Majalisar Dokokin Jihar Kaduna ta amince da wani kudirin doka da ya soke Dokar Kwalejin Kimiyya da Fasaha na Jihar Kaduna ta shekarar 1989, tare da maye gurbin ta da dokar Kwalejin Kimiyya da Fasaha ta Nuhu Bamalli.

Kudirin, mai taken “Kudirin Soke Dokar Kwalejin Kimiyya da Fasaha ta Jihar Kaduna na Shekarar 1989 (Dokokin Jihar Kaduna na Shekarar 1991) da kuma Kafa Dokar Kwalejin Kimiyya da Fasaha ta Nuhu Bamalli, 2025,” an amince da shi ne yayin zaman majalisar wanda Shugaban Majalisar, Rt.

Hon. Yusuf Dahiru Liman, ya jagoranta.

 

Yusuf Liman ya bayyana cewa sabuwar dokar za ta bai wa kwalejin damar yin gogayya da sauran manyan cibiyoyin ilimi a fadin kasar nan, tare da dacewa da tsarin karatu na zamani. Ya jaddada muhimmancin sabunta tsarin dokar duba da yadda kwalejin ke samar da kwararrun dalibai masu nagarta.

Tunda farko da Yake gabatar da rahoto akan Kudirin dokar, Shugaban Kwamitin Hadin Giwa na Ilimi da Shari’a na majalisar, Barr. Mahmud Lawal Isma’ila, ya ce sun gudanar da bincike mai zurfi tare da tuntubar masu ruwa da tsaki, kuma suka gano cewa tsohuwar dokar ba ta dace da tsarin zamani ba.

Barrister Isma’ila ya ce sabuwar dokar ta kunshi muhimman sauye-sauye kamar mayar da wa’adin shugabancin makarantar zuwa shekara biyar kacal ba tare da sabuntawa ba, maimakon tsohon tsarin wa’adin shekara biyu da za a iya sabunta.

Yace wannan doka ta dace da tsarin ilimin manyan makarantu na kasar nan musamman a bangaren fasaha da kere-kere don cigaba mai maana.

Shima da Yake tsokaci Bayan amincewa da kudirin ya zama doka, Barr. Emmanuel Kantiyok, wanda ya dauki nauyin gabatar kudirin, ya yaba da yadda majalisar ta amince da dokar, yana mai cewa sabuwar dokar za ta bayar da ginshikin doka mai karfi ga ci gaban kwalejin, tare da tabbatar da cewa za a aiwatar da sauye-sauyen da dokar ta tanadar sannu a hankali don inganta tsarin ilimi a Jihar Kaduna.

Ya ce, daga yanzu, duk wanda ke rike da takardar shaidar Kwalejin Kimiyya da Fasaha ta Nuhu Bamalli yana da cikakken kariya da amincewa karkashin tanadin doka.

Shamsuddeen Mannir Atiku

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Kwaleji Majalisar Dokar Kwalejin Kimiyya da Fasaha dokar Kwalejin Kimiyya da Fasaha Kwalejin Kimiyya da Fasaha ta Jihar Kaduna

এছাড়াও পড়ুন:

Kawancen Jam’iyyun Adawa A Kasar Ivory Coast Ya Bukaci Gyara Wa Tsarin Zabe Kasar

Kawamcen jam’iyyun siyasa na kasar Ivory Coast ya bukaci a sake lalen yadda aka tsara yadda ake ristar jam’iyyu a hukumar zaben kasar, ganin yadda ta hana rijistar wasu jam’iyyun saboda dalilai daban daban.

Shafin yanar gizo na labarai Afirka news ya bayyana cewa an kafa kawancen ne wanda aka sanyawa suna CAP-CI a farkon wannan shekarar, don tunkarar zaben shugaban kasa wanda za’a gudanar a ranar 25 ga watan Octoban shekara ta 2025 da muke ciki.

Kawancen CAP gamayyar jam’iyyun adawa da dama ne na kasar, in banda Jam’iyyar da Lauranta Bagbo a kafa don tunkarar zaben na watan Octoba. Har’ila yau kawancen na zargin hukumar zaben kasar da rashin adalci a yadda take amincewa da yan takara a zaben. A ranar 31 ga watan Mayun da muke cikin ne kawancen jam’iyyun adawar zasu gabatar da taronsu na farko don tattauana wadan nan matsaloli, da kuma yadda zasu tunkari gwamnati mai ci da kuma hukumar zabe don warwaresu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ‘Yan sanda sun bankaɗo masana’antar man gyaɗa na bogi a Kaduna
  • Nijar Ta Soke Yarjejeniyar Tattara Bayanai Da Rasha Da Turkiyya, Ta Fara Neman Sabbin Abokan Hulɗa
  • Majalisar Dattawa ta kafa kwamitin lura da gwamnan riƙo na Jihar Ribas
  • Kawancen Jam’iyyun Adawa A Kasar Ivory Coast Ya Bukaci Gyara Wa Tsarin Zabe Kasar
  • Friedrich Merz ya zama sabon shugaban gwamnatin Jamus
  • An kashe mutum 6 a sabon hari a Filato
  • Majalisar Kano Ta Amince Da Dokar Wutar Lantarki Da Za Ta Raba Wa Jihohi 3 Wuta
  • Amurka sake kai sabon hari kan kasar Yemen
  • An Kama Wani Ɗan Ghana Bisa Zargin Kai Mata Hajji Ba Tare Da Lasisi Ba