Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-12-10@13:50:13 GMT

An Fara Bada Horo Ga Masu Horas da Mabiyan Bana A Jigawa

Published: 17th, April 2025 GMT

An Fara Bada Horo Ga Masu Horas da Mabiyan Bana A Jigawa

Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Jigawa ta shirya taron horaswa gaa malamai daga dukkan kananan hukumomi 27 domin shirya su, su horar da maniyyata aikin hajjin 2025 na jihar.

Darakta Janar na hukumar Alhaji Ahmed Umar Labbo ya bayyana hakan a yayin wani taron karawa juna sani na kwana daya ga sabbin masu wa’azin aikin hajjin na kananan hukumomi.

Ya ce masu gudanar da aikin, an zabo su ne daga kowace karamar hukuma 27 na jihar domin gudanar da aikin hajjin mai zuwa.

Alhaji Ahmed Umar Labbo ya ce su kuma masu gudanar da aikin za su horas da maniyyatan a cibiyoyin da aka kebe a kananan hukumominsu na jihar.

Ya bayyana cewa, an shirya taron bitar ne domin wayar da kan jami’an ayyukan da gwamnatin jihar ta dora masu aikin.

Ya ce an yi hakan ne domin a tabbatar da horar da alhazan jihar yadda ya kamata kan abubuwan da suka shafi aikin Hajji.

“An umurci masu gudanar da aikin Hajji su horar da mahajjata kan wajibai, rukunan da ka’idojin aikin Hajji a Saudiyya.”

Labbo, ya yi nuni da cewa, tarbiyyar alhazai yadda ya kamata, zai shiryar da su gudanar da aikin Hajji kamar yadda addinin Musulunci ya tanada da kuma zama jakadu nagari na jiha da kasa baki daya.

A cewarsa taron bitar zai baiwa maniyyatan damar sanin ayyukan hajjin da ya dace kuma karbabbe.

Ya kuma bayyana cewa, hukumar za ta nada masu gudanar da aikin a cikin kwamitoci daban-daban domin ganin an samu nasarar gudanar da ayyukan Hajji na shekarar 2025.

Alhaji Ahmed Umar Labbo ya ci gaba da bayanin cewa, a matsayinsu na jagororin alhazai, dole ne su kasance kusa da mahajjata don samun taimako a Najeriya da Saudiyya idan bukatar hakan ta taso.

Yayin da yake tsokaci kan shirye-shiryen, DG ya lura cewa, hukumar ta riga ta tattara tare da mika fasfunan kasa da kasa na maniyyata aikin hajjin na zuwa tsarin biza.

Ya bayyana daukar nauyin malamai daga dukkanin kananan hukumomi 27 na jihar zuwa kasar Saudiyya a matsayin irinsa na farko da gwamnatin jihar ta jigawa ta yi.

Tun da farko, Daraktan wayar da kan jama’a da yada labarai na hukumar Alhaji Abdullahi Aliyu ya yi wa jami’an jawabi a kan ayyukan da suka rataya a wuyansu a lokacin gudanar da aikin hajjin 2025.

Wasu daga cikin mahalarta taron da suka zanta da gidan rediyon Najeriya sun yabawa Gwamna Umar Namadi da Darakta Janar na hukumar Ahmed Umar Labbo bisa amincewa da su na kasancewa cikin jami’an da za su jagoranci alhazan jihar domin gudanar da aikin hajjin nan gaba.

Sun kuma yi kira ga maniyyatan da su ba su hadin kai domin cimma burin da ake so.

USMAN MZ

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Jigawa gudanar da aikin Hajji masu gudanar da aikin su gudanar da aikin Ahmed Umar Labbo

এছাড়াও পড়ুন:

’Yan jaridar Daily Trust da Trust TV sun lashe kyautar binciken ƙwaƙwaf ta Wole Soyinka ta bana

Jaridar Daily Trust da gidan talabijin na Trust TV, dukkansu mallakar kamfanin Media Trust, a bana ma sun sake yin fice bayan ’yan jaridansu suka lashe kyautar binciken kwakwaf ta Wole Soyinka ta bana.

’Yan jaridar na Daily Trust da Trust TV, Afeez Hanafi da Muslim Muhammad Yusuf, sun lashe gasar ne a matsayin zakaru a rukunin rahoton jarida da kuma na talabijin mafi daraja a bana a Najeriya.

Majalisar Dattawa ta amince Tinubu ya tura sojojin Najeriya zuwa Jamhuriyar Benin Sojoji sun kashe ’yan bindiga 13, sun ceto ’yan kasuwa a Sakkwato

Hanafi ya lashe rukuni na rubutu bisa labarinsa mai taken: “Bincike: Dan jarida ya samu ayyuka biyu da takardun bogi na Oluwole.”

Wanda ya zo na biyu da na uku a rukunin na rubutu su ne Kingsley Jeremiah da Ann Godwin, dukkansu daga jaridar The Guardian.

Sai dai kamar yadda aka saba, babu wanda ya lashe kyautar a rukuni na rediyo, kuma babu wanda ya fito a matsayin na biyu ko na uku.

A rukuni na yanar gizo, Theophilus Adeokun na National Record ya lashe gaba ɗaya da labarinsa mai taken: “Dangote, a neman makamashi mai arha, yana zubar da guba cikin kogunan Binuwai.”

Wanda ya yi na biyu shi ne Kunle Adebajo daga HumAngle, yayin da Isah Ismaila, shi ma daga HumAngle din ya zo na uku.

A rukunin hoto kuwa, Elliot Ovadje na jaridar Punch ya fito a matsayin zakara, sannan shi ɗin ne ya sake fitowa a matsayin na biyu da na uku.

A bangaren girmamawa, tsohon Alkalin Kotun Ƙoli, Justice Ayo Salami, ya samu kyautar mai rajin kare hakkin dan Adam, yayin da fitaccen marubuci kuma mawaki, Odia Ofeimun, ya samu kyautar kwarewa a aikin jarida.

Tun kafin gabatar da kyaututtuka, shugabar alkalai ta shekarar 2025, Abigail Ogwezzy‑Ndisika, a jawabinta ta ce an samu shigar da rubuce‑rubuce 180, amma aka tace su zuwa 129.

Ta jaddada abubuwan da aka yi amfani da su wajen tantance kowanne rubutu da suka hada da jarumta, zurfi, daidaito, tasiri da kuma jajircewa ga muradun jama’a.

“Mun yi wannan aikin ne daban‑daban kuma ba tare da katsalandan ba, ta amfani da wasu ka’idoji da suka shafi rufe batutuwan cin hanci, take hakkin ɗan adam, laifuka da ayyukan ɓoye, da kuma kyawawan hanyoyin binciken jarida,” in ji ta.

Marubucin da aka saka wa gasar sunansa kuma mai lambar yabo ta Nobel, Wole Soyinka, ya taya dukkan wadanda suka samu kyautar murna, yana mai gargadin kada su yi sakaci.

“Wasu daga cikin jaruman da za su ceci wannan ƙasa za a same su a cikin kafafen yada labarai. Amma a lokaci guda, dole ne in roƙi kafafen yada labarai su yi dada takatsantsan, su yi bincike mai zurfi kan abin da suke wallafawa. Akwai labarai masu yawa da ake wallafawa da ba daidai ba ne,” in ji shi.

Ya kuma yi kira ga jaridun da su inganta rahotanninsu, yana nuna damuwa kan yawan labaran karyar da ke yawo a kafafen sada zumunta.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Australia ta Fara Aiwhatar da Dokar Hana Yara Amfani da Shafukan Sada Zumunta
  • ’Yan jaridar Daily Trust da Trust TV sun lashe kyautar binciken ƙwaƙwaf ta Wole Soyinka ta bana
  • An Yaba Ma Iyaye Bisa Goyon Bayansu ga Shirin Rigakafin Shan Inna a Karamar Hukumar Ringim
  • Za a Yi wa Yara 194,000 Rigakafin Cutar Shan Inna a Karamar Hukumar Birnin Kudu
  • RSF : Rabin ‘Yan jarida 67 da aka kashe a bana, a Zirin Gaza ne
  • Yara masara zuwa makaranta barazana ne ga kasa — Shettima
  • An dakatar da Shugaban Karamar Hukumar Lafia
  • Gwamnonin Arewa Za Su Zuba Biliyoyin Naira Don Yaki da Matsalar Tsaro
  • ASUU-SSU Ta Zargi VC Da KaryDokokin Jami’ar Jihar Sakkwato
  • Mutum 5 sun rasu sanadin gobara da faɗa wa rijiya a Kano