Aminiya:
2025-07-06@21:15:31 GMT

Najeriya da gwamnatin sojin Nijar da Nijar sun sasanta

Published: 17th, April 2025 GMT

Gwmanatin Sojin Nijar ta sanar da cewa sun sasanta da Gwmanatin Najeriya.

Hakan ta faru ne bayan ziyarar aiki da Ministan Harkokin Wajen Najeriya, Yusuf Tuggar ya kai birnin Yamai, fadar gwamnatin Nijar.

Bayan sanya hannu kan takardar, Ministan Harkokin Wajen Nijar, Bakary You Sangare, ya bayyana cewa, “da ma Najeriya ’yan uwanmu ne, duk wanda ya ce zai raba  Nijar da Najeriya, shi da kansa ya san ba gaskiya ba ne, abu ne na Allah.

Allah Ne Ya haɗa wannan zumunta ka, babu wanda ya isa ya raba ta.”

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: gwamnatin sojin Nijar Najeriya Nijar Tuggar Yamai

এছাড়াও পড়ুন:

Makusantan Gwamnatin Buhari da suka shiga haɗakar ADC

Kusoshin gwamnatin tsohon Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari sun shiga haɗakar jam’iyyun adawa ta ADC da nufin kayar da Gwamnatin Shugaba Bola Tinubu ta APC.

Tsofaffin mukarraban gwamnatin Buhari da suka koma haɗakar ADC sun haɗa da tsofaffin ministoci da tsofaffin gwamnoni da masu muƙaman siyasa.

Yawanci sun raba gari da APC ne saboda zargin an yi musu rashin adalci a jam’iyyar da kuma gazawar Gwamnatin Tinubu wajen magance matsalolin da ke ci wa ’yan Najeriya tuwo a ƙwarya.

1- Nasiru El-Rufai

Tsohon Gwamnan Jihar Kaduna Nasir El-Rufai na gaba ne a tafiyar haɗakar inda tun farko ya lashi takobin ƙalubalantar gwamnatin Tinubu a zaɓen 2027.

NAJERIYA A YAU: Shin Ko Hadakar Sabuwar Jamiyyar ADC Za Ta Fidda Wa ‘Yan Najeriya Kitse Daga Wuta? Rasha ta amince da gwamnatin Taliban a Afghanistan

Fara maganar haɗakar ke da wuya aka ga El-Rufai a gidan Buhari da ke Kaduna, inda ya sanar da ficewarsa daga APC.

Daga bisani El-Rufai tare da tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa Atiku Abubakar da wasu jaga-jigan ’yan APC a gwamnatin Buhari suka ziyarci shugaba kasan.

An yi zargin sun je ne domin neman albarkarsa domin ya amince wa ’yan tsohuwar jam’iyyarsa ta CPC su fice daga APC su shiga haɗakar.

2- Abubakar Malami

Ministan Shari’a a wa’adi biyu da Buhari ya yi, ya sanar da ficewarsa daga APC da kuma aniyarsu ta yaƙar Gwamnatin Tinubu a zaɓen 2027 saboda ta jefa ’yan Najeriya cikin halin ƙaƙa-ni-ka-yi da kuma gaza magance matsalolin tsaro da na tattalin arziki.

Tsohon ministan shari’an, kuma wanda tsohon wanda a baya ya nemi takarar Gwamnan Jihar Kebbi, an lura ya yi baya-baya a harkokin APC tun bayan hawan mulkin Tinubu.

3- Hadi Sirika

Tsohon Ministan Sufurin Jiragen Sama a zamanin Buhari, dan asalin Jihar Katsina ne, wato mahaifar tsohon shugaban ƙasan.

Hadi Siriya sun jima da taba da raba gari da Gwamnatin Tinubu kuma a halin yanzu yana fuskantar shari’a kan zargin karkatar da kuɗaɗen kwangila da sauran zarge-zarge a ma’aikatar sufurin jiragen sama.

4- Rotimi Amaechi

Tsohon Ministan Sufuri a zamanin Buhari, kuma tsohon Gwamnan Jihar Ribas, Rotimi Amaechi, ya bayyana aniyarsa ta fitowa takarar shugaban ƙasa a ADC.

Amaechi kamar takwarorinsa da suka fice daga APC bisa zargin an yi musu ba daidai ba, na zargin gwamnatin Tinubu da gazawa.

5- Rauf Aregbesola

Tsohon Gwamnan Jihar Osun wanda Buhari ya naɗa Ministan Harkokin Cikin Gida, tsohon na hannun daman Tinubu ne.

A halin yanzu shi ne ADC ta nada a matsayin Sakataren Jam’iyya.

6- Solomon Dalung

Tsohon Ministan Wasanni ya daga cikin waɗanda suka shiga wannan haɗaka ta ADC.

Ko da yake wa’adi daya kadai Dalung ya yi minista a zamanin Buhari, ida gaba bisani ya koma sukan kamun ludayin gwamnatin.

Bayan shafe watanni ana tattaunawa kan haɗakar jam’iyyun adawar ne dai a ranar Laraba suka ƙaddamar da shugabannin riƙo a ƙarƙashin jagorancin tsohon Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata David Mark.

Haka kuma sun naɗa tsohon Gwamnan Jihar Osun, Rauf Aregbesola a matsayin sakataren riko na ƙasa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Bincike ya nuna ’yan Najeriya ba su gamsu da gwamnatin Tinubu ba
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Da Tawagarsa Sun Isa Kasar Brazil Don Halartar Taron BRICS Karo Na 17
  • Sojoji sun kashe ’yan ta’adda 41 a Nijar
  • Wang Yi Da Takwaransa Na Ghana Sun Aikewa Juna Sakon Murnar Cika Shekaru 65 Da Kulla Dangantakar Diplomasiyya A Tsakanin Kasashensu
  • Shugaban Kasar Iran Ya Gana Da Fira Ministan Pakistan Tare Da Tattaunawa Kan Harin Da Iran Ta Fsukanta
  • “ADC za ta fuskanci matsala wajen zaɓen wanda zai yi mata takarar shugaban ƙasa”
  • Aragchi Ya Musanta Zargin Da Jamus Take Watsawa Dangane sa Shirin Nukliyar Kasar
  • Makusantan Gwamnatin Buhari da suka shiga haɗakar ADC
  • NAJERIYA A YAU: Shin Ko Hadakar Sabuwar Jamiyyar ADC Za Ta Fidda Wa ‘Yan Najeriya Kitse Daga Wuta?
  • Rasha ta amince da gwamnatin Taliban a Afghanistan