Sojojin Haramtacciyar Kasar Isra’ila Sun Kona Yara Da Mata A Harin Da Suka Kai Khum Yunis Na Gaza
Published: 17th, April 2025 GMT
Hare-haren sojojin mamayar Isra’ila sun kona kananan yara a garin Khun-Yunis da ke kudancin Zirin Gaza
Hukumar tsaron fararen hula a Zirin Gaza ta fitar da wani faifan bidiyo a yau alhamis, inda ta ke nuna irin mummunan halin da ‘yan gudun hijiran Falasdinawa suka shiga a Khan Yunis, bayan da jiragen saman yakin gwamnatin haramtaciyar kasar Isra’ila suka yi luguden bama-bamai a kan tantunan ‘yan gudun hijiran Falasdinawa da suka rasa matsugunansu,
Tun da tsakar daren jiya ne jiragen suka fara luguden wutan kan tantunan ‘yan gudun hijiran zuwa wayewar garin yau Alhamis, inda wutar bama-baman suka kone gawarwakin yara da mata, bayan shahadan mutane da dama.
Rahotonni sun bayyana cewa: An hae-haren sun janyo shahadan yara da mata tare da kona gawarwakinsu sakamakon yin luguden makamai masu linzami kan sansanoninsu musamman wadanda suke rayuwa a cikin tantuna a yankin al-Mawasi da ke yammacin Khan Yunis.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
HKI Tana Amfani Yunwa A Matsayin Makamin Yaki A Kan Falasdinawa A Gaza
Wakilin falasdinawa a kutun kasa da kasa ta ICJ da ke birnin Haque na kasar Nerthelands yace HKI tana amfani da hana kayakin agaji daga ciki har da abinci shiga gaza a matsayin makami kan Falasdinawa don kashesu.
Tashar talabijib ta Presstv a nan Tehran ta nakalto Ammar Hijazi jakadan kasar Faladinu a cibiyoyin MDD a kasashen Turai yana fadar haka a gaban alkalai a kotun ta ICJ a jiya litinin.
Ya ce HKI tana kisa ta sama da makamai, sannan tana kisa ta kasa da yunwa banda haka tana ci gaba da korar Falasdinawa daga yankin yamma da kogin Jordan tun fiye da watanni 3 da sua habata.
Kutun ta bude wannan zaman ne bisa bukatar MDD ta shekara ta 2024 na bincike don tabbatar da cewa HKI tana amfani yunwaa a matsayin makami a Gaza. Ammar Hijazi ya kara da cewa banda wannan babban kotun HKI tana goyon bayan amfani da yunwa a matsayin makami a gaza tun fiye da watanni 2 da suka gabata.
Wasu lauyoyi daga kasashe daban–daban wadanda suka hada da Nerthlands da Afirka ta kudu duk sun yi magana sun kuma yi allawadai da HKI kan abinda take aikatawa a Gaza.