Najeriya da gwamnatin sojin Nijar da Nijar sun sasanta
Published: 17th, April 2025 GMT
Gwmanatin Sojin Nijar ta sanar da cewa sun sasanta da Gwmanatin Najeriya.
Hakan ta faru ne bayan ziyarar aiki da Ministan Harkokin Wajen Najeriya, Yusuf Tuggar ya kai birnin Yamai, fadar gwamnatin Nijar.
Bayan sanya hannu kan takardar, Ministan Harkokin Wajen Nijar, Bakary You Sangare, ya bayyana cewa, “da ma Najeriya ’yan uwanmu ne, duk wanda ya ce zai raba Nijar da Najeriya, shi da kansa ya san ba gaskiya ba ne, abu ne na Allah.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: gwamnatin sojin Nijar Najeriya Nijar Tuggar Yamai
এছাড়াও পড়ুন:
12 ga Yuni: Najeriya na bikin ranar dimokuraɗiyya
A yau ne Najeriya ke bikin ranar Dimokuraɗiyya, wanda masana siyasa a ciki da wajen ƙasar ke jinjina kan yadda aka kwashe shekara 26 kan tafarkin mulkin farar hula.
Najeriya, ta kasance ƙasa mafi yawan al’umma a Nahiyar Afirka inda ake bikin murnar ranar dimokuraɗiyyar domin tunawa da zaɓen 12 ga watan Yuni wanda ake ganin shi ne zaɓe mafi inganci da aka taɓa gudanarwa a Najeriya.
NAJERIYA A YAU: 12 Ga Yuni: Me Ranar Dimokuraɗiyya Ke Nufi Ga Talakan Najeriya? An kashe jaririn wata 9 da wasu 3 a FilatoHakan dai na zuwa ne duk kuwa da cewa an soke zaɓen, lamarin da ya haifar da taƙaddama da ruɗani game da zaɓen.
Tsohon shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ne ya sauya bikin ranar dimokuradiyyar daga 29 ga watan Mayu zuwa 12 ga watan Yuni domin karrama wanda ake da yaƙinin shi ne ya lashe zaɓen shugaban ƙasar na 1993, wato Moshood Abiola.
Hakan dai na nufin Najeriya ta kwashe shekara 26 tana kan tafarkin mulkin farar hula dimukuraɗiyya ba tare da katsalandan na sojoji ba.