Aminiya:
2025-12-12@22:45:24 GMT

Najeriya da gwamnatin sojin Nijar da Nijar sun sasanta

Published: 17th, April 2025 GMT

Gwmanatin Sojin Nijar ta sanar da cewa sun sasanta da Gwmanatin Najeriya.

Hakan ta faru ne bayan ziyarar aiki da Ministan Harkokin Wajen Najeriya, Yusuf Tuggar ya kai birnin Yamai, fadar gwamnatin Nijar.

Bayan sanya hannu kan takardar, Ministan Harkokin Wajen Nijar, Bakary You Sangare, ya bayyana cewa, “da ma Najeriya ’yan uwanmu ne, duk wanda ya ce zai raba  Nijar da Najeriya, shi da kansa ya san ba gaskiya ba ne, abu ne na Allah.

Allah Ne Ya haɗa wannan zumunta ka, babu wanda ya isa ya raba ta.”

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: gwamnatin sojin Nijar Najeriya Nijar Tuggar Yamai

এছাড়াও পড়ুন:

Dalibin jami’a ya rasu a hatsarin motar murnar kammala jarabawa

Wani dalibin shekarar ƙarshe a Jami’ar Ambrose Alli da ke jihar Edo, ya mutu a wani hatsarin mota bayan shi da wasu dalibai sun yi jerin gwanon motoci domin murnar kammala jarabawar ƙarshe.

Aminiya ta samu labari a ranar Talata daga wani mai amfani da Facebook mai suna Inside Edo, cewa hatsarin ya faru ne a ranar Litinin jim kaɗan bayan daliban sun gama jarabawar ƙarshe. Sai dai ba a bayyana sunan dalibin ba.

DAGA LARABA: Ko Ziyarar Tawagar Amurka Za Ta Kawo Karshen Matsalar Tsaro A Najeriya? Iya sojojin da ke tsaron Seyi Tinubu sun isa su samar da tsaro a Benin – Soyinka

Majiyar ta ce motar ta yi ƙoƙarin wuce wata mota kafin ta kwace ta kuma daki wata babbar mota.

A cewar majiyar: “Wani mummunan hatsari ya faru a Ujoelen, kusa da makarantar firamare, wanda ya yi sanadiyyar mutuwar wani dalibi da ya kammala karatu a jami’ar Ambrose Alli, Ekpoma.

“A cewar masu gani da ido, hatsarin ya faru ne yayin da aka yi yunƙurin wucewa da ɗaya daga cikin motocin da abin ya shafa.

“Wannan haɗarin ya jawo rasa iko, wanda ya haifar da mutuwar. Mazauna yankin da ke kusa sun ruga wurin, amma ba a iya ceto wanda ya jikkata ba.”

Haka kuma, Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya (NAN) ya rawaito cewa daliban sun kasance suna tukin mota cikin ganganci kafin su yi taho-mu-gama da wata babbar mota da ta tsaya a hanya.

An ce wanda ya rasu yana cikin jerin gwanon motocin da daliban da suka kammala karatu suka yi.

NAN ta ruwaito: “An ce yana cikin jerin gwanon sabbin daliban da suka shiga kan hanya a ranar Litinin jim kaɗan bayan bikin kammala makaranta.

“Lamarin ya faru ne lokacin da wanda ya rasu ya yi yunƙurin wuce wata babbar mota mai tafiya, amma ya buge da wata mota da ta tsaya a gefen hanya.”

Ƙoƙarin samun martani daga kwamandan sashe na jihar Edo a Hukumar Kiyaye Hadura ta Ƙasa (FRSC), Cyril Mathew, ya ci tura, domin lambar ba ta shiga har zuwa lokacin hada wannan rahoton.

Sai dai NAN ya rawaito daga baya Mathew ya tabbatar da lamarin, yana mai cewa mutum ɗaya ya mutu yayin da wasu biyar suka jikkata a hatsarin.

Ya ce: “Daliban, bayan sun gama rubuta takardar jarabawa ta ƙarshe, sun shiga hanya cikin jerin gwanon motoci.

“A cikin wannan yanayi, ɗaya daga cikinsu ya yi yunƙurin wuce wata mota, ya kuma buge da wata babbar mota da ta tsaya a gefen hanya,” kamar yadda NAN ya rawaito daga Mathew.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Jigawa Ta Amince da Sama da Naira Biliyan 2.6 Domin Aikin Hajjin 2026
  • Duniyarmu A Yau: Iran Da Amurka A Yakin Kwanaki 12 Wa Ya Sami Nasara
  • Dan sanda ya yi batan dabo a bakin aikinsa a Katsina
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Amince Ya Ziyarci Beirut
  • EFCC ta tsare tsohon ministan ƙwadago, Chris Ngige
  • Ghana ta yi Allah wadai da cin mutuncin ‘yan kasarta da ke balaguro a Isra’ila
  • Kisan Zariya: Na bar Buhari da Allah — Sheikh El-Zakzaky
  • Karamar Hukumar Agwara ta Jinjinawa Gwamnati Bisa Tabbatar da Tsaron Rayuka da Dukiyoyin Jama’a
  • Najeriya da Saudiyya sun rattaba hannu kan yarjejeniyar samar da tsaro
  • Dalibin jami’a ya rasu a hatsarin motar murnar kammala jarabawa