Aminiya:
2025-12-14@04:34:21 GMT

Najeriya da gwamnatin sojin Nijar da Nijar sun sasanta

Published: 17th, April 2025 GMT

Gwmanatin Sojin Nijar ta sanar da cewa sun sasanta da Gwmanatin Najeriya.

Hakan ta faru ne bayan ziyarar aiki da Ministan Harkokin Wajen Najeriya, Yusuf Tuggar ya kai birnin Yamai, fadar gwamnatin Nijar.

Bayan sanya hannu kan takardar, Ministan Harkokin Wajen Nijar, Bakary You Sangare, ya bayyana cewa, “da ma Najeriya ’yan uwanmu ne, duk wanda ya ce zai raba  Nijar da Najeriya, shi da kansa ya san ba gaskiya ba ne, abu ne na Allah.

Allah Ne Ya haɗa wannan zumunta ka, babu wanda ya isa ya raba ta.”

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: gwamnatin sojin Nijar Najeriya Nijar Tuggar Yamai

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Jigawa Ta Amince da Sama da Naira Biliyan 2.6 Domin Aikin Hajjin 2026

Daga Usman Muhammad Zaria 

Gwamnatin Jihar Jigawa ta amince da kashe sama da naira biliyan 2.6 domin gudanar da ayyukan Hajjin shekarar 2026.

Kwamishinan Yada Labarai, Matasa, Wasanni da Al’adu na jihar, Alhaji Sagir Musa Ahmed ne ya bayyana hakan jim kadan bayan kammala taron Majalisar Zartarwa ta Jiha da aka gudanar a gidan gwamnati da ke Dutse, babban birnin jihar.

A cewarsa, majalisar ta amince da kashe sama da naira biliyan 2 da miliyan 651 domin ayyukan Hajjin 2026, biyo bayan gabatar da bukatar da Sakataren Gwamnatin Jihar (SSG) ya yi.

Alhaji Sagir Musa Ahmed ya ce za a yi amfani da kudaden ne a bangarorin sufuri da jijigilaAlhazai, jin dadinsu, ayyukan lafiya da kuma shirye-shiryen gudanarwa.

Sauran bangarorin sun hada da duk wasu muhimman abubuwa da za su tabbatar da ingantaccen tsari da nasarar aikin Hajji ga Alhazan jihar Jigawa.

Kwamishinan ya kara da cewa, majalisar ta kuma amince da kashe sama da Naira Biliyan 1 da Miliyan 300 domin tallafin karatu (bursary) ga dalibai 19,716 da aka tantance kwanan nan.

Ya bayyana cewa daga cikin adadin, akwai dalibai maza 12,638,  da mata 7,088 da ke karatu a manyan makarantu 77.

Ya ce wannan tallafi zai taimaka wajen bunkasa harkar ilimi, rage nauyin kudi a kan iyaye da iyalai, tare da karfafa gwiwar dalibai su yi fice a karatunsu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yadda Rashin Bincike Ke Haifar Da Yawaitar Mutuwar Aure
  • Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan(a) 170
  • Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan(a) 169
  • Farfesa na Farko a fannin Ilimi a Arewa, Adamu Baikie, ya rasu yana da shekara 94
  • Gwamnatin Jigawa Ta Amince da Sama da Naira Biliyan 2.6 Domin Aikin Hajjin 2026
  • Duniyarmu A Yau: Iran Da Amurka A Yakin Kwanaki 12 Wa Ya Sami Nasara
  • Dan sanda ya yi batan dabo a bakin aikinsa a Katsina
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Amince Ya Ziyarci Beirut
  • EFCC ta tsare tsohon ministan ƙwadago, Chris Ngige
  • Ghana ta yi Allah wadai da cin mutuncin ‘yan kasarta da ke balaguro a Isra’ila