Sojojin Haramtacciyar Kasar Isra’ila Sun Kona Yara Da Mata A Harin Da Suka Kai Khum Yunis Na Gaza
Published: 17th, April 2025 GMT
Hare-haren sojojin mamayar Isra’ila sun kona kananan yara a garin Khun-Yunis da ke kudancin Zirin Gaza
Hukumar tsaron fararen hula a Zirin Gaza ta fitar da wani faifan bidiyo a yau alhamis, inda ta ke nuna irin mummunan halin da ‘yan gudun hijiran Falasdinawa suka shiga a Khan Yunis, bayan da jiragen saman yakin gwamnatin haramtaciyar kasar Isra’ila suka yi luguden bama-bamai a kan tantunan ‘yan gudun hijiran Falasdinawa da suka rasa matsugunansu,
Tun da tsakar daren jiya ne jiragen suka fara luguden wutan kan tantunan ‘yan gudun hijiran zuwa wayewar garin yau Alhamis, inda wutar bama-baman suka kone gawarwakin yara da mata, bayan shahadan mutane da dama.
Rahotonni sun bayyana cewa: An hae-haren sun janyo shahadan yara da mata tare da kona gawarwakinsu sakamakon yin luguden makamai masu linzami kan sansanoninsu musamman wadanda suke rayuwa a cikin tantuna a yankin al-Mawasi da ke yammacin Khan Yunis.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Buɗe cibiyar horas da sabbin sojoji a Kudu zai taimaka — Janar Shaibu
Babban Hafsan Sojin Ƙasa na Najeriya, Laftanar-Janar Shaibu ya yaba, ya bayyana cewa buɗe cibiyoyin horas da sabbin kuratan sojoji (Depot) a jihohin Kudu zai ƙara ƙarfin rundunar wajen karɓar sabbin ma’aikata a faɗin ƙasa.
Laftanar-Janar Shaibu ya bayyana cewa za a buɗe sabbin cibiyoyin horas da sabbin kuratan sojojin ne a Osogbo da ke Jihar Osun da kuma Abakaliki a Jihar Ebonyi.
Ya bayyana haka ne a yayin bikin yaye sabbin dakarun soji 3,439 da aka yi a Cibiyar Horas da Sabbin Kuratan sojoji (Depot) da ke Zariya, inda ya shawarce su da su zama masu kishin ƙasa da jajircewa.
Ya yaba wa sabbin sojojin bisa jajircewa, juriya da ƙwarewa da suka nuna a tsawon watannin da suka shafe suna karɓar horo a cibiyar.
Shirin kafa ‘Hisbar Ganduje’ ya tayar da ƙura a Kano Dalilin da ya sa muka ziyarci Obasanjo — TurakiLaftanar-Janar Shaibu ya bayyana ranar a matsayin ranar nuni da babban ci gaba wajen cika manufar rundunar sojojin Najeriya ta faɗaɗa karfin ma’aikata.
Ya taya sabbin sojojin murnar kammala horon farko na soja, wanda, a cewarsa, shi ne matakin farko na doguwar tafiyar sadaukarwa, kishin ƙasa, da hidima ga al’umma.
“Kuna shiga rundunar soja ne a wani lokaci mai muhimmanci a tarihin ƙasarmu, lokacin da ƙalubalen tsaro ya yi yawa. Ku ɗauki wannan dama da muhimmanci domin ku zama wani ɓangare na mafita ga matsalolin ta’addanci da rashin tsaro,” in ji shi.
Ya buƙace su da su riƙe gaskiya, ladabi, da bin ƙa’ida a duk inda suka samu kansu, yana mai cewa horon da suka samu (a Depot NA) ya shirya su wajen fuskantar manyan ayyukan soja na zamani.
Janar Shaibu ya bayyana cewa manufar sauya tsarin rundunar soja a ƙarƙashin jagorancin Babban Hafsan Sojoji na nufin kafa runduna mai ƙwarewa, ɗorewa, da shirye-shiryen fuskantar ƙalubale cikin haɗin kai da sauran hukumomin tsaro.
Ya kuma jinjina wa Kwamandan Depot na Zariya, Janar Ahmadu Bello Muhammad, da malamai da jami’an horo saboda jajircewarsu wajen ganin an kammala horon cikin nasara.
Haka kuma, Babban Hafsan Sojoji ya gode wa Shugaban Ƙasa Bola Ahmad Tinubu, wanda shi ne Kwamandan Rundunar Sojojin Najeriya, bisa jagoranci da goyon bayan da yake bai wa rundunar, tare da godewa Gwamnan Jihar Kaduna, Sanata Uba Sani, da Mai Martaba Sarkin Zazzau, Ambasada Ahmad Nuhu Bamalli, da al’ummar Zariya saboda kyakkyawar alaƙa da rundunar soja.