Mutane fiye 300 ne suka mutu a cikin kwanaki a wani kazamin fada a yankin Darfur da ke yammacin kasar Sudan

Hukumar kula da ayyukan jin kai ta Majalisar Dinkin Duniya ta watsa rahoton cewa: Sama da fararen hula 300 ne aka kashe a wani kazamin fada na kwanaki biyu a yankin Darfur na kasar Sudan mai fama da rikici.

Dakarun kai daukin gaggawa na Rapid Support Forces sun kaddamar da hare-hare a ranakun Juma’a da Asabar a kan sansanonin ‘yan gudun hijira biyu da ke fama da matsalar yunwa a arewacin Darfur da kuma babban birnin da ke kusa, inda rahotannin farko suka nuna cewa sama da mutane 100 ne suka mutu, ciki har da yara 20 da ma’aikatan agaji tara, a cewar wani jami’in Majalisar Dinkin Duniya.

A halin da ake ciki kuma, ofishin kula da ayyukan jin kai na Majalisar Dinkin Duniya (OCHA) ya sanar da samun karuwar adadin wadanda suka mutu a ranar Litinin, kamar yadda wasu majiyoyi na cikin gida suka tabbatar da hakan.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Mutane 315 ne suka ɓace bayan hari a makaranta Neja

Shugaban Cocin Katolika reshen Kontagora, ƙarƙashin ya ce ɗalibai 88 da aka yi zaton sun tsere yayin harin da ’yan ta’adda suka kai a makarantar St Mary Secondary School da ke Papiri, ƙaramar hukumar Agwara ta Jihar Neja, har yanzu ba a san inda suke ba.

A cewar majiyoyi, iyaye da dama sun garzaya makarantar domin kwashe ’ya’yansu bayan harin, amma ba ba su yaran ba.

A baya  Aminiya ta ruwaito cewa ’yan bindiga sun kutsa cikin makarantar da daddare a ranar Juma’a, inda suka yi garkuwa da ɗalibai da ma’aikatan makarantar.

Shugaban Cocin Katolika ta Kontagora, Mai Girma Bishop Bulus Dauwa Yohanna, ya sanar ta hannun mai taimaka masa, Daniel Atori, cewa an yi garkuwa da ɗalibai 303, malamai mata huɗu da malamai maza takwas a yayin harin.

Gobara ta lalata gidaje 40 a sansanin ’yan gudun a Borno

Ya ce makarantar na da ɗalibai 430 a ɓangaren firamare, da kuma ɗalibai 199 a ɓangaren sakandare.

Bishop ɗin ya ƙaryata zargin da Sakataran Gwamnatin Jihar Neja ya yi cewa gwamnati ko jami’an tsaro sun yi wa makarantar gargaɗi tun kafin harin.

Ya ce, “Mun tambayi Sakataren Ilimi ko ya samu wata takarda daga gwamnati, ya ce babu; ko an ce ya tura mana wata sanarwa, ma babu. Mun tambaye shi ko an sanar da shi a baki, ya ce a’a. To su faɗa wa duniya wa suka bai wa wannan takarda, ko ta wane hanya aka turo ta?

“Mun kuma tambayar Ƙungiyar Makarantu Masu zaman kansu ta Ƙasa, suma ba su samu wata irin sanarwa ba. Suka ce makarantar an rufe ta kuma an sake buɗe ta kwanaki kaɗan da suka gabata — wannan ma ba gaskiya ba ne. Mu masu bin doka ne,” in ji shi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Mutane 315 ne suka ɓace bayan hari a makaranta Neja
  • Duniyarmu A Yau: Sabon Kuduri Mai Yin Allawadai Da Iran A Hukumat IAEA
  • Wani Tsohon Ma’aikacin CIA Ya Ce HKI Ta Yi Barazanar Amfani Da Makaman Nukliya Kan Iran
  • Zaman Majalisar Amurka Kan Zargin Kisan Kiristoci A Najeriya
  • Ƴan Bindiga Sun Sace Dalibai Mata 25 a Jihar Kebbi 
  • Wayar wutar lantarki ta kashe mutum 4 a wajen cashiya a Legas
  • Babu addinin da ake yi wa kisan ƙare dangi a Binuwai — Gwamna Alia
  • Isra’ila ta kashe akalla Falasdinawa 27 a wani sabon harin bam
  • Sudan ta yaba da kokarin Amurka da Saudiyya na kawo karshen rikicin kasar
  • Tankin ruwa ya kashe mutum 4, wasu sun jikkata a Jigawa