Ɗaliban Kano za su koma makaranta ranar Lahadi da Litinin – Gwamnati
Published: 5th, April 2025 GMT
Gwamnatin Jihar Kano, ta bayyana cewa ɗaliban makarantun kwana na gwamnati da na masu zaman kansu za su koma makaranta a ranar Lahadi 6 ga watan Afrilu, 2025.
Wannan ya shafi makarantun firamare da sakandare domin ci gaba da zangon karatu na uku na shekarar 2024 zuwa 2025.
Boko Haram haram ta kashe ɗan sanda a sabon hari a Borno An haramta wa Akpabio da Natasha tattaunawa da manema labaraiGa ɗaliban makarantun jeka ka dawo kuwa, za su koma makaranta a ranar Litinin 7 ga wata.
Sanarwar da Daraktan Wayar da Kai na Ma’aikatar Ilimi ta Jihar Kano, Balarabe Abdullahi Kiru, ya fitar, ta buƙaci iyaye da su kula da wannan rana domin tabbatar da cewa yara sun koma makaranta a kan lokaci.
Kwamishinan Ilimi na Jihar Kano, Dokta Ali Haruna Makoda, ya gargadi ɗalibai da su guji kawo miyagun abubuwa kamar wuƙa, reza ko ƙwayoyi zuwa makaranta.
Ya kuma ce gwamnati za ta ɗauki mataki a kan duk ɗalibin da ya ƙi bin wannan doka.
Ya ƙara da cewa bin doka da ƙa’ida na taimaka wa ɗalibai su samu nasara a karatunsu.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Ɗalibai gwamnati Komawa Makaranta Ma aikatar ilimi koma makaranta
এছাড়াও পড়ুন:
Majalisar Dokokin Jihar Jigawa Na Da Kwamitoci 30 Da Ke Sa Ido Kan Ma’aikatun Gwamnati
Majalisar Dokokin Jihar Jigawa ta ce akwai kwamitoci guda 30 da aka daurawa nauyin bibiyar yadda ma’aikatu da hukumomin gwamnatin Jihar ke sarrafa kudade domin gudanar da harkokin yau da kullum, gami da ayyukan raya kasa.
Shugaban Kwamatin kananan hukumomi na majalisar dokokin jihar, Alhaji Aminu Zakari, ya bayyana hakan lokacin wata ziyarar aiki a karamar hukumar Babura.
Yayi bayanin cewar, an dorawa Kwamatinsa alhakin duba kananan hukumomi domin tabbatar da shugabanci nagari a yankunan karkara.
A cewarsa, kwamatin yana duba kundin bayanan sha’anin mulki da na harkokin kudi da suka hada da jadawalin kudaden da karamar hukuma ke samu daga kason arzikin kasa, da littafin hulda da banki,da takardun biyan kudade na voucher da kundin bayanan tarukan kwamitocin karamar hukuma domin tabbatar da ritita kudaden gwamnati.
Alhaji Aminu Zakari ya kuma lura cewar, ziyarar tana bada damar ganawa tsakanin ‘yan kwamatin da masu ruwa da tsaki na kananan hukumomi domin tattaunawa da su, da nufin samar da kyakkyawan yanayin aiki tare tsakanin bangarori daban daban.
Karamin Kwamatin da wakilin mazabar Guri Alhaji Usman Abdullahi Tura Musari ya jagoranta, ya duba aikin noman shinkafa a fadamar Garu da ta Dangoriba da karamar hukumar Babura ta bullo da shi akan Kudi Naira Milyan 49 da dubu 500, inda aka samar da rijiyoyin ban ruwa dari-dari a kowacce fadama.
Alhaji Usman Musari ya kuma yabawa karamar hukumar Babura bisa kyakkyawar aniyarta, ta mara baya ga kokarin gwamnatin Malam Umar Namadi wajen bunkasa tattalin arzikin matasa ta fuskar hadahadar aikin noma.
A jawabin sa, shugaban karamar hukumar Babura Malam Hamisu Muhammad Garu, ya bayyana ziyarar a matsayin wani sanannen aiki da Majalisa ke yi duk shekara, inda ya yi kira ga ma’aikata da ‘yan majalisar zartaswar karamar hukumar da su bada cikakken hadin kai domin samun nasarar ziyarar.
Sauran ‘yan kwamatin sun hada da mataimakin shugaban kwamatin kuma wakilin mazabar Kaugama Alhaji Sani Sale Zaburan da wakilin mazabar Kanya Babba Alhaji Ibrahim Hashim Kanya da mataimakan sakatare da Oditoci biyu.
Usman Mohammed Zaria