HausaTv:
2025-07-09@07:50:49 GMT

Amurka ta kakaba wa Iran sabbin takunkumai duk da tattaunawa

Published: 23rd, April 2025 GMT

Gwamnatin Amurka ta kakabawa kamfanonin kasar Iran sabbin takunkumi, duk da tattaunawar da ake yi kan shirin nukiliyar.  

Ofishin kula da kadarorin waje na ma’aikatar baitul malin Amurka (OFAC) ya sanar a cikin wata sanarwa jiya Talata cewa, ya kara sunan wani dan kasuwa dan kasar Iran, Seyyed Assadollah Emamjomeh da kamfaninsa cikin jerin takunkumin da aka kakabawa Iran bisa zarginsu da hannu wajen fitar da danyen mai da iskar gas a Iran.

Amurka ta yi zargin cewa Emamjomeh da mukarrabansa ne ke da alhakin jigilar danyen mai na iran da aka kiyasta ya kai daruruwan miliyoyin daloli zuwa kasuwannin kasashen waje.     

Ma’aikatar Baitulmali ta Amurka ta yi zargin cewa kamfanin Emamjomeh ya fitar da dubunnan kayayyaki daga Iran zuwa Pakistan tare da gudanar da hada-hadar kudi na miliyoyin daloli.

Sabon takunkumin dai shi ne irinsa na bakwai da gwamnatin Amurka ta dauka kan Iran tun a ranar 4 ga watan Fabrairu, lokacin da shugaban Amurka Donald Trump ya zartar da dokar yin matsin lamba kan Tehran.

Sabbin takunkuman dai na zuwa ne a daidai lokacin da Iran da Amurka suka gudanar da shawarwari guda biyu domin warware sabanin da ke tsakaninsu dangane da shirin nukiliyar Iran na zaman lafiya.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Kakakin Hafsan Hafsoshin Sojin Iran Ya Ce: Iranta Dorawa Amurka Alhakin Duk Harin Da Ta Fuskanta

Kakakin hafsan hafsoshin sojojin Iran ya ce; Iran tana dora wa Amurka  alhakin duk wani hari da za a kai mata

Kakakin hafsan hafsoshin sojojin kasar Iran Birgediya Janar Abul-fazl Shekarchi ya jaddada cewa: Iran tana dorawa Amurka alhakin duk wani harin wuce gona da iri da za a kaddamar kan kasarta.

A wata hira ta musamman da ya yi da tashar talabijin ta Al-Mayadeen, Shekarchi ya bayyana cewa: Sojojin kasar Iran ba su ne suka kaddamar da harin kan wata kasa ba, amma sun mayar da martani cikin kwanaki 12 na arangama da munanan hare-hare da suka fuskanta daga mabartan ‘yan sahayoniyya makiya.

Ya kara da cewa, “An sanya wa makiya tsagaita bude wuta ne bayan da suka fuskanci munanan hare-hare daga sojojin Iran,” yana mai cewa, “Iran sakamakon karfin martanin sojojinta ne ta tilastawa makiya dakatar da yakin, ba kamar yadda suke ikirari ba, cewa su ne suka dakatar da yakin a kashin kansu, sannan kuma Iran ce karshen wacce ta harba makamai masu linzami da jirage marasa matuka ciki kan mabarnata ‘yan sahayoniyya.”

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Aragchi: Amurka Tana Iya Farfado Da Tattaunawa Kan Shirin Makamashin Nukliyar Kasar Idan Tanaso
  • Aragchi: Amurka Tana Iya Farfado Da Tattaunawa Kan Shirin Makamashin Nukliya Kasar Idan Tanaso
  • Iran Ta Tabbatar Da Cewa Tana Iya Yakar Amurka Da HKI A Lokaci Guda
  • Iran Za Ta Yi Nazarin Sabuwar Gayyatar Da Amurka Ta Yi Mata Na  Sabuwar Tattaunawa
  • Shugaban Kasar Iran Ya Ce; An Rusa Hanyar Tattaunawa da Iran Kan Shirin Na Makamashin Nukiliya Na Zaman Lafiya
  • Kakakin Hafsan Hafsoshin Sojin Iran Ya Ce: Iranta Dorawa Amurka Alhakin Duk Harin Da Ta Fuskanta
  • HKI Tana Tana Son Ci Gaba Da Yaki Kuma Trump Yana Tare Da Shi
  • Reuters: Amurka Tana Da Shirin Korar Falasdinawa Daga Gaza
  • Al’ummar A sassan Duniya Sun Gudanar Da Zanga-Zangar Goyon Bayan Falasdinawa
  • Al’ummar Iran Mabiya Imam Husain {a.s} Ba Za Su Taba Mika Kai Ga Kaskanci Ba