jaddada cewa, shirin na Sin na da muhimmanci matuka ga tunkarar sauyin yanayi. Su ma kafafen yada labarai na kasa da kasa da manyan jami’an hukumomi da kasashe da dama, sun yaba wa shirin, wanda ya nuna cewa, ana kara ammana da irin rawar da kasar Sin ke takawa a harkokin da suka shafi duniya.

 

Ba alkawari da gabatar da shirin kadai take yi ba, ta kasance mai aiwatar da su a aikace kuma ana ganin nasarorin da take samu a zahiri. Zuwa yanzu, babu wata kasa da ta bayar da gudunmuwa a wannan bangare kamar kasar Sin, kuma abun takaici shi ne, maimakon a dauki haka a matsayin zaburarwa, wasu na gujewa sauke nauyin da ya rataya a wuyansu. Zuwa yanzu, kasar Sin ta zama jagora a fannin kirkirowa da amfani da makamashi mai tsafta. Ta kasance kasa mafi samar da kayayyakin sola a duniya, inda karfinta a bangaren ya zarce na duk duniya baki daya. Haka ma idan aka tabo karfin samar da lantarki daga iska da ruwa. Bugu da kari, tana kara cimma burinta na rage fitar da hayakin Carbon, inda daga 2005 zuwa 2020, yawan hayakin da take fitarwa ya ragu da kaso 48, kana tattalin arzikinta na habaka cikin sauri fiye da yawan hayakin da take fitarwa.

 

Kudurinta a wannan bangare ne ya sa take kai wa ga cika alkawuranta kafin ma lokacin da ta ayyana, wanda ke nuna da gaske take kuma ta amsa sunanta na babbar kasa mai sauke nauyi da ganin an samu duniya mai kyakkyawan muhallin rayuwa ga daukacin bil adama. (Fa’iza Mustapha)

 

ShareTweetSendShareMASU ALAKA Daga Birnin SinDaukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu October 7, 2025Daga Birnin SinFiraministan Sin Zai Halarci Bikin Cika Shekaru 80 Na Kafuwar Jam’iyyar WPK Ta Korea Ta Arewa October 7, 2025Daga Birnin SinHabakar Yin Sayayya A Lokacin Hutu Ta Nuna Kirkira Da Irin Ci Gaban Da Tattalin Arzikin Kasar Sin Ke Samu    October 6, 2025

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

CMG Ya Kaddamar Da Shirin “Dabarun Tallata Kayayyakin Sin” A Tafarkin Gina Kasa Bisa Hadin Gwiwa

A yau Jumma’a 10 ga watan Oktoba, an kaddamar da wani shiri na aikin hadin gwiwa mai lakabin “Dabarun Tallata Kayayyakin Sin” na rukunin gidajen rediyo da talabijin na kasar Sin (CMG) na shekarar 2026 a birnin Beijing.

 

Shen Haixiong, babban darektan CMG, ya gabatar da jawabi a wajen taron, inda ya bayyana cewa, CMG ya samu damar zamowa kan gaba a fagen yada labarai na kasa da kasa bisa kayayyakin aiki da ma’aikata, kuma shi ne muhimmin dandali na tallata kayayyakin kasar Sin. Kamfanin a shirye yake ya dauki shirin a matsayin wata damar yin aiki kafada da kafada da abokan kawance daga kowane bangare na rayuwa, tare da rubuta sabon babi a fagen gina kasa mai kunshe da kayayyakin kamfanonin da suka kasance a kan gaba. (Mai fassara: Abdulrazaq Yahuza Jere)

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin Sin Za Ta Fara Cajin Kudi Na Musamman Ga Jiragen Ruwan Amurka October 10, 2025 Daga Birnin Sin Kasar Sin Ta Samu Manyan Nasarori A Fannin Inganta Walwalar Yara Da Tsoffi Cikin Shekaru 5 Da Suka Gabata   October 10, 2025 Daga Birnin Sin Sin Ta Gabatar Da Shawarwari Shida Game Da Karfafa Tsarin Shari’a Da Inganta Shugabanci A Duniya October 10, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Da Shawarwari Hudu A Taron Kolin Mata Na Duniya
  • Kasar Sin Ta Kare Matakinta Na Takaita Fitar Da Ma’adanan Farin Karfe Na Rare Earth
  • Zuwa Kofin Duniya: Za A Yi Ta Ta Kare A Nahiyar Afirka
  • Rashin Amincewa Da Kasashen Yamma Yana Haifar Da Sabon Tunani Kan Huldar Kasa Da Kasa
  • Egbetokun ya sauke kwamishinan ’yan sandan Abuja
  • An Yi Girgizar Kasa Mai Daraja 5 A Ma’aunin Richter  A Kasar Habasha
  • Ranar Malamai Ta Duniya: Rashin Kulawa Ke Sa Malamai Barin Aiki
  • CMG Ya Kaddamar Da Shirin “Dabarun Tallata Kayayyakin Sin” A Tafarkin Gina Kasa Bisa Hadin Gwiwa
  • Kasar Sin Ta Samu Manyan Nasarori A Fannin Inganta Walwalar Yara Da Tsoffi Cikin Shekaru 5 Da Suka Gabata  
  • Sin Ta Gabatar Da Shawarwari Shida Game Da Karfafa Tsarin Shari’a Da Inganta Shugabanci A Duniya