Hare-haren sojojin mamayar Isra’ila sun kona kananan yara a garin Khun-Yunis da ke kudancin Zirin Gaza

Hukumar tsaron fararen hula a Zirin Gaza ta fitar da wani faifan bidiyo a yau alhamis, inda ta ke nuna irin mummunan halin da ‘yan gudun hijiran Falasdinawa suka shiga a Khan Yunis, bayan da jiragen saman yakin gwamnatin haramtaciyar kasar Isra’ila suka yi luguden bama-bamai a kan tantunan ‘yan gudun hijiran Falasdinawa da suka rasa matsugunansu,

Tun da tsakar daren jiya ne jiragen suka fara luguden wutan kan tantunan ‘yan gudun hijiran zuwa wayewar garin yau Alhamis, inda wutar bama-baman suka kone gawarwakin yara da mata, bayan shahadan mutane da dama.

Rahotonni sun bayyana cewa: An hae-haren sun janyo shahadan yara da mata tare da kona gawarwakinsu sakamakon yin luguden makamai masu linzami kan sansanoninsu musamman wadanda suke rayuwa a cikin tantuna a yankin al-Mawasi da ke yammacin Khan Yunis.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

HKI Ta Kashe Falasdinawa 72 A Cikin Gaza A Yua Litinin

Sojojin HKI sun kai falasdinawa akalla 72 ga shahada a safiyar yau Litinin, daga cikinsu har da yara kanana da kuma wadanda suke jiraran a basu taimakon abinci a cibiyoyinsu a cikin Gazzar.

Tashar talabijan ta Presstv a nan Tehran ta bayyana cewa a yau litinin a Gaza sojojin HKI sun kashe Falasdinawa a wurare da dama a gaza. Labarin ya kara da cewa an garzaya da wadanda suka ji ciwo zuwa asbitin Al-Ahli. Bayan haka yahudawan kai kai hare-hare a yankin Zaitun da kuma kasuwar zawiyya.

Labarin ya kara da cewa baba gadaje a Asbitin don haka zaka ga wadanda suka ji ciwon kwance a kasa. Har’ila yau labaran sun bayyana cewa mafi yawan wadanda sojojin yahudawa suka kashe sun kashesu ne a cibiyar bada agajin gaggawa wanda Amurka da HKI suka tsara don kashe mafi yawan adadi da zasu iya kashewa a Gaza, bayan sun hanasu abinci na kimani watanni 3.

A karshen watan mayun de ya gabata ne Amurka tare da yahudawan suka bullo da wannan tarkon don kara kashe Falasdinawa bayan sun hana shigo da abinci yankin.  Suna kashesu ne a dai-dai lokacinda suke cikin tsananin yunwa. Inda ya zama masu dole su je su nemi abinci duk inda yake.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kasar Iran Ta Nuna Ire-Iren Makamai Masu Linzami Da Ta Mayar Da Martani Da Su Kan ‘Yan Mamaya
  • Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Yi Luguden Bama-Bamai Kan Falasdinawa Da Suka Janyo Shahada Da Jikkata
  • Ɗantata: Majalisar Dattawa Ta Ɗage Taron Jin Ra’ayin Jama’a A Arewa maso Yamma
  • Wakilan Kasashen Duniya Da Kungiyoyin Sun Je Ta’aziyya Mutanen Da Suka Yi Shahada A Yakin Iran Da H.K.Isra’ila
  • Isra’ila na bincike kan harin dakarunta da ya kashe fararen hula a Gaza
  • Uwargidar Gwamnan Kaduna Ta Kaddamar Da Rabon Kayan Noma Ga Mata Manoma
  • Laftanar Kanar Shikarci: Sojojin Iran Suna Cikin Shirin Ko-Ta-Kwana Fiye Da Kowane Lokaci
  • Iran Ta Bukaci Gudanar Da Bincike Kan Dalilin Isra’ila Na Kai Harin Kan Gidan Yarin Tehran
  • CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata
  • HKI Ta Kashe Falasdinawa 72 A Cikin Gaza A Yua Litinin