Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-11-26@08:23:03 GMT

An Fara Bada Horo Ga Masu Horas da Mabiyan Bana A Jigawa

Published: 17th, April 2025 GMT

An Fara Bada Horo Ga Masu Horas da Mabiyan Bana A Jigawa

Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Jigawa ta shirya taron horaswa gaa malamai daga dukkan kananan hukumomi 27 domin shirya su, su horar da maniyyata aikin hajjin 2025 na jihar.

Darakta Janar na hukumar Alhaji Ahmed Umar Labbo ya bayyana hakan a yayin wani taron karawa juna sani na kwana daya ga sabbin masu wa’azin aikin hajjin na kananan hukumomi.

Ya ce masu gudanar da aikin, an zabo su ne daga kowace karamar hukuma 27 na jihar domin gudanar da aikin hajjin mai zuwa.

Alhaji Ahmed Umar Labbo ya ce su kuma masu gudanar da aikin za su horas da maniyyatan a cibiyoyin da aka kebe a kananan hukumominsu na jihar.

Ya bayyana cewa, an shirya taron bitar ne domin wayar da kan jami’an ayyukan da gwamnatin jihar ta dora masu aikin.

Ya ce an yi hakan ne domin a tabbatar da horar da alhazan jihar yadda ya kamata kan abubuwan da suka shafi aikin Hajji.

“An umurci masu gudanar da aikin Hajji su horar da mahajjata kan wajibai, rukunan da ka’idojin aikin Hajji a Saudiyya.”

Labbo, ya yi nuni da cewa, tarbiyyar alhazai yadda ya kamata, zai shiryar da su gudanar da aikin Hajji kamar yadda addinin Musulunci ya tanada da kuma zama jakadu nagari na jiha da kasa baki daya.

A cewarsa taron bitar zai baiwa maniyyatan damar sanin ayyukan hajjin da ya dace kuma karbabbe.

Ya kuma bayyana cewa, hukumar za ta nada masu gudanar da aikin a cikin kwamitoci daban-daban domin ganin an samu nasarar gudanar da ayyukan Hajji na shekarar 2025.

Alhaji Ahmed Umar Labbo ya ci gaba da bayanin cewa, a matsayinsu na jagororin alhazai, dole ne su kasance kusa da mahajjata don samun taimako a Najeriya da Saudiyya idan bukatar hakan ta taso.

Yayin da yake tsokaci kan shirye-shiryen, DG ya lura cewa, hukumar ta riga ta tattara tare da mika fasfunan kasa da kasa na maniyyata aikin hajjin na zuwa tsarin biza.

Ya bayyana daukar nauyin malamai daga dukkanin kananan hukumomi 27 na jihar zuwa kasar Saudiyya a matsayin irinsa na farko da gwamnatin jihar ta jigawa ta yi.

Tun da farko, Daraktan wayar da kan jama’a da yada labarai na hukumar Alhaji Abdullahi Aliyu ya yi wa jami’an jawabi a kan ayyukan da suka rataya a wuyansu a lokacin gudanar da aikin hajjin 2025.

Wasu daga cikin mahalarta taron da suka zanta da gidan rediyon Najeriya sun yabawa Gwamna Umar Namadi da Darakta Janar na hukumar Ahmed Umar Labbo bisa amincewa da su na kasancewa cikin jami’an da za su jagoranci alhazan jihar domin gudanar da aikin hajjin nan gaba.

Sun kuma yi kira ga maniyyatan da su ba su hadin kai domin cimma burin da ake so.

USMAN MZ

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Jigawa gudanar da aikin Hajji masu gudanar da aikin su gudanar da aikin Ahmed Umar Labbo

এছাড়াও পড়ুন:

Gobarar tankar mai ta ƙone gidaje a Jihar Neja

Wata tankar mai ta yi gobara a wani gudan mai a yankin Tungan-Bunu da ke Ƙaramar Hukumar Rijau a Jihar Neja, lamarin da ya janyo ƙonewar gidaje da kadarori da masu yawa.

Shaidu sun ce gobarar ta tashi ne a lokacin da tankar take shirin sauke mai a ranar Litinin da yamma, inda wutar ta bazu zuwa gidajen da ke kusa.

Duk da cewa babu wanda ya rasa ransa, lamarin ya haifar da firgici inda mazauna yankin suka yi ta tserewa suka bar gidajensu yayin da tankar ke ci da wuta.

Tankar mai ta yi hatsari a hanyar Lapai-Agaie Amurka za ta tallafa wa Nijeriya daƙile matsalar tsaro Mayaƙan Boko Haram sun fille kan mata 2 a Borno

A wani lamari ba daban, wata tankar mai ta kife a kan hanyar Lapai zuwa Agaie, lamarin da ya toshe hanya tare da haddasa cunkoson ababen hawa.

Shaidu sun ce tankar, wadda ke ɗauke da fetur daga Legas zuwa Gombe, ta kife ne da misalin karfe 10 na safe a ranar Litinin bayan jikinta ya rabu da kan motar, ya ƙetare hanya, abin da ya tayar da hankalin jama’a.

Wani mazaunin yankin, Malam Mahmud Abubakar, ya ce jami’an tsaro sun garzaya wajen domin tsare yankin, sannan aka tura ma’aikatan kashe gobara don kauce wa tashin wuta.

Ya ƙara da cewa lamarin ya faru ne a yankin Efu-Nda-Egbo na Ƙaramar Hukumar Lapai, inda ya haddasa cunkoson ababen hawa mai tsanani.

Kokarin tuntuɓar Darakta-Janar na Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta Jihar Neja (NSEMA), Abdullahi Baba Arah, bai yi nasara ba, domin bai amsa kiran wayar da wakilinmu ya yi masa ba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Jigawa Za Ta Yi Wa Yara Miliyan 1.5 Rigakafin Cutar Shan Inna
  • An buɗe wasu makarantu domin ci gaba da jarawaba a Katsina
  • NAJERIYA A YAU: Irin Radadin Da Masu Cutar Amosanin Jini Ke Fuskanta
  • Gobarar tankar mai ta ƙone gidaje a Jihar Neja
  • Gwamna Namadi Ya Kaddamar da Titi Mai Tsawon Kilomita 13 a ‘Yankwashi
  • An rufe duk makarantu a Jihar Bauchi saboda matsalar tsaro
  • Umarnin janye ’yan sanda masu gadin manyan mutane na iya zama zance kawai —Shehu Sani
  • Hukumar Alhazai Ta Jihar Kwara Ta Sanar da Wa’adin Biyan Kudin Aikin Hajjin 2026
  • An rufe duk makarantu a Jihar Bauchi na saboda matsalar tsaro
  • Kungiyoyi Masu Gwagwarmaya Sun Yi Tir Da HKI Saboda Hare-haren Beirut