An Fara Bada Horo Ga Masu Horas da Mabiyan Bana A Jigawa
Published: 17th, April 2025 GMT
Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Jigawa ta shirya taron horaswa gaa malamai daga dukkan kananan hukumomi 27 domin shirya su, su horar da maniyyata aikin hajjin 2025 na jihar.
Darakta Janar na hukumar Alhaji Ahmed Umar Labbo ya bayyana hakan a yayin wani taron karawa juna sani na kwana daya ga sabbin masu wa’azin aikin hajjin na kananan hukumomi.
Ya ce masu gudanar da aikin, an zabo su ne daga kowace karamar hukuma 27 na jihar domin gudanar da aikin hajjin mai zuwa.
Alhaji Ahmed Umar Labbo ya ce su kuma masu gudanar da aikin za su horas da maniyyatan a cibiyoyin da aka kebe a kananan hukumominsu na jihar.
Ya bayyana cewa, an shirya taron bitar ne domin wayar da kan jami’an ayyukan da gwamnatin jihar ta dora masu aikin.
Ya ce an yi hakan ne domin a tabbatar da horar da alhazan jihar yadda ya kamata kan abubuwan da suka shafi aikin Hajji.
“An umurci masu gudanar da aikin Hajji su horar da mahajjata kan wajibai, rukunan da ka’idojin aikin Hajji a Saudiyya.”
Labbo, ya yi nuni da cewa, tarbiyyar alhazai yadda ya kamata, zai shiryar da su gudanar da aikin Hajji kamar yadda addinin Musulunci ya tanada da kuma zama jakadu nagari na jiha da kasa baki daya.
A cewarsa taron bitar zai baiwa maniyyatan damar sanin ayyukan hajjin da ya dace kuma karbabbe.
Ya kuma bayyana cewa, hukumar za ta nada masu gudanar da aikin a cikin kwamitoci daban-daban domin ganin an samu nasarar gudanar da ayyukan Hajji na shekarar 2025.
Alhaji Ahmed Umar Labbo ya ci gaba da bayanin cewa, a matsayinsu na jagororin alhazai, dole ne su kasance kusa da mahajjata don samun taimako a Najeriya da Saudiyya idan bukatar hakan ta taso.
Yayin da yake tsokaci kan shirye-shiryen, DG ya lura cewa, hukumar ta riga ta tattara tare da mika fasfunan kasa da kasa na maniyyata aikin hajjin na zuwa tsarin biza.
Ya bayyana daukar nauyin malamai daga dukkanin kananan hukumomi 27 na jihar zuwa kasar Saudiyya a matsayin irinsa na farko da gwamnatin jihar ta jigawa ta yi.
Tun da farko, Daraktan wayar da kan jama’a da yada labarai na hukumar Alhaji Abdullahi Aliyu ya yi wa jami’an jawabi a kan ayyukan da suka rataya a wuyansu a lokacin gudanar da aikin hajjin 2025.
Wasu daga cikin mahalarta taron da suka zanta da gidan rediyon Najeriya sun yabawa Gwamna Umar Namadi da Darakta Janar na hukumar Ahmed Umar Labbo bisa amincewa da su na kasancewa cikin jami’an da za su jagoranci alhazan jihar domin gudanar da aikin hajjin nan gaba.
Sun kuma yi kira ga maniyyatan da su ba su hadin kai domin cimma burin da ake so.
USMAN MZ
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Jigawa gudanar da aikin Hajji masu gudanar da aikin su gudanar da aikin Ahmed Umar Labbo
এছাড়াও পড়ুন:
’Yan sanda sun gano zinaren N23m bayan shekara 12 da ɓacewarsu a Borno
’Yan sanda sun gano tare da miƙa wa wata mata zinarenta da kuɗinwu ta kai Naira miliyan 23 da suna ɓace a lokacin wani harin Boko Haram shekara 12 da suka gabata a Jihar Borno.
Jami’an tsaro da ke sintiri a kan iyakar Jihar Borno da Nijar ne suka gano kayan zinaren waɗanda suka haɗa da sarƙoƙi da sulallan zinariya a yankin Ƙaramar Hukumar Abadam.
Jami’an Ƙaramar Hukumar ne suka sanar a ranar Asabar a Malam Fatori cewa tsabar zinaren da aka gano, darajarsu ta kai Naira miliyan 23, mallakin wata uwa ce mai ’ya’ya shida.
Matar, wacce ke zaune a gaɓar Tafkin Chadi, ta ce, “A yau ina cike da farin ciki game da gano tsabar zinare na masu daraja da suka ɓace tun 2012, lokacin da ’yan Boko Haram suka ƙona gidaje da shaguna da yawa a cikin al’ummarmu.”
Ta jaddada cewa, “babu daga cikin zinare da aka samu ya ɓace ko ya lalace a lokacin mamayar Malam Fatori da ’yan ta’adda suka yi fiye da nawa.”
Wani babban jami’in Majalisar Ƙaramar Hukumar Abadam da ya sakaya sunansa saboda dalilan tsaro, ya yaba wa ’yan sandan da aka tura don kare rayukan mutane da kadarorinsu a yankin Tafkin Chadi.
Bayan gano tsabar zinare na naira miliyan 23, jami’in ya lura cewa martanin ’yan sanda a ayyukan yaƙi da ta’addanci da ake ci gaba da yi wani abin karfafa gwiwa ne ga sojoji da sauran hukumomin tsaro a yankin Tafkin Chadi, wanda ya ƙunshi qananan hukumomi takwas da ke yankin.