An Fara Bada Horo Ga Masu Horas da Mabiyan Bana A Jigawa
Published: 17th, April 2025 GMT
Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Jigawa ta shirya taron horaswa gaa malamai daga dukkan kananan hukumomi 27 domin shirya su, su horar da maniyyata aikin hajjin 2025 na jihar.
Darakta Janar na hukumar Alhaji Ahmed Umar Labbo ya bayyana hakan a yayin wani taron karawa juna sani na kwana daya ga sabbin masu wa’azin aikin hajjin na kananan hukumomi.
Ya ce masu gudanar da aikin, an zabo su ne daga kowace karamar hukuma 27 na jihar domin gudanar da aikin hajjin mai zuwa.
Alhaji Ahmed Umar Labbo ya ce su kuma masu gudanar da aikin za su horas da maniyyatan a cibiyoyin da aka kebe a kananan hukumominsu na jihar.
Ya bayyana cewa, an shirya taron bitar ne domin wayar da kan jami’an ayyukan da gwamnatin jihar ta dora masu aikin.
Ya ce an yi hakan ne domin a tabbatar da horar da alhazan jihar yadda ya kamata kan abubuwan da suka shafi aikin Hajji.
“An umurci masu gudanar da aikin Hajji su horar da mahajjata kan wajibai, rukunan da ka’idojin aikin Hajji a Saudiyya.”
Labbo, ya yi nuni da cewa, tarbiyyar alhazai yadda ya kamata, zai shiryar da su gudanar da aikin Hajji kamar yadda addinin Musulunci ya tanada da kuma zama jakadu nagari na jiha da kasa baki daya.
A cewarsa taron bitar zai baiwa maniyyatan damar sanin ayyukan hajjin da ya dace kuma karbabbe.
Ya kuma bayyana cewa, hukumar za ta nada masu gudanar da aikin a cikin kwamitoci daban-daban domin ganin an samu nasarar gudanar da ayyukan Hajji na shekarar 2025.
Alhaji Ahmed Umar Labbo ya ci gaba da bayanin cewa, a matsayinsu na jagororin alhazai, dole ne su kasance kusa da mahajjata don samun taimako a Najeriya da Saudiyya idan bukatar hakan ta taso.
Yayin da yake tsokaci kan shirye-shiryen, DG ya lura cewa, hukumar ta riga ta tattara tare da mika fasfunan kasa da kasa na maniyyata aikin hajjin na zuwa tsarin biza.
Ya bayyana daukar nauyin malamai daga dukkanin kananan hukumomi 27 na jihar zuwa kasar Saudiyya a matsayin irinsa na farko da gwamnatin jihar ta jigawa ta yi.
Tun da farko, Daraktan wayar da kan jama’a da yada labarai na hukumar Alhaji Abdullahi Aliyu ya yi wa jami’an jawabi a kan ayyukan da suka rataya a wuyansu a lokacin gudanar da aikin hajjin 2025.
Wasu daga cikin mahalarta taron da suka zanta da gidan rediyon Najeriya sun yabawa Gwamna Umar Namadi da Darakta Janar na hukumar Ahmed Umar Labbo bisa amincewa da su na kasancewa cikin jami’an da za su jagoranci alhazan jihar domin gudanar da aikin hajjin nan gaba.
Sun kuma yi kira ga maniyyatan da su ba su hadin kai domin cimma burin da ake so.
USMAN MZ
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Jigawa gudanar da aikin Hajji masu gudanar da aikin su gudanar da aikin Ahmed Umar Labbo
এছাড়াও পড়ুন:
ASUU-SSU Ta Zargi VC Da KaryDokokin Jami’ar Jihar Sakkwato
Ƙungiyar Malaman Jami’o’i ta Nijeriya (ASUU), reshen Jami’ar Jihar Sakkwato (ASUU-SSU), ta zargi Mataimakin Shugaban Jami’ar (Vice-Chancellor) da kin bin umarnin Gwamnan Jihar Sakkwato game da sauke Bursar da ya kai lokacin ritaya.
A cikin wata sanarwa da ta fitar a Sakkwato a ranar Litinin, 8 ga Disamba 2025, ƙungiyar ta ce Gwamna Dr. Ahmed Aliyu Sakkwato, wanda shi ne Visitor na Jami’ar, ya amince da buƙatarsu na tabbatar da bin dokokin Jami’ar ta hanyar amincewa da ritayar Bursar ɗin.
ASUU-SSU ta bayyana cewa Ofishin Shugaban Ma’aikatan Gwamnatin Jihar Sakkwato ya aika da takardar umarni mai lamba HS/ADM/101/VOL-1, ɗauke da kwanan wata 18 ga Nuwamba 2025, wadda ta umurci Bursar ya miƙa ragamar ofis ga jami’in da ya fi kowa girma a sashen Bursary, har sai an naɗa sabon Bursar bisa tanadin dokar Jami’ar Jihar Sakkwato ta 2009.
Sai dai ƙungiyar ta ce kusan wata guda ke nan VC ɗin bai aiwatar da umarnin ba.
Shugaban reshen ASUU-SSU, Kwamared Bello Musa, ya bayyana cewa sun rubuta wa VC takardar tunatarwa da wata takarda ta biyu, amma ba su samu amsa ba.
Haka kuma, sun gudanar da taro biyu da shi, amma ya dage cewa akwai wata amincewa da Ma’aikatar Ilimi Mai Zurfi ta jihar ta bayar a 2024 game da matsayin Bursar.
Sai dai ASUU ta ce wannan hujja “ba ta da tushe”, domin sabon umarnin Gwamna “ya fi ƙarfi kuma ya shafe duk wani tsohon matsayi”, musamman ma ganin cewa Bursar ya kai lokacin ritaya tun 3 ga Oktoba 2024.
A cewarta, Ma’aikatar Kula Da Ma’aikata ta riga ta aika masa da takardar ritaya ta hannun Ma’aikatar Kudi ta jihar.
Ƙungiyar ta ce ci gaba da bari tsohon ma’aikaci ya rattaɓa hannu kan muhimman takardun Jami’a “na karya doka, kuma na tauye ikon Jami’a (University Autonomy).”
ASUU-SSU ta yaba wa Gwamnan jihar bisa “ƙarin nuna biyayya ga doka da buɗe ƙofar sauraron ƙorafe-ƙorafe”, tare da buƙatar ya tabbatar da cewa ba a katse hanyoyin isar da sahihan koke-koke zuwa gare shi ba.
Ƙungiyar ta ce zanga-zangar lumana da ta gudanar a Jami’ar na nufin matsa wa VC lamba ya aiwatar da umarnin Gwamna ba tare da ɓata lokaci ba, domin tabbatar da zaman lafiya da daidaiton aiki.
Ta kuma sha alwashin ɗaukar “mataki mafi tsauri” idan ba a aiwatar da umarnin ba.