HausaTv:
2025-07-09@05:36:30 GMT

Amurka ta kakaba wa Iran sabbin takunkumai duk da tattaunawa

Published: 23rd, April 2025 GMT

Gwamnatin Amurka ta kakabawa kamfanonin kasar Iran sabbin takunkumi, duk da tattaunawar da ake yi kan shirin nukiliyar.  

Ofishin kula da kadarorin waje na ma’aikatar baitul malin Amurka (OFAC) ya sanar a cikin wata sanarwa jiya Talata cewa, ya kara sunan wani dan kasuwa dan kasar Iran, Seyyed Assadollah Emamjomeh da kamfaninsa cikin jerin takunkumin da aka kakabawa Iran bisa zarginsu da hannu wajen fitar da danyen mai da iskar gas a Iran.

Amurka ta yi zargin cewa Emamjomeh da mukarrabansa ne ke da alhakin jigilar danyen mai na iran da aka kiyasta ya kai daruruwan miliyoyin daloli zuwa kasuwannin kasashen waje.     

Ma’aikatar Baitulmali ta Amurka ta yi zargin cewa kamfanin Emamjomeh ya fitar da dubunnan kayayyaki daga Iran zuwa Pakistan tare da gudanar da hada-hadar kudi na miliyoyin daloli.

Sabon takunkumin dai shi ne irinsa na bakwai da gwamnatin Amurka ta dauka kan Iran tun a ranar 4 ga watan Fabrairu, lokacin da shugaban Amurka Donald Trump ya zartar da dokar yin matsin lamba kan Tehran.

Sabbin takunkuman dai na zuwa ne a daidai lokacin da Iran da Amurka suka gudanar da shawarwari guda biyu domin warware sabanin da ke tsakaninsu dangane da shirin nukiliyar Iran na zaman lafiya.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Ministan Harkokin Wajen Kasar Iran Yace Mutanen Kasarsa Suna Cikin Shiri Don Kare Kansu Da Karfi

Ministan harkokin wajen kasar Aran Abbas arachi ya bayyana cewa mutanen kasarsa a shirin suke su ci gaba da kare kasarsu daga Amurka da kuma HKI .

Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto Abbas Aragchi yana fadar haka a jiya litinin a lokacinda yake ganawa da tawagar kasar Brazil a gefen taron kungiyar BRICS karo 17 wanda ke tafiya a halin yanzu a birnin Rio de Jenero na kasar Brazil.

An gudanar da wannan taron ne saboda hare-haren da HKI da kuma Amurka suka kaiwa JMI a baya bayan nan, da kuma tasirinsa a cikin al-amuran siyasa da kuma tattalin arziki a yankin Asiya ta yamma da kuma duniya gaba daya.

Abbas Aragchi ya bayyana cewa hare-haren HKI da kuma Amurka ya sabawa dikokin kasa da kasa sannan ko wane bangare yana da rawar da zai take don ganin an tabbatar da zaman lafiya a duniya.

A nashi bangaren ministan harkokin wajen kasar Rasha Sergey Lavrov yace: hare-hare kan kasar Iran musamman a kan shirinta na makamashin nukliya na zaman lafiya abin yin tir da shi ne. Sannan ya kara da cewa kasar Rasha a shirye take ta taimaka ko a fagen kwamitin tsaro na MDD ne.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iran Za Ta Yi Nazarin Sabuwar Gayyatar Da Amurka Ta Yi Mata Na  Sabuwar Tattaunawa
  • Shugaban Kasar Iran Ya Ce; An Rusa Hanyar Tattaunawa da Iran Kan Shirin Na Makamashin Nukiliya Na Zaman Lafiya
  • Kakakin Hafsan Hafsoshin Sojin Iran Ya Ce: Iranta Dorawa Amurka Alhakin Duk Harin Da Ta Fuskanta
  • Ministan Harkokin Wajen Kasar Iran Yace Mutanen Kasarsa Suna Cikin Shiri Don Kare Kansu Da Karfi
  • HKI Tana Tana Son Ci Gaba Da Yaki Kuma Trump Yana Tare Da Shi
  • Reuters: Amurka Tana Da Shirin Korar Falasdinawa Daga Gaza
  • Al’ummar A sassan Duniya Sun Gudanar Da Zanga-Zangar Goyon Bayan Falasdinawa
  • Al’ummar Iran Mabiya Imam Husain {a.s} Ba Za Su Taba Mika Kai Ga Kaskanci Ba
  • Iran ta Bukaci Gudanar da Bincike Kan Sacewar jami’ar Diblomasiyyar kasar A Lebanon Shekaru 43 Da Suka gabata
  • Muhimman Kamfanonin Jiragen Sama A Duniya Sun Farfado Da Zirga-Zirgaf Zuwa Iran