Burkina Faso ta sanar da dakile wani yunkurin juyin mulkin a kasar
Published: 23rd, April 2025 GMT
Hukumomin Burkina Faso sun sanar da cewa sun dakile wani sabon yunkurin juyin mulki, da aka shirya daga Abidjan babban birnin kasar Ivory Coast.
Ministan tsaron Burkina Faso Mahamadou Sana ne ya fitar da cikakken bayani kan juyin mulkin da bai yi nasara ba, ya kuma kara da cewa ana fargabar sake yunkurin tayar da zaune tsaye.
Ministan tsaron Burkina Faso, Mahamadou Sana, ya bayyana a gidan talabijin na kasar cewa hukumomin kasar sun dakile yunkurin juyin mulkin da aka yi wa hukumomin gwamnati.
An dai shirya juyin mulkin ne a ranar 16 ga watan Afrilu tare da kai farmakin hadin gwiwa a fadar shugaban kasa.
Sanarwar da aka fitar a hukumance ta ce jami’an leken asiri sun kame mutane da dama musamman sojoji dake da alaka da yunkurin juyin mulkin.
Ma’aikatar ta kuma yi nuni da cewa, masu yunkurin juyin mulkin sun bullo da dabarun da za su bijire wa jami’an leken asiri tare da ingiza su wajen aiwatar da kame-kame a cikin jami’an tsaro da na cikin gida.
Idan dai ba a manta ba, an dakile wani yunkurin juyin mulkin da sojoji suka yi a watan Satumban shekarar 2023 inda aka kama sojoji hudu tare da korar mutane biyu.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Tarayya Da Stellar Steel, Sun Sanya Hannu Kan Yarjejeniyar Habaka Karafan Cikin Gida
ShareTweetSendShare MASU ALAKA Labarai Ƴansanda Sun Kama Wani Mai Wasa Da Bindiga AK-47 A Cikin Wani Bidiyo A Adamawa October 31, 2025
Manyan Labarai Kifewar Kwalekwale: Gwamnan Gombe Ya Jajanta Wa Al’ummar Nafada Kan Mutuwar Matasa Biyar October 31, 2025
Manyan Labarai NPA Da Ƙungiyar Injiniyoyi Ta Yi Haɗaka Don Bunƙasa Tashoshin Jiragen Ruwa October 31, 2025