Majalisar Jihar Kaduna Ta Zartas da Dokar Sabon Kudiri Kan Kwalejin Nuhu Bamalli, Ta Soke Na 1989
Published: 7th, May 2025 GMT
Majalisar Dokokin Jihar Kaduna ta amince da wani kudirin doka da ya soke Dokar Kwalejin Kimiyya da Fasaha na Jihar Kaduna ta shekarar 1989, tare da maye gurbin ta da dokar Kwalejin Kimiyya da Fasaha ta Nuhu Bamalli.
Kudirin, mai taken “Kudirin Soke Dokar Kwalejin Kimiyya da Fasaha ta Jihar Kaduna na Shekarar 1989 (Dokokin Jihar Kaduna na Shekarar 1991) da kuma Kafa Dokar Kwalejin Kimiyya da Fasaha ta Nuhu Bamalli, 2025,” an amince da shi ne yayin zaman majalisar wanda Shugaban Majalisar, Rt.
Yusuf Liman ya bayyana cewa sabuwar dokar za ta bai wa kwalejin damar yin gogayya da sauran manyan cibiyoyin ilimi a fadin kasar nan, tare da dacewa da tsarin karatu na zamani. Ya jaddada muhimmancin sabunta tsarin dokar duba da yadda kwalejin ke samar da kwararrun dalibai masu nagarta.
Tunda farko da Yake gabatar da rahoto akan Kudirin dokar, Shugaban Kwamitin Hadin Giwa na Ilimi da Shari’a na majalisar, Barr. Mahmud Lawal Isma’ila, ya ce sun gudanar da bincike mai zurfi tare da tuntubar masu ruwa da tsaki, kuma suka gano cewa tsohuwar dokar ba ta dace da tsarin zamani ba.
Barrister Isma’ila ya ce sabuwar dokar ta kunshi muhimman sauye-sauye kamar mayar da wa’adin shugabancin makarantar zuwa shekara biyar kacal ba tare da sabuntawa ba, maimakon tsohon tsarin wa’adin shekara biyu da za a iya sabunta.
Yace wannan doka ta dace da tsarin ilimin manyan makarantu na kasar nan musamman a bangaren fasaha da kere-kere don cigaba mai maana.
Shima da Yake tsokaci Bayan amincewa da kudirin ya zama doka, Barr. Emmanuel Kantiyok, wanda ya dauki nauyin gabatar kudirin, ya yaba da yadda majalisar ta amince da dokar, yana mai cewa sabuwar dokar za ta bayar da ginshikin doka mai karfi ga ci gaban kwalejin, tare da tabbatar da cewa za a aiwatar da sauye-sauyen da dokar ta tanadar sannu a hankali don inganta tsarin ilimi a Jihar Kaduna.
Ya ce, daga yanzu, duk wanda ke rike da takardar shaidar Kwalejin Kimiyya da Fasaha ta Nuhu Bamalli yana da cikakken kariya da amincewa karkashin tanadin doka.
Shamsuddeen Mannir Atiku
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Kwaleji Majalisar Dokar Kwalejin Kimiyya da Fasaha dokar Kwalejin Kimiyya da Fasaha Kwalejin Kimiyya da Fasaha ta Jihar Kaduna
এছাড়াও পড়ুন:
Korea Ta Arewa Ta Sanar Da Kera Wani Sabon Makami Na Sirri
Shugaban kasar Korea Ta Arewa Kim jung Un ne ya sanar da cewa kasarsa ta kera wani sabon makami na sirri, kuma ta samu ci gaba sosai a fagen nazari da binciken kayan tsaro.
Shugaban kasar ta Korea Ta Arewa Kim Jun Ung wanda ya yi Magana da kamfanin dillancin labarun kasar ya kara da cewa; Sabbin makaman da su ka kera za su taimaka matuka wajen karfafa sojojin kasar.”
Haka nan kuma ya ce, kasar Korea ta Arewa ta kuma karfafa sojojinta na ruwa ta hanyar kara samar da jiragen ruwa na yaki masu ninkaya a karkashin ruwa.”
Kamfanin dillancin labarun Korea Ta Arewa ya sanar da cewa, a ranar Juma’ar da ta gabata ne shugaban kasar Kim Jun Ung ya sa ido akan gwajin sabon makamin da aka yi, da su ka hada da jiragen sama marasa matuki na kai hari.”
Shugaban kasar ta Korea Ta Arewa ya jaddada muhimmancin yin amfani da kirkirarriyar fasaha domin karfafa harkokin tsaro.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Jirgin Ruwan “Umar Mukhtar” Na Agaji Ya Kama Hanyar Zuwa Gaza Daga Kasar Libya September 22, 2025 Jagoran Juyin Juya Halin Musulunci Ya Jinjinawa Tawagar Kokawar Greco-Roma Ta Iran Murnar Lashe Gasar Cin Kofin Duniya September 22, 2025 Pezeshkian: Kasashen Da Ba Su Cika Alkawura Da Suka Dauka Ba Suke Zargin Iran Kan Rashin Mutanta Yarjejeniyar Nukiliya September 22, 2025 Dakarun IRGC: Iran Za Ta Tarwatsa Makiya Tare Da Mayar Da Martani Kan Duk Wani Zalunci September 22, 2025 Kungiyar Ansarullahi Ta Yemen: ‘Yan Koren Amurka Da Isra’ila Suke Neman Wargaza Hadin Kan Larabawa Da Na Musulmi September 22, 2025 Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Aiwatar Da Kisan Gilla Kan Fararen Hula 5 A Kudancin Kasar Lebanon September 22, 2025 Ministan Harkokin Waken Falasdinu Ta Yi Kira Ga Karin Kasashe Su Amince Da Samuwar Kasarta September 21, 2025 Iran Da Pakistan Sun Sake Tsara Dangantakarsu Ta Tattalin Arziki September 21, 2025 Trump Ya Bukaci Afganistan Ta Mayarwa Amurka Sansanin Jiragen Sama Na bagram September 21, 2025 Kasashen Ingila Da Canada Da Kuma Australia Sun Bayyana Amincewarsu Da Samuwar Kasar Falasdinu September 21, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci