Ɗaliban Kano za su koma makaranta ranar Lahadi da Litinin – Gwamnati
Published: 5th, April 2025 GMT
Gwamnatin Jihar Kano, ta bayyana cewa ɗaliban makarantun kwana na gwamnati da na masu zaman kansu za su koma makaranta a ranar Lahadi 6 ga watan Afrilu, 2025.
Wannan ya shafi makarantun firamare da sakandare domin ci gaba da zangon karatu na uku na shekarar 2024 zuwa 2025.
Boko Haram haram ta kashe ɗan sanda a sabon hari a Borno An haramta wa Akpabio da Natasha tattaunawa da manema labaraiGa ɗaliban makarantun jeka ka dawo kuwa, za su koma makaranta a ranar Litinin 7 ga wata.
Sanarwar da Daraktan Wayar da Kai na Ma’aikatar Ilimi ta Jihar Kano, Balarabe Abdullahi Kiru, ya fitar, ta buƙaci iyaye da su kula da wannan rana domin tabbatar da cewa yara sun koma makaranta a kan lokaci.
Kwamishinan Ilimi na Jihar Kano, Dokta Ali Haruna Makoda, ya gargadi ɗalibai da su guji kawo miyagun abubuwa kamar wuƙa, reza ko ƙwayoyi zuwa makaranta.
Ya kuma ce gwamnati za ta ɗauki mataki a kan duk ɗalibin da ya ƙi bin wannan doka.
Ya ƙara da cewa bin doka da ƙa’ida na taimaka wa ɗalibai su samu nasara a karatunsu.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Ɗalibai gwamnati Komawa Makaranta Ma aikatar ilimi koma makaranta
এছাড়াও পড়ুন:
Ministan Harkokin Wajen Kasar Iran Ya Ce Ba’a Rufe Kofar Diblomasiyya Ba, Matukar HKI Ta Dakatar Da Kaiwa Kasar HKI
Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Araghchi ya bayyaana cewa kasarsa bata rufe kofar diblomasiyya dangane da shirinta na makamashin Nukliya ba, matukar HKI zata dakatar da hare-haren da take kaiwa kasar.
Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto ministan yana fadar haka a yau Lahadi a taron yan jaridun da ya kira a birnin Tehran. Ya kuma kara da cewa Iran tana son ta ci gaba da shirinta na makamashin Nukliya ta zaman lafiya ta hanyar diblomasiyya idan an bata damar yin haka.
Ministan ya ce ikidar JMI ne warware dukkan matsaloli da farko ta hanyar Diblomasiyya, da kuma tattaunawa amma ba zamu taba amincewa wani ya hanamu hakkimu na mallakar makamashi nukliya ta zaman lafiya ba. Kuma mun bayyana cewa a shirye muke a gudanar da bincike a ayyukammu. Sojojin Iran sun cilla wasu sabbin hare-hare a kan HKI a yau Lahadi da rana.
Yakin da HKI ta fara a safiyar jumma’an da ta gabata, mai kuma samun goyon bayan Amurka, don tilsatawa Iran amincewa da sharuddanta na shirin Iran na makamashin nukliya ne.