Amurka ta kakaba wa Iran sabbin takunkumai duk da tattaunawa
Published: 23rd, April 2025 GMT
Gwamnatin Amurka ta kakabawa kamfanonin kasar Iran sabbin takunkumi, duk da tattaunawar da ake yi kan shirin nukiliyar.
Ofishin kula da kadarorin waje na ma’aikatar baitul malin Amurka (OFAC) ya sanar a cikin wata sanarwa jiya Talata cewa, ya kara sunan wani dan kasuwa dan kasar Iran, Seyyed Assadollah Emamjomeh da kamfaninsa cikin jerin takunkumin da aka kakabawa Iran bisa zarginsu da hannu wajen fitar da danyen mai da iskar gas a Iran.
Amurka ta yi zargin cewa Emamjomeh da mukarrabansa ne ke da alhakin jigilar danyen mai na iran da aka kiyasta ya kai daruruwan miliyoyin daloli zuwa kasuwannin kasashen waje.
Ma’aikatar Baitulmali ta Amurka ta yi zargin cewa kamfanin Emamjomeh ya fitar da dubunnan kayayyaki daga Iran zuwa Pakistan tare da gudanar da hada-hadar kudi na miliyoyin daloli.
Sabon takunkumin dai shi ne irinsa na bakwai da gwamnatin Amurka ta dauka kan Iran tun a ranar 4 ga watan Fabrairu, lokacin da shugaban Amurka Donald Trump ya zartar da dokar yin matsin lamba kan Tehran.
Sabbin takunkuman dai na zuwa ne a daidai lokacin da Iran da Amurka suka gudanar da shawarwari guda biyu domin warware sabanin da ke tsakaninsu dangane da shirin nukiliyar Iran na zaman lafiya.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Hakar man Kolmani: Jihohin Bauchi da Gombe sun gana da NNPC kan bukatun al’umma
Jami’an gwamnati daga jihohin Gombe da Bauchi sun gudanar da wani taron kwana biyu tare da wakilan kamfanin NNPC da Kamfanin AOML, waɗanda ke gudanar da aikin hakar danyen mai a yankin Kolmani.
An kira taron ne don neman ƙarin bayani kan matakan da AOML ta riga ta ɗauka da kuma gyara kura-kuran da aka gani daidai da Dokar Masana’antar Man Fetur (PIA), da nufin kauce wasau matsalolin da suka addabi sauran yankuna masu arzikin mai.
Wata sanarwa da Kwamishinan Ma’adinai da Makamashi na Jihar Gombe, Sanusi Ahmed Pindiga, ya fitar, ta ce Kwamitin Haɗin Gwiwa da ke wakiltar jihohin biyu ya gano muhimman fannoni huɗu da ke kawo damuwa, waɗanda suka haɗa da sayen filaye, rashin gudanar da ‘Yancin Aiki (FTO), rashin bin ka’idojin Alhakin Ci Gaban Al’umma (CSR) daga AOML, da kuma gibin sadarwa.
Ya ƙara da cewa don magance matsalolin da aka gano, Kwamitin Haɗin Gwiwa ya yanke shawarar cewa za a kammala sayen filaye da zarar AOML ta samar da takardun biyan kuɗi da suka dace, yayin da NNPC zai ta bi diddigin kamfanin kan biyan kuɗin FTO don hakar mai.
Jami’an Sibil Difens sun bude wuta a garin Jos Za mu gina mayankar dabbobi ta Naira biliyan 3 a Gombe —GwamnatiA cewarsa, za a gudanar da cikakken binciken buƙatu a cikin al’ummomin masu makwabtaka da rijiyar man da waɗanda suka fuskanci matsaloli a sakamakon aikin hakar man don jagorantar shirye-shiryen ayyukan Alhakin Ci Gaban Al’umma (CSR).
Bugu da kari, za a kafa tsarin sadarwa don tabbatar da ingantacciyar mu’amala tsakanin masu gudanar da aikin Filin Mai na Kolmani da dukkan masu ruwa da tsaki.
“Mahalarta taron sun nuna godiya ga shiga tsakani a kan lokaci kuma sun sake jaddada jajircewarsu ta haɗin gwiwa don tabbatar da cewa aikin Filin Mai na Kolmani ya ci gaba ta hanyar da za ta amfani dukkan masu ruwa da tsaki kuma ta bi doka,” in ji Pindiga.
Ya ƙara da cewa: “Sun kuma sake jaddada fatansu cewa burin samun mai da iskar gas na Arewacin ƙasar da aka daɗe ana jira zai tabbata, kuma zai kawo ci gaban tattalin arziki ga yankin.”