Hukumar Kasuwanci ta Duniya (WTO) da asusun lamuni na duniya (IMF) sun nuna damuwa game da tabarbarewar tattalin arziki daga sabbin harajin da gwamnatin Trump ta laftawa duniya, suna masu gargadin cewa hakan zai iya kawo cikas ga harkokin kasuwanci da kuma ci gaban tattalin arzikin duniya.

A cikin wata sanarwa da ta fitar, WTO ta yi hasashen cewa harajin Amurka da ya hada da wanda aka gabatar a farkon wannan shekara zai iya rage cinikin hajoji a duniya da kashi 1 cikin 100 a shekarar 2025, wanda zai kaucewa hasashen da ta yi a baya na fadada cinikayya.

Rahoton ciniki na duniya na WTO, wanda aka fitar a watan Oktoban bara, ya yi hasashen cinikin kayayyaki a duniya zai karu da kashi 3 cikin 100 a bana, saidai karuwar rikicin siyasa da rashin tabbas kan manufofin tattalin arziki a yanzu sun sanya shakku sosai kan wannan hasashen.

Darakta-Janar na WTO Ngozi Okonjo-Iweala ta yi gargadin cewa matakan harajin na iya rikidewa zuwa yakin cinikayya, wanda zai kai ga daukar matakin ramuwar gayya daga wasu kasashe da kuma kara cutar da kasuwancin duniya.

Ita ma a nata bangaren, shugabar hukumar ba da lamuni ta duniya IMF, Kristalina Georgieva, ta bayyana irin wannan damuwar a ranar Alhamis, inda ta bayyana irin hadarin da harajin na Amurka ke haifarwa ga daidaiton tattalin arzikin duniya.

Yayin da IMF ke ci gaba da tantance tasirin lamarin, ta yi gargadin cewa wadannan matakan za su iya dagula hasashen ci gaban da aka samu a duniya da kuma haifar da rashin tabbas.

Sabon harajin da shugaban Amurka Donald Trump ya sanar a baya-bayan nan, wanda zai fara aiki a ranar Asabar, ya sanya kashi 10% kan duk wasu kayayyakin da ake shigowa da su kasar waje, tare da karin haraji kan kasashen da ke da gibin kasuwanci mafi girma da kasarsa.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

An Bude Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayya Na Sin Da Afirka A Changsha

A yau Alhamis ne aka bude bikin baje kolin hada-hadar tattalin arziki da cinikayya na Sin da Afirka karo na hudu a birnin Changsha fadar mulkin lardin Hunan, taron dake kara jaddada himmar kasar Sin ta fuskar karfafa alaka da nahiyar Afirka, nahiyar dake da mafiya yawan kasashe masu tasowa a duniya baki daya.

Kusan kamfanonin Sin da na kasashen Afirka 4,700, da sama da mahalarta 30,000 ne za su halarci bikin na kwanaki hudu, wanda aka yiwa taken “Sin da Afirka: Tunkarar zamanantarwa tare.” Rahotanni daga mashirya bikin na cewa, kwarya-kwaryar darajar ayyukan hadin gwiwa da aka amincewa sun haura dalar Amurka biliyan 11.

Ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi, ya halarci bikin bude baje kolin, inda kuma ya yi amannar cewa taron zai samar da karin damammaki ga hadin gwiwar Sin da Afirka, tare da haifar da kyakkyawan sakamako.

Wang Yi, wanda memba ne a ofishin siyasa na kwamitin kolin JKS, ya kara da cewa, duk irin sauyin da aka samu a fannin cudanyar sassan kasa da kasa, Sin za ta ci gaba da tsayawa tsayin daka tare da nahiyar Afirka, za ta samar da kakkarfan tallafi ga ayyukan zamanantar da nahiyar, da kasancewa kawa ta gari, kuma sahihiyar ‘yar uwa ga Afirka kan hanyar nahiyar ta samun ci gaba. (Mai fassara: Saminu Alhassan)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Trump ya dakatar da kamen baƙin haure a wasu wurare na Amurka
  • Wakilin Sin: Matakin Amurka Game Da Harajin Kwastam Bai Yi La’akari Da Rarar Cinikayyar Hidimomi Ba
  • Gwamnatin Najeriya Ta Yi Allawadai Da Harin Da “Isra’ila” Ta Kawo Wa Iran
  • Arakci: Babu Wani Dalili Na Ci Gaba Da Tattaunawa Tsakanin Iran Da Amurka
  • Nijeriya Na Kan Hanyar Farfaɗowar Tattalin Arziki Da Dawo Da Martabar Ƙasa — Ministan Yaɗa Labarai
  • Bin Hanya Daya Da Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Muhimmin Mataki Ne Na Ba Da Tabbaci Ga Huldar Ciniki Da Tattalin Arzikin Sin Da Amurka
  • Iran tana da hakkin mayar da martani ga Isra’ila : Sanarwar Ma’aikatar harkokin waje
  • Kuri’un Jin Ra’ayi Na CGTN: An Yi Kira Ga Amurka Da Ta Cimma Daidaito Da Sin Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya
  • Ministocin Harkokin Wajen Sin Da Afirka Sun Yi Alkawarin Karfafa Alaka
  • An Bude Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayya Na Sin Da Afirka A Changsha