Mutane fiye 300 ne suka mutu a cikin kwanaki a wani kazamin fada a yankin Darfur da ke yammacin kasar Sudan

Hukumar kula da ayyukan jin kai ta Majalisar Dinkin Duniya ta watsa rahoton cewa: Sama da fararen hula 300 ne aka kashe a wani kazamin fada na kwanaki biyu a yankin Darfur na kasar Sudan mai fama da rikici.

Dakarun kai daukin gaggawa na Rapid Support Forces sun kaddamar da hare-hare a ranakun Juma’a da Asabar a kan sansanonin ‘yan gudun hijira biyu da ke fama da matsalar yunwa a arewacin Darfur da kuma babban birnin da ke kusa, inda rahotannin farko suka nuna cewa sama da mutane 100 ne suka mutu, ciki har da yara 20 da ma’aikatan agaji tara, a cewar wani jami’in Majalisar Dinkin Duniya.

A halin da ake ciki kuma, ofishin kula da ayyukan jin kai na Majalisar Dinkin Duniya (OCHA) ya sanar da samun karuwar adadin wadanda suka mutu a ranar Litinin, kamar yadda wasu majiyoyi na cikin gida suka tabbatar da hakan.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

‘Yan Sanda Sun Kama Wani Kasurgumin Barowon Shanu Da Garkuwa Da Mutane A Kasuwar Shinge

Jami’an Sashen Binciken Laifuka na Rundunar ‘Yan Sanda a Jihar Nasarawa (SCID) sun kama wani mai garkuwa da mutane a Kasuwar Shinge da ke Lafia, bisa rahotonnin sirri da suka samu.

An samu nasarar cafke wanda ake zargin bayan shafe dogon lokaci  rundunar na nemasa ruwa a jallo saboda laifuka da dama da suka hada da garkuwa da mutane da kuma satar shanu.

A yayin bincike, wanda ake zargin ya amsa laifinsa, sannan ya jagoranci jami’an tsaro zuwa maboyarsa da ke kauyen Ruwan Baka a karamar hukumar Doma, inda aka samu bindiga kirar AK-49 mai lamba 453144 tare da alburusai.

Wannan nasarar ta biyo bayan kama wata Fatima Salisu a ‘yan kwanakin baya, wadda aka tare tana jigilar makamai daga Doma zuwa Jihar Katsina domin kaiwa miyagu.

Kwamishinan ‘Yan Sanda na Jihar Nasarawa, CP Shattima Jauro Mohammed, ya jaddada kudirin rundunar na ci gaba da yaki da aikata laifuka tare da tabbatar da tsaro ga dukkan mazauna jihar Nasarawa.

Ya bukaci jama’a da su kasance masu lura, tare da bayar da rahoton duk wani motsi ko aikin da ba su yarda da shi ba, domin ‘yan sanda za su ci gaba da aiki tukuru don tabbatar da zaman lafiyar  al’umma.

Aliyu Muraki

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sojojin Sudan Sun Gama Tsarkaka Birnin Khartoum Daga ‘Yan Tawayen Rapid Support Forces
  • An kashe makiyaya 2 a wani hari a Filato
  • Yadda aka kashe dan fashi aka kama wasu 7 a Abuja
  • Shugaban Kasar Colombia: Ayyukan Kasar Sin Sun Nuna Wani Sabon Salo Na Ci Gaban Zamantakewar Al’ummar Bil’adama
  • ‘Yan Sanda Sun Kama Wani Kasurgumin Barowon Shanu Da Garkuwa Da Mutane A Kasuwar Shinge
  • Yankin Taiwan Ba Shi Da Iko Ko Hujjar Halartar Taron WHA
  • Kotu Ta Daure Wasu Mutane 3 Da Ake Zargi Da Kisan Wani Mutum A Gidan Yarin Adamawa
  • ’Yan bindiga sun kashe mutum 3, sun sace 26 a ƙauyukan Zamfara
  • Sharhin Bayan Labarai: Dandalin Tattaunawa Na Tehran
  • Mutane 7 Sun Mutu 11Sun Jikkata A Hadarin Mota A Niger.