Aminiya:
2025-11-15@09:08:32 GMT

Najeriya da gwamnatin sojin Nijar da Nijar sun sasanta

Published: 17th, April 2025 GMT

Gwmanatin Sojin Nijar ta sanar da cewa sun sasanta da Gwmanatin Najeriya.

Hakan ta faru ne bayan ziyarar aiki da Ministan Harkokin Wajen Najeriya, Yusuf Tuggar ya kai birnin Yamai, fadar gwamnatin Nijar.

Bayan sanya hannu kan takardar, Ministan Harkokin Wajen Nijar, Bakary You Sangare, ya bayyana cewa, “da ma Najeriya ’yan uwanmu ne, duk wanda ya ce zai raba  Nijar da Najeriya, shi da kansa ya san ba gaskiya ba ne, abu ne na Allah.

Allah Ne Ya haɗa wannan zumunta ka, babu wanda ya isa ya raba ta.”

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: gwamnatin sojin Nijar Najeriya Nijar Tuggar Yamai

এছাড়াও পড়ুন:

Cin ganda na sa Najeriya tafka asarar $5bn — Gwamnatin Tarayya

Gwamnatin Tarayya ta yi gargaɗin cewa ci gaba da cin ganda da ake samu daga fatar shanu na barazana ga masana’antar fata ta Najeriya wadda darajarta ta kai kusan Dala biliyan biyar.

Yayin jawabi a taron ƙaddamar da yaƙi da cin ganda da aka gudanar a ranar Alhamis a Abuja, Darakta-Janar na Hukumar Bincike da Ci gaban Kayan Masana’antu, Farfesa Nnanyelugo Ikemounso, ya ce wannan dabi’a tana hana masana’antu na cikin gida samun muhimman kayayyakin da ake buƙata wajen samar da fata da kuma fitar da ita ƙasashen waje.

Tinubu ya sake naɗa Buba Marwa a matsayin shugaban NDLEA Majalisar Wakilai ta dage lokacin fara yin jarabawar WAEC a kwamfuta zuwa 2030

Ikemounso ya ce kasuwar kayan fata ta Najeriya ta kai darajar dala biliyan 2.79 a shekarar 2024, kuma ana hasashen za ta haura zuwa dala biliyan 4.96 nan da shekarar 2033.

Sai dai ya yi gargadin cewa ci gaba da karkatar da fata zuwa yin ganda na iya kawo cikas ga wannan ci gaban.

Ya ce, “Daga mahangar tattalin arziki da masana’antu, fatar shanu na ɗaya daga cikin muhimman kayan masarufi a Najeriya. Ƙasarmu na da masana’antar fata mai ƙarfi wadda ke da babbar damar samar da ayyukan yi, samun kuɗaɗen waje, da kuma ƙara gudummawa ga GDP.”

“A shekarar 2024, kasuwar kayan fata ta Najeriya ta kai darajar dala biliyan 2.79, tare da hasashen ta kai dala biliyan 4.96 nan da 2033.”

“Abin takaici, ci gaba da karkatar da fata zuwa cin ganda yana hana masana’antunmu samun ingantattun kayan masarufi, yana raunana sashen yin fata da sarrafa ta, kuma yana rage matsayin Najeriya a kasuwar fata ta duniya.”

A cewarsa, darajar sarkar fata ta duniya ana kiyasta ta tsakanin dala biliyan 420 zuwa dala tiriliyan 1, kuma idan aka yi kyakkyawan tsari sannan aka inganta kayan aiki, Najeriya na iya ƙara samun kaso mai yawa daga wannan kasuwa.

Shugaban ya ce amma wannan gangami ba ya nufin hana ’yan Najeriya cin ganda, sai dai don tabbatar da cewa fatar shanu da ta sauran dabbobi ana karkatar da su zuwa amfani na masana’antu domin amfanin ƙasa baki ɗaya.

Ana ɗaukar masana’antar fata ta Najeriya a matsayin ɗaya daga cikin manyan sassan tattalin arzikin da ba na man fetur ba, wadda ke da damar zama babbar hanyar samun kuɗaɗen fitar da kaya da kuma samar da ayyukan yi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Rikicin PDP: Fiye Da Wakilai 3,000 Ne Za Su Raba Gardama A Babban Taron Jam’iyyar
  • Manzon Allah (SAW) A Matsayin Dan Gatan Allah 
  • Cin ganda na sa Najeriya tafka asarar $5bn — Gwamnatin Tarayya
  • Ministan Harkokin Wajen Mali: Ba Abu Ne Mai Yiwawa Ba ‘Yan Tawaye Su Mamaye Mali
  • Ministocin Harkokin Wajen Iran da na Rasha sun Tattauna  Gabanin Taron Kwamitin Gwamnonin IAEA
  • MURIC ta buƙaci Tinubu ya sauke Amupitan daga shugabancin INEC
  • An gano motar da aka sace a Gidan Gwamnatin Kano
  • Ministocin Harkokin Wajen Kasashen Iran Da Rasha Sun Tattauna Kan Rikicin Yankin
  • Wike: Za mu kare duk wani soja da ke aiki bisa doka — Ministan Tsaro
  • Gwamnatin Jigawa Ta Himmatu Wajen Inganta Harkokin Kiwon Lafiya a Jihar