Majalisar Dokokin Jihar Kaduna ta amince da wani kudirin doka da ya soke Dokar Kwalejin Kimiyya da Fasaha na Jihar Kaduna ta shekarar 1989, tare da maye gurbin ta da dokar Kwalejin Kimiyya da Fasaha ta Nuhu Bamalli.

Kudirin, mai taken “Kudirin Soke Dokar Kwalejin Kimiyya da Fasaha ta Jihar Kaduna na Shekarar 1989 (Dokokin Jihar Kaduna na Shekarar 1991) da kuma Kafa Dokar Kwalejin Kimiyya da Fasaha ta Nuhu Bamalli, 2025,” an amince da shi ne yayin zaman majalisar wanda Shugaban Majalisar, Rt.

Hon. Yusuf Dahiru Liman, ya jagoranta.

 

Yusuf Liman ya bayyana cewa sabuwar dokar za ta bai wa kwalejin damar yin gogayya da sauran manyan cibiyoyin ilimi a fadin kasar nan, tare da dacewa da tsarin karatu na zamani. Ya jaddada muhimmancin sabunta tsarin dokar duba da yadda kwalejin ke samar da kwararrun dalibai masu nagarta.

Tunda farko da Yake gabatar da rahoto akan Kudirin dokar, Shugaban Kwamitin Hadin Giwa na Ilimi da Shari’a na majalisar, Barr. Mahmud Lawal Isma’ila, ya ce sun gudanar da bincike mai zurfi tare da tuntubar masu ruwa da tsaki, kuma suka gano cewa tsohuwar dokar ba ta dace da tsarin zamani ba.

Barrister Isma’ila ya ce sabuwar dokar ta kunshi muhimman sauye-sauye kamar mayar da wa’adin shugabancin makarantar zuwa shekara biyar kacal ba tare da sabuntawa ba, maimakon tsohon tsarin wa’adin shekara biyu da za a iya sabunta.

Yace wannan doka ta dace da tsarin ilimin manyan makarantu na kasar nan musamman a bangaren fasaha da kere-kere don cigaba mai maana.

Shima da Yake tsokaci Bayan amincewa da kudirin ya zama doka, Barr. Emmanuel Kantiyok, wanda ya dauki nauyin gabatar kudirin, ya yaba da yadda majalisar ta amince da dokar, yana mai cewa sabuwar dokar za ta bayar da ginshikin doka mai karfi ga ci gaban kwalejin, tare da tabbatar da cewa za a aiwatar da sauye-sauyen da dokar ta tanadar sannu a hankali don inganta tsarin ilimi a Jihar Kaduna.

Ya ce, daga yanzu, duk wanda ke rike da takardar shaidar Kwalejin Kimiyya da Fasaha ta Nuhu Bamalli yana da cikakken kariya da amincewa karkashin tanadin doka.

Shamsuddeen Mannir Atiku

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Kwaleji Majalisar Dokar Kwalejin Kimiyya da Fasaha dokar Kwalejin Kimiyya da Fasaha Kwalejin Kimiyya da Fasaha ta Jihar Kaduna

এছাড়াও পড়ুন:

Bio ya maye gurbin Tinubu a matsayin sabon shugaban ECOWAS

Shugaban Ƙasar Saliyo, Julius Maada Bio, ya zama sabon shugaban Ƙungiyar Raya Tattalin Arziƙin Ƙasashen Yammacin Afirka (ECOWAS), inda ya karɓi ragamar shugabancin daga Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu.

An sanar da hakan ne a taron shugabannin ECOWAS karo na 67 da aka gudanar a Abuja.

An kashe matar aure, manomi ya jikkata a wani sabon hari a Kaduna ’Yan bindiga sun sace babban alƙali a Bayelsa 

Shugaba Tinubu, wanda ya yi wa’adin shugabancin ƙungiyar sau biyu tun daga shekarar 2023, ya bayyana cewa shugabancin ECOWAS babban abu ne a rayuwarsa.

Ya ce: “Yayin da nake miƙa ragamar shugabanci ga abokina kuma ɗan uwana, Shugaba Julius Maada Bio, ina mai gamsuwa da fatan alheri ga makomar Yammacin Afirka.”

Ya ƙara da cewa wajibi ne ƙasashen yankin su haɗa kai wajen tabbatar da zaman lafiya, ci gaban dimokuraɗiyya da kuma bunƙasa tattalin arziƙi.

“Mu ƙara inganta haɗin kai, mu mutunta ƙa’idojin diflomasiyya, sannan mu tabbatar da ci gaba wanda zai haɗa kowa da kowa musamman matasa, mata da waɗanda ke cikin mawuyacin hali,” in ji Tinubu.

A jawabinsa na karɓar shugabanci, Shugaba Bio ya gode wa Tinubu bisa jagoranci mai cike da hangen nesa da kyakkyawan fata.

Ya ce: “Shugabancinka a ECOWAS ya nuna jajircewa wajen ƙarfafa tattaunawar yankin, farfaɗo da tattalin arziƙi da wanzar da zaman lafiya.

“Na ji kaina a matsayin mai ɗaukar wannan nauyi domin ci gaba daga inda ka tsaya.”

Shugaba Bio ya bayyana cewa akwai buƙatar ECOWAS ta ƙara dagewa wajen kare dimokuraɗiyya, inganta tsaro da bunƙasa tattalin arziƙi.

“Dole mu sake fasalin ECOWAS ta yadda za ta zama mai gaskiya, inganci da amsa buƙatun al’ummarta,” in ji shi.

Ya kuma bayyana matsalolin da yankin ke fuskanta kamar ta’addanci, taɓarɓarewar siyasa da matsin tattalin arziki.

Ya ce: “Fagen dimokuraɗiyya yana fuskantar ƙalubale a sassa daban-daban na yankin. A wasu ƙasashe, tsarin mulki ya rikiɗe.

“Amma matasa na faɗin Yammacin Afirka na buƙatar ba kawai zaɓe ba, har ma da gaskiya, da ba su damar shiga cikin tafiyar da rayuwar ƙasa.”

Hakazalika, Bio ya ce zai yi jagoranci ECOWAS cikin gaskiya da fifita buƙatun al’umma tare da inganta haɗin kan yankin.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Majalisa Ta Yi Allah-wadai Da Kashe Wasu Matafiya ‘Yan Kaduna 13 A Jihar Filato
  • Majalisar Dattawa Ta Kara Tsawaita Aiwatar Da Ayyukan Kasafin Kudi Na 2024 Da Wata 6
  • Sarkin Musulmi ya ba da umarnin fara duban watan Muharram
  • ‘Yan Bindiga Sun Sace Dukkan Fasinjojin Motar Bas A Jihar Benuwe
  • Ina Da Isassun Kuɗi, Ban Ciwo Bashin Ko Kwabo Ɗaya Don Gyara Jihar Zamfara Ba – Gwamna Lawal
  • Bio ya maye gurbin Tinubu a matsayin sabon shugaban ECOWAS
  • An kashe matar aure, manomi ya jikkata a wani sabon hari a Kaduna
  • Gwamnatin Hong Kong Ta Gudanar Da Bikin Cika Shekaru Biyar Da Kafuwar Dokar Tsaron Kasa Ta Yankin
  • Gwamnonin Arewa sun yi Allah-wadai da kisan ’yan ɗaurin aure a Filato
  • Firaministan Singapore: Jama’ar Sin Suna Da Kwarewar Kirkire-Kirkiren Fasahohi