Ka dawo Najeriya ka magance matsalar tsaro —Obi ga Tinubu
Published: 17th, April 2025 GMT
Ɗan takarar shugaban kasa na Jam’iyyar Labour (LP) a zaben 2023, Peter Obi, ya buƙaci Shugaba Bola Ahmed Tinubu da ya dawo gida nan take domin tunkarar matsalar rashin tsaro da ke ƙara ƙamari.
Ya bayyana hakan ne a shafinsa na X, a daidai lokacin da ake samun ƙaruwar hare-haren ’yan bindiga a jihohin Filato, Zamfara, Borno da wasu sassan ƙasar.
Shugaba Tinubu ya tafi Faransa a ranar 2 ga Afrilu don “tafiyar aiki” na makonni biyu. Daniel Bwala, Mataimakin Shugaban Ƙasa na Musamman kan Yaɗa Manufofi, ya ce tafiyar na da nufin yin yin bitar tsare-tsaren gwamnatin Tinubu da kuma sauye-sauyen, gabanin cikar shekaru biyu na gwamnatin.
A cikin saƙonsa na ranar Laraba, Obi ya ce ya zama dole ya ja hankalin “shugabanmu mai janyewa, zuwa ga ƙalubalen tsaro a gida,” yana mai jaddada buƙatar “ya dakatar da kansa bayan da yake yi a ƙasar waje nan take, ya dawo gida domin magance matsalar tsaro da ta mamaye ƙasar.”
An kashe shanu 36, an ba 42 guba a Filato Gwamnatin Tarayya ta buƙaci ’yan jarida su daina kawo rahoton ayyukan ’yan ta’addaYa bayyana cewa, wannan kira nasa na gaggawa ya zama dole saboda ƙaruwar ta’addanci da miyagun laifuka a faɗin Najeriya, tare da rashin ganin matakan da gwamnati ke ɗauka a zahiri.
Ya bayyana wa Tinubu cewa, “A cikin makonni biyu da kuka yi a waje, sama da ’yan Najeriya 150 sun rasa rayukansu sakamakon rashin tsaro a faɗin ƙasar, musamman a jihohin Filato da Zamfara. Fashewar bututun mai da aka yi a yankin Neja Delta, ya ƙara nuna kasar cikin kunci.
“A Arewa Maso Gabas, shugabannin Jihar Borno na kuka game da dawowar ’yan ta’adda, inda ake kashe sojoji da fararen hula ba tare da dalili ba. A Kudu Maso Gabas, labarin haka yake: kashe-kashe da garkuwa da mutane.
“A cikin duk waɗannan, shugaban kamfanin da ke da cikin matsala, mai suna Najeriya, ya bar hedikwatar kamfanin ya je ya yi zamansa a ƙasar Faransa,” in ji Obi.
Ya jaddada cewa, babban aikin kowace gwamnati shi ne tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyin ’yan kasarta, yana mai tambayar “dalilin zaman a wata ƙasa da shugabanninsu suka tabbatar da zaman lafiya yayin da jini ke ci gaba da zuba a tamu ƙasar.”
Obi ya ce, gwagwarmayar samun Najeriya ta gari ba batu ne na tabbatar da cewa kowane ɗan kasa ya ga, ya ji, kuma ya amfana da manufofi da shawarwarin waɗanda ke kan mulki.
“Don haka, ina kira ga shugaban ƙasa da ya dakatar da duk abin da yake yi a Faransa da sauri ya dawo gida ya ɗauki mataki ta hanyar magance waɗannan batutuwa masu tayar da hankali,” in ji Obi.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Faransa Najeriya Tsaro
এছাড়াও পড়ুন:
Kungiyar Hamas Ta Yi Kiran Da A Sanya Isra’ila Cikin Jerin Masu Aikata Abin Kunya Saboda Kashe Yara
Kungiyar Gwagwarmayar Musulunci ta Hamas ta yi kira da a saka gwamnatin mamayar Isra’ila cikin jerin ‘masu aikata abin kunya’ saboda take hakkin yara
Majalisar Dinkin Duniya ta yi bikin Ranar Yara ta Duniya a ranar 20 ga Nuwamba, yayin da yaran Falasdinawa ke fuskantar mummunan yanayi sakamakon laifukan Yahudawan sahayoniyya ‘yan mamaya, wanda ya lalata tushen rayuwa, gami da abinci, magani, ruwa mai tsafta, kiwon lafiya, ilimi, da tallafin tunani. Wannan ya zama keta yarjejeniyoyi na duniya da dabi’un jin kai, da kuma rashin biyayya ga kudurorin Majalisar Dinkin Duniya da ke tabbatar da ‘yancin yaran Falasdinawa.
A Ranar Yara ta Duniya, Kungiyar gwagwarmayar Musulunci ta Hamas ta bayyana cewa: Bikin na wannan shekarar ya zo ne yayin da yakin shekaru biyu na kisan kare dangi da yunwa a yankin Gaza ya bar yara sama da 20,000 suka mutu, dubbai kuma suka bata a karkashin baraguzan gine-gine, da kuma yara sama da 30,000 wadanda suka rasa iyaye. Dubban mutane sun ji rauni kuma suna rashin lafiya, suna bukatar jinyar gaggawa a kasashen waje.
A yankin yammacin Kogin Jordan da aka mamaye, wahalar da yara ke sha ta ci gaba saboda kisan gilla da gangan, wariyar al’umma, rushe gidaje, rufe hanyoyi da makarantu, tilastawa mutane yin gudun hijira, hana ilimi, kai hare-haren wuce gona da iri kan Falasdinawa. Adadin yara da suka yi shahada a Yammacin Kogin Jordan kadai ya wuce 300 a cikin shekaru biyu da suka gabata.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Tarayyar Turai Ta Kakaba Takunkumi Kan Dan Uwan Kwamandan Rapid Support Forces Ta Sudan November 21, 2025 Iran Tana Cikin kasashe 10 Na Farko Da Su Ka Fi Yawan Wuraren Tarihi November 20, 2025 Nigeria:Kotu Ta Yanke Wa Nnamdi Kanu Hukuncin Zaman Kurkuku Na Har Abada November 20, 2025 Nigeria: An Rufe Makarantun Kwana A Jahar Kwara Saboda Matsalar Tsaro November 20, 2025 Hizbullah: Ba Za Mu Taba Ajiye Makamanmu Ba November 20, 2025 Ribadu Ya Jagoranci Tawagar Nijeriya Zuwa Amurka Kan Zargin Yi Wa Kiristoci Kisan Gilla November 20, 2025 Hukumar Kula Da Jiragen Sama Ta Najeriya Ta ci Tarar Kamfanin Jiragen Sama Na Qatar November 20, 2025 Hamas Tayi Gargadi Game Da Kara Dagulewar Al’amura Bayan Harin Isra’ila A Gaza November 20, 2025 Labanon Ta Bukaci Gudanar Da Taron Kwamitin Tsaro Na MDD Cikin Gaggawa November 20, 2025 Achraf Hakimi Ya Zama Gwarzon Wasan Kwallon Kafar Afirka Na Shekara Ta 2025 November 20, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci