Najeriya da gwamnatin sojin Nijar da Nijar sun sasanta
Published: 17th, April 2025 GMT
Gwmanatin Sojin Nijar ta sanar da cewa sun sasanta da Gwmanatin Najeriya.
Hakan ta faru ne bayan ziyarar aiki da Ministan Harkokin Wajen Najeriya, Yusuf Tuggar ya kai birnin Yamai, fadar gwamnatin Nijar.
Bayan sanya hannu kan takardar, Ministan Harkokin Wajen Nijar, Bakary You Sangare, ya bayyana cewa, “da ma Najeriya ’yan uwanmu ne, duk wanda ya ce zai raba Nijar da Najeriya, shi da kansa ya san ba gaskiya ba ne, abu ne na Allah.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: gwamnatin sojin Nijar Najeriya Nijar Tuggar Yamai
এছাড়াও পড়ুন:
Makusantan Gwamnatin Buhari da suka shiga haɗakar ADC
Kusoshin gwamnatin tsohon Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari sun shiga haɗakar jam’iyyun adawa ta ADC da nufin kayar da Gwamnatin Shugaba Bola Tinubu ta APC.
Tsofaffin mukarraban gwamnatin Buhari da suka koma haɗakar ADC sun haɗa da tsofaffin ministoci da tsofaffin gwamnoni da masu muƙaman siyasa.
Yawanci sun raba gari da APC ne saboda zargin an yi musu rashin adalci a jam’iyyar da kuma gazawar Gwamnatin Tinubu wajen magance matsalolin da ke ci wa ’yan Najeriya tuwo a ƙwarya.
1- Nasiru El-RufaiTsohon Gwamnan Jihar Kaduna Nasir El-Rufai na gaba ne a tafiyar haɗakar inda tun farko ya lashi takobin ƙalubalantar gwamnatin Tinubu a zaɓen 2027.
NAJERIYA A YAU: Shin Ko Hadakar Sabuwar Jamiyyar ADC Za Ta Fidda Wa ‘Yan Najeriya Kitse Daga Wuta? Rasha ta amince da gwamnatin Taliban a AfghanistanFara maganar haɗakar ke da wuya aka ga El-Rufai a gidan Buhari da ke Kaduna, inda ya sanar da ficewarsa daga APC.
Daga bisani El-Rufai tare da tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa Atiku Abubakar da wasu jaga-jigan ’yan APC a gwamnatin Buhari suka ziyarci shugaba kasan.
An yi zargin sun je ne domin neman albarkarsa domin ya amince wa ’yan tsohuwar jam’iyyarsa ta CPC su fice daga APC su shiga haɗakar.
2- Abubakar MalamiMinistan Shari’a a wa’adi biyu da Buhari ya yi, ya sanar da ficewarsa daga APC da kuma aniyarsu ta yaƙar Gwamnatin Tinubu a zaɓen 2027 saboda ta jefa ’yan Najeriya cikin halin ƙaƙa-ni-ka-yi da kuma gaza magance matsalolin tsaro da na tattalin arziki.
Tsohon ministan shari’an, kuma wanda tsohon wanda a baya ya nemi takarar Gwamnan Jihar Kebbi, an lura ya yi baya-baya a harkokin APC tun bayan hawan mulkin Tinubu.
3- Hadi SirikaTsohon Ministan Sufurin Jiragen Sama a zamanin Buhari, dan asalin Jihar Katsina ne, wato mahaifar tsohon shugaban ƙasan.
Hadi Siriya sun jima da taba da raba gari da Gwamnatin Tinubu kuma a halin yanzu yana fuskantar shari’a kan zargin karkatar da kuɗaɗen kwangila da sauran zarge-zarge a ma’aikatar sufurin jiragen sama.
4- Rotimi AmaechiTsohon Ministan Sufuri a zamanin Buhari, kuma tsohon Gwamnan Jihar Ribas, Rotimi Amaechi, ya bayyana aniyarsa ta fitowa takarar shugaban ƙasa a ADC.
Amaechi kamar takwarorinsa da suka fice daga APC bisa zargin an yi musu ba daidai ba, na zargin gwamnatin Tinubu da gazawa.
5- Rauf AregbesolaTsohon Gwamnan Jihar Osun wanda Buhari ya naɗa Ministan Harkokin Cikin Gida, tsohon na hannun daman Tinubu ne.
A halin yanzu shi ne ADC ta nada a matsayin Sakataren Jam’iyya.
6- Solomon DalungTsohon Ministan Wasanni ya daga cikin waɗanda suka shiga wannan haɗaka ta ADC.
Ko da yake wa’adi daya kadai Dalung ya yi minista a zamanin Buhari, ida gaba bisani ya koma sukan kamun ludayin gwamnatin.
Bayan shafe watanni ana tattaunawa kan haɗakar jam’iyyun adawar ne dai a ranar Laraba suka ƙaddamar da shugabannin riƙo a ƙarƙashin jagorancin tsohon Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata David Mark.
Haka kuma sun naɗa tsohon Gwamnan Jihar Osun, Rauf Aregbesola a matsayin sakataren riko na ƙasa.