Aminiya:
2025-05-21@21:56:35 GMT

Ka dawo Najeriya ka magance matsalar tsaro —Obi ga Tinubu

Published: 17th, April 2025 GMT

Ɗan takarar shugaban kasa na Jam’iyyar Labour (LP) a zaben 2023, Peter Obi, ya buƙaci Shugaba Bola Ahmed Tinubu da ya dawo gida nan take domin tunkarar matsalar rashin tsaro da ke ƙara ƙamari.

Ya bayyana hakan ne a shafinsa na X, a daidai lokacin da ake samun ƙaruwar hare-haren ’yan bindiga a jihohin Filato, Zamfara, Borno da wasu sassan ƙasar.

Shugaba Tinubu ya tafi Faransa a ranar 2 ga Afrilu don “tafiyar aiki” na makonni biyu. Daniel Bwala, Mataimakin Shugaban Ƙasa na Musamman kan Yaɗa Manufofi, ya ce tafiyar na da nufin yin yin bitar tsare-tsaren gwamnatin Tinubu da kuma sauye-sauyen, gabanin cikar shekaru biyu na gwamnatin.

A cikin saƙonsa na ranar Laraba, Obi ya ce ya zama dole ya ja hankalin “shugabanmu mai janyewa, zuwa ga ƙalubalen tsaro a gida,” yana mai jaddada buƙatar “ya dakatar da kansa bayan da yake yi a ƙasar waje nan take, ya dawo gida domin magance matsalar tsaro da ta mamaye ƙasar.”

An kashe shanu 36, an ba 42 guba a Filato Gwamnatin Tarayya ta buƙaci ’yan jarida su daina kawo rahoton ayyukan ’yan ta’adda

Ya bayyana cewa, wannan kira nasa na gaggawa ya zama dole saboda ƙaruwar ta’addanci da  miyagun laifuka a faɗin Najeriya, tare da rashin ganin matakan da gwamnati ke ɗauka a zahiri.

Ya bayyana wa Tinubu cewa, “A cikin makonni biyu da kuka yi a waje, sama da ’yan Najeriya 150 sun rasa rayukansu sakamakon rashin tsaro a faɗin ƙasar, musamman a jihohin Filato da Zamfara. Fashewar bututun mai da aka yi a yankin Neja Delta, ya ƙara nuna kasar cikin kunci.

“A Arewa Maso Gabas, shugabannin Jihar Borno na kuka game da dawowar ’yan ta’adda, inda ake kashe sojoji da fararen hula ba tare da dalili ba. A Kudu Maso Gabas, labarin haka yake: kashe-kashe da garkuwa da mutane.

“A cikin duk waɗannan, shugaban kamfanin da ke da cikin matsala, mai suna Najeriya, ya bar hedikwatar kamfanin ya je ya yi zamansa a ƙasar Faransa,” in ji Obi.

Ya jaddada cewa, babban aikin kowace gwamnati shi ne tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyin ’yan kasarta, yana mai tambayar “dalilin zaman a wata ƙasa da shugabanninsu suka tabbatar da zaman lafiya yayin da jini ke ci gaba da zuba a tamu ƙasar.”

Obi ya ce, gwagwarmayar samun Najeriya ta gari ba batu ne na tabbatar da cewa kowane ɗan kasa ya ga, ya ji, kuma ya amfana da manufofi da shawarwarin waɗanda ke kan mulki.

“Don haka, ina kira ga shugaban ƙasa da ya dakatar da duk abin da yake yi a Faransa da sauri ya dawo gida ya ɗauki mataki ta hanyar magance waɗannan batutuwa masu tayar da hankali,” in ji Obi.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Faransa Najeriya Tsaro

এছাড়াও পড়ুন:

Wani Mutum Ya Kashe Matarsa Da Duka Har Lahira A Edo

Mahaifinta, Everistus Nnadozie, ya ce an sanar da shi cewa surukinsa Esosa Imasuen ne ya yi wa ‘yarsa duka har ta samu raunika sosai.

Ya ƙara da cewa an kai ta asibiti inda likita ya tabbatar da cewa tana fama da zubar jini a cikin jikinta.

Ya ce kafin ya isa asibitin, ‘yarsa ta rasu.

Bayan haka kuma, Esosa ya ɗauki gawarta ya kai wani waje ba tare da ya sanar da iyayenta ba.

“Na je gidansa, sai aka ce ya tsere,” in ji mahaifin.

Ya ce yana ta kiran Esosa domin ya nuna masa inda aka kai gawar ‘yarsa, amma ya ƙi amsa waya.

Da aka tuntuɓi kakakin rundunar ‘yansandan Jihar Edo, ya ce sun duba wurare da dama a Benin, amma babu rahoton wannan lamari.

Ana ci gaba da neman Esosa Imasuen ruwa a jallo.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shirye-shiryen Shugaba Tinubu Suna Buɗe Hanyar Farfaɗowar Tattalin Arzikin Nijeriya – Minista
  • Sojoji da ’yan siyasa na taimaka wa Boko Haram da bayanai — Zulum
  • Wani Mutum Ya Kashe Matarsa Da Duka Har Lahira A Edo
  • Gwamnatin Jihar Neja Ta Jaddada Shirinta Na Yaki Da  Matsalar Tsaro 
  • An kashe makiyaya 2 a wani hari a Filato
  • An kama matar ɗan ta’adda Ado Aliero da mahaifiyarsa a cikin maniyyata a Saudiyya
  • Kasashen duniya 22 sun bukaci Isra’ila da ta dawo da agaji gaba daya a Gaza
  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutum 3, Sun Sace 26 A Zamfara
  • Yadda jami’an tsaron Vatican suka hana Seyi zuwa wajen Tinubu da Fafaroma
  • NAJERIYA A YAU: Mece ce Makomar Dimokuraɗiyya Idan Aka Wajabta Kada Kuri’a?