Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-12-02@05:07:19 GMT

An Fara Bada Horo Ga Masu Horas da Mabiyan Bana A Jigawa

Published: 17th, April 2025 GMT

An Fara Bada Horo Ga Masu Horas da Mabiyan Bana A Jigawa

Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Jigawa ta shirya taron horaswa gaa malamai daga dukkan kananan hukumomi 27 domin shirya su, su horar da maniyyata aikin hajjin 2025 na jihar.

Darakta Janar na hukumar Alhaji Ahmed Umar Labbo ya bayyana hakan a yayin wani taron karawa juna sani na kwana daya ga sabbin masu wa’azin aikin hajjin na kananan hukumomi.

Ya ce masu gudanar da aikin, an zabo su ne daga kowace karamar hukuma 27 na jihar domin gudanar da aikin hajjin mai zuwa.

Alhaji Ahmed Umar Labbo ya ce su kuma masu gudanar da aikin za su horas da maniyyatan a cibiyoyin da aka kebe a kananan hukumominsu na jihar.

Ya bayyana cewa, an shirya taron bitar ne domin wayar da kan jami’an ayyukan da gwamnatin jihar ta dora masu aikin.

Ya ce an yi hakan ne domin a tabbatar da horar da alhazan jihar yadda ya kamata kan abubuwan da suka shafi aikin Hajji.

“An umurci masu gudanar da aikin Hajji su horar da mahajjata kan wajibai, rukunan da ka’idojin aikin Hajji a Saudiyya.”

Labbo, ya yi nuni da cewa, tarbiyyar alhazai yadda ya kamata, zai shiryar da su gudanar da aikin Hajji kamar yadda addinin Musulunci ya tanada da kuma zama jakadu nagari na jiha da kasa baki daya.

A cewarsa taron bitar zai baiwa maniyyatan damar sanin ayyukan hajjin da ya dace kuma karbabbe.

Ya kuma bayyana cewa, hukumar za ta nada masu gudanar da aikin a cikin kwamitoci daban-daban domin ganin an samu nasarar gudanar da ayyukan Hajji na shekarar 2025.

Alhaji Ahmed Umar Labbo ya ci gaba da bayanin cewa, a matsayinsu na jagororin alhazai, dole ne su kasance kusa da mahajjata don samun taimako a Najeriya da Saudiyya idan bukatar hakan ta taso.

Yayin da yake tsokaci kan shirye-shiryen, DG ya lura cewa, hukumar ta riga ta tattara tare da mika fasfunan kasa da kasa na maniyyata aikin hajjin na zuwa tsarin biza.

Ya bayyana daukar nauyin malamai daga dukkanin kananan hukumomi 27 na jihar zuwa kasar Saudiyya a matsayin irinsa na farko da gwamnatin jihar ta jigawa ta yi.

Tun da farko, Daraktan wayar da kan jama’a da yada labarai na hukumar Alhaji Abdullahi Aliyu ya yi wa jami’an jawabi a kan ayyukan da suka rataya a wuyansu a lokacin gudanar da aikin hajjin 2025.

Wasu daga cikin mahalarta taron da suka zanta da gidan rediyon Najeriya sun yabawa Gwamna Umar Namadi da Darakta Janar na hukumar Ahmed Umar Labbo bisa amincewa da su na kasancewa cikin jami’an da za su jagoranci alhazan jihar domin gudanar da aikin hajjin nan gaba.

Sun kuma yi kira ga maniyyatan da su ba su hadin kai domin cimma burin da ake so.

USMAN MZ

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Jigawa gudanar da aikin Hajji masu gudanar da aikin su gudanar da aikin Ahmed Umar Labbo

এছাড়াও পড়ুন:

Yadda ’yan mata ke kufancewa da kasuwancin fara a Kano

A baya, samun fara da yawa a shekara abin tsoro ne ga kowa, dalilin ɗab’arta ta lalata amfanin gona, sai dai a yanzu ta zamo hanyar samun abincin mutanen da dama, musamman ma mata a Jihar Kano.

Duk da cewa a baya ma akwai tsirarun mutane da ke cin fara dace kuma halaccin cin ta a Musulunce, masu ƙyamar ta sun fi yawa, har ma wasu ke ganin masu cin ta za su iya cin kyankyaso.

Sai dai a yanzu wannan ɗabi’a ta kusa zama tarihi, saboda fara ta zamo abincin taɓaka-lashe ba ga mata kaɗai ba da aka saba gani a baya, har ma da maza da masu kuɗi, inda ake mata mazubi na musamman da tsarabe-tsarabe, har ake sayarwa a manyan shaguna da ma ƙasashen waje.

Farar da ake kawowa daga Nijar ba ta wadatarwa —Ɗan kasuwa

Wani dattijo da ya shafe shekaru da dama yana cinikin busasshiya da ɗanyar fara a Kasuwar Rimi da ke Kano, Malam Muhammad Bello ya bayyana wa Aminiya cewa, sana’ar fara ta yi farin jinin da a Kano yanzu wacce ake shigo da ita daga Nijar ba ta wadatar da masu saye.

Ya ce, ‘‘shekarun baya mu biyar ne kaɗai ke kawo fara Kasuwar Rimi daga Nijar da Maigatari da ke Jigawa. Amma yanzu saboda an samu ƙarin masu sayen ta, sai mun dangana da jihohin Bauchi da Yobe da garin Maiduguri da kuma Katsina, kuma masu sayarwar ma ko’ina ga su nan a Kano.

“Kuma wani abin ban sha’awa shi ne da Nijar muke zuwa mu sayo, amma yanzu su ma gurinmu suke zuwa nema, saboda tasu ta yi ƙaranci ga kuma mutane na nema. Dalili shi ne mutane da ba su fahimci arzikin da yake cikin sana’ar ba, yanzu sun fahimta.

“Kin ga a da, ina sayar da kwano 10-20 na fara a rana, amma yanzu sai na sayar da buhu 20-30 a rana ɗaya, ranar da ba kasuwa kuma buhu biyu zuwa uku. Don abin da ma ya sanya na fora fana kan sana’ar ke nan. Ga rumfarsa can, saboda yadda ake sayan fara yanzu ko kayan ƙamshin da ake zubawa a abinci ba a sayensu haka. Kuma a haka ma sanyi bai yi nisa ba.

Nau’in farar da aka fi sayarwa a kasuwa

Malam Bello ya ce, duk da fara a duniya kala-kala ce, a Kano kala uku aka fi sayarwa, waɗanda launinsu da lokacin da aka fi samun su ne ke bambanta su.

Akwai wacce ta fi kowacce girma mai launin ja da maiƙo-maiƙo da muke kira da Zanka, ita sai sanyi ya yi nisa sosai take zuwa. Ta fi kowacce nau’in fara farin jini, saboda maiƙonta da ya sa ba ta buƙatar mai sosai a wajen suya.

Sannan akwai Babe wacce launin ƙasa-ƙasa ce ita ba ta kai Zanka ba, kuma yanzu ne lokacinta, wato farkon sanyi.

Sai kuma Kwarsaye ita da damina take zuwa, kuma duk ta fi sauran ƙanƙanta.

Dalilin da muke son fara — Matasa

Aminiya ta gana da wasu matasa, musamman maza a Kano, kan ko mene ne dalilin da ya sa yanzu suke cin fara babu ƙaƙƙautawa?

Malam Musbahu Inuwa ya ce, a da ƙyanƙyamin fara yake sosai, domin ko gida ya je, ya ga suna soya fara ya daina cin abincinsu.

‘‘Abin da ya sa na fara cin fara budurwata ce ta saya, ta ba ni kyauta, ta ce idan ban ci ba, za ta rabu da ni. Son da nake mata ne ya sa na cije, na ci cinya ɗaya. Duk da haka dai ban saki jiki na ci ba sai da na ji wani likita a rediyo na faɗar amfaninta. Yanzu haka a ɗakina akwai wani ƙaramin farin bokiti cike da ita, ita muke ci muna kallon ƙwallo da abokaina.”

Shi kuwa Halliru Yusha’u da aka fi sani da Messi cewa ya yi, kafar sada zumunta ce ta sanya shi fara cin fara.

Ita ma wata mai suna Zahra’u ta ce, ta fi shekara 10 tana cin fara, kuma ba ta taɓa yin da na sani ba.

‘‘Amma gaskiya ni kai da cinya kafai nake iya ci, saboda fargabar ko maganin ƙwari da ake fesa musu sannan a busar a kawo mana nan”, in ji ta.

Yadda mata suka zamanantar da kasuwacin fara

Wata matashiya mai suna Aisha Adamu ta ce, daga tsokanar ƙawayenta a shafin WhatsApp ta fara cinikinta ta kafar sada zumunta.

‘‘Ba na mantawa ranar 10 ga watan Disambar 2019 na fara sayar da fara da sunan Kamfanin AyeeshFries da kuma Crunchy Fara, amma da tsokana.

“Na sanya hoton soyayyiyar fara a status ɗina sai kawai mutane suka fara tambaya ta farashi. Sai wasu ƙawayena biyu suka ba ni shawarar na fara sayarwa, kuma babu izinina suka fara ɗorawa a nasu status ɗin suna min talla. Da haka na fara.

“Na fara da Naira dubu 3 ne, sai na sayi madaidatan robobi na zuba a ciki, a sati sai na sayar da robobi 10. A lokacin ma Naira fari 5 ne farashin. Da kasuwa ta fara kankama kuma kan ka ce wannan, sai na fara cinikin robobi 60 a sati.

“Wannan harkar ina jin dafinta, ta yadda a kafar sada zumunta na samu kwastamomi daga ƙasashen waje irin su Dubai da Habasha da Azerbaijan Birtaniya da Amurka (musamman Birnin Washington) da Sudan da ma Nijar maƙwabciyarmu.”

Sarrafa fara daidai da zamani

A da akan wanke ta da ruwa sannan a shanya ta bushe a kuma bafa mata yaji, amma yanzu akan tafasa sai suya. Kuma yanayin suyar kala biyu ne ba kamar na baya ba.

Wasu kan soya ta da mai kaɗan (Gentle frying) ko a soya ta mai ya sha kanta (Deep frying).

Baya ga suyar ma, zamani ya sanya wasu suna ci da miyar barkono (Pepper Sauce), wasu ma har da su hafin kabeji na zamani.

Sai dai Aisha ta ce, an fi cinikin soyayya da aka baɗe da yaji saboda takan yi wata biyu ba ta yi komai ba.

Fara na ƙara ƙarfin garkuwar jiki — Masani

Ƙwarrare a harkar abinci, Malam Auwal Musa Umar ya ce, baya ga daɗinta a baki, fara na da abubuwa da dama da ke taimakon lafiyar jikin ɗan-adam.

Fara taɓa-ka-lashe ce da za iya cewa mutane sun maye gurbin kaza naman sa da kifi da sauran dabbobin ruwa da ita.

Ta ƙunshi sinadaran Protein da Fat waɗanda ke gina jiki da kuma taimaka masa wajen samun ƙarfin gudanar da ayyuka.

Haka kuma tana da sinadarin Zinc, wanda yake taimaka wa garkuwar jikin fan-adam da Calcium wanda ke ƙara wa ƙasusuwa da haƙora ƙarfi da sauran abubuwan inganta lafiya da dama.

Amma fa duk da haka tana da nata matsalolin da take haifarwa idan aka fiye ci.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • MAAUN: Ƙungiyar iyaye ta musanta zargin ƙara ƙudin yaye ɗalibai a jami’ar
  • ’Yan sanda sun gano zinaren N23m bayan shekara 12 da ɓacewarsu a Borno
  • Gwamnatin Kano Ta Kara Jaddada Dokar Haramcin Yin Haya da Babur a Jihar
  • ’Yan bindiga sun sace fasto da matarsa  masu ibada a Kogi 
  • Jihar Jigawa Ta Mayar da Rarar Kudi Sama da Naira Miliyan 50 Ga Maniyyatan Aikin Hajjin 2026
  • Mutum 6 sun jikkata a rikici manoma da makiyaya a Jigawa
  • Likitoci sun gindaya sabon sharaɗi bayan janye yajin aiki
  • Trump Ya Bada Sanarwan Rufe Sararin Samaniyar Kasar Venezuela Gaba Daya
  • Yadda ’yan mata ke kuɗancewa da kasuwancin fara a Kano
  • Yadda ’yan mata ke kufancewa da kasuwancin fara a Kano