An Fara Bada Horo Ga Masu Horas da Mabiyan Bana A Jigawa
Published: 17th, April 2025 GMT
Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Jigawa ta shirya taron horaswa gaa malamai daga dukkan kananan hukumomi 27 domin shirya su, su horar da maniyyata aikin hajjin 2025 na jihar.
Darakta Janar na hukumar Alhaji Ahmed Umar Labbo ya bayyana hakan a yayin wani taron karawa juna sani na kwana daya ga sabbin masu wa’azin aikin hajjin na kananan hukumomi.
Ya ce masu gudanar da aikin, an zabo su ne daga kowace karamar hukuma 27 na jihar domin gudanar da aikin hajjin mai zuwa.
Alhaji Ahmed Umar Labbo ya ce su kuma masu gudanar da aikin za su horas da maniyyatan a cibiyoyin da aka kebe a kananan hukumominsu na jihar.
Ya bayyana cewa, an shirya taron bitar ne domin wayar da kan jami’an ayyukan da gwamnatin jihar ta dora masu aikin.
Ya ce an yi hakan ne domin a tabbatar da horar da alhazan jihar yadda ya kamata kan abubuwan da suka shafi aikin Hajji.
“An umurci masu gudanar da aikin Hajji su horar da mahajjata kan wajibai, rukunan da ka’idojin aikin Hajji a Saudiyya.”
Labbo, ya yi nuni da cewa, tarbiyyar alhazai yadda ya kamata, zai shiryar da su gudanar da aikin Hajji kamar yadda addinin Musulunci ya tanada da kuma zama jakadu nagari na jiha da kasa baki daya.
A cewarsa taron bitar zai baiwa maniyyatan damar sanin ayyukan hajjin da ya dace kuma karbabbe.
Ya kuma bayyana cewa, hukumar za ta nada masu gudanar da aikin a cikin kwamitoci daban-daban domin ganin an samu nasarar gudanar da ayyukan Hajji na shekarar 2025.
Alhaji Ahmed Umar Labbo ya ci gaba da bayanin cewa, a matsayinsu na jagororin alhazai, dole ne su kasance kusa da mahajjata don samun taimako a Najeriya da Saudiyya idan bukatar hakan ta taso.
Yayin da yake tsokaci kan shirye-shiryen, DG ya lura cewa, hukumar ta riga ta tattara tare da mika fasfunan kasa da kasa na maniyyata aikin hajjin na zuwa tsarin biza.
Ya bayyana daukar nauyin malamai daga dukkanin kananan hukumomi 27 na jihar zuwa kasar Saudiyya a matsayin irinsa na farko da gwamnatin jihar ta jigawa ta yi.
Tun da farko, Daraktan wayar da kan jama’a da yada labarai na hukumar Alhaji Abdullahi Aliyu ya yi wa jami’an jawabi a kan ayyukan da suka rataya a wuyansu a lokacin gudanar da aikin hajjin 2025.
Wasu daga cikin mahalarta taron da suka zanta da gidan rediyon Najeriya sun yabawa Gwamna Umar Namadi da Darakta Janar na hukumar Ahmed Umar Labbo bisa amincewa da su na kasancewa cikin jami’an da za su jagoranci alhazan jihar domin gudanar da aikin hajjin nan gaba.
Sun kuma yi kira ga maniyyatan da su ba su hadin kai domin cimma burin da ake so.
USMAN MZ
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Jigawa gudanar da aikin Hajji masu gudanar da aikin su gudanar da aikin Ahmed Umar Labbo
এছাড়াও পড়ুন:
Karamar Hukumar Maru Ta Bukaci A Dauki Matakan Kariya Kan Cutar Kwalaraci
Shugaban Karamar Hukumar Maru ta Jihar Zamfara, Alhaji Bello Mohammed Jabaka, ya yi kira ga al’ummar yankin da su dauki matakan kariya domin dakile yaduwar cutar kwalara da sauran cututtukan da ke yaduwa cikin sauri a yankin.
Ya yi wannan kiran ne yayin da yake zantawa da manema labarai a Gusau, babban birnin jihar, kan matakan da hukumar ta dauka domin dakile barkewar cutar ta amai da gudawa a wasu sassan karamar hukumar.
Alhaji Jabaka ya jaddada muhimmancin tsaftar muhalli, musamman wajen tsaftace rijiyoyi da sauran hanyoyin samun ruwan sha, wuraren da ake dafa abinci, da kuma tsaftace muhalli gaba daya, tare da tsaftar jiki wanda ya ce shi ne mabuɗin hana yaduwar cutar ta kwalara.
A cewarsa, kwalara cuta ce da za ta iya bulla a ko ina, don haka ya zama wajibi al’umma su kasance cikin shiri da lura.
Yayin da yake bayani kan halin da aka shiga, ya ce ya gaggauta bayar da umarni ga jami’an lafiya da su dauki wadanda cutar ta shafa zuwa asibitoci domin samun kulawar gaggawa kyauta.
A cewar shugaban karamar hukumar, an samu rahoton mutane sama da 27 da suka kamu da cutar, dukkaninsu kuma sun warke sun koma gida lafiya.
Ya kara da cewa duk wasu sabbin lamurra na bullar cutar an rika ba da kulawa kyauta ba tare da wata matsala ba.
“Zuwo yanzu, babu rahoton mutuwar kowa sakamakon cutar,” in ji shi.
Alhaji Jabaka ya bayyana cewa karamar hukumar ta samu wadatattun magunguna wadanda aka raba su a cibiyoyin lafiya daban-daban domin ci gaba da kula da duk wani sabon lamari na bullar cutar kyauta.
Game da matsalar tsaro a karamar hukumar Maru kuwa, shugaban karamar hukumar ya bayyana cewa ya bayar da umarnin a rika karanta Alkur’ani mai girma a kowace Juma’a da fatan Allah a kawo karshen matsalolin tsaro da suka dade suna addabar yankin.
Ya bayyana fatansa na cewa addu’o’in za su taimaka wa jami’an tsaro wajen yaki da ‘yan bindiga tare da dawo da zaman lafiya a yankunan da lamarin ya shafa.
Alhaji Jabaka ya kuma yaba wa Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, bisa ayyukan raya kasa daban-daban da ya aiwatar a karamar hukumar Maru, musamman gyaran Asibitin Gaba Daya, gina tituna da sauran ayyukan gine-gine.
Ya tabbatar wa da gwamnan da cikakken goyon baya da hadin kan al’ummar Maru domin cigaban Jihar Zamfara.
Daga Aminu Dalhatu