Aminiya:
2025-12-13@14:14:08 GMT

Ka dawo Najeriya ka magance matsalar tsaro —Obi ga Tinubu

Published: 17th, April 2025 GMT

Ɗan takarar shugaban kasa na Jam’iyyar Labour (LP) a zaben 2023, Peter Obi, ya buƙaci Shugaba Bola Ahmed Tinubu da ya dawo gida nan take domin tunkarar matsalar rashin tsaro da ke ƙara ƙamari.

Ya bayyana hakan ne a shafinsa na X, a daidai lokacin da ake samun ƙaruwar hare-haren ’yan bindiga a jihohin Filato, Zamfara, Borno da wasu sassan ƙasar.

Shugaba Tinubu ya tafi Faransa a ranar 2 ga Afrilu don “tafiyar aiki” na makonni biyu. Daniel Bwala, Mataimakin Shugaban Ƙasa na Musamman kan Yaɗa Manufofi, ya ce tafiyar na da nufin yin yin bitar tsare-tsaren gwamnatin Tinubu da kuma sauye-sauyen, gabanin cikar shekaru biyu na gwamnatin.

A cikin saƙonsa na ranar Laraba, Obi ya ce ya zama dole ya ja hankalin “shugabanmu mai janyewa, zuwa ga ƙalubalen tsaro a gida,” yana mai jaddada buƙatar “ya dakatar da kansa bayan da yake yi a ƙasar waje nan take, ya dawo gida domin magance matsalar tsaro da ta mamaye ƙasar.”

An kashe shanu 36, an ba 42 guba a Filato Gwamnatin Tarayya ta buƙaci ’yan jarida su daina kawo rahoton ayyukan ’yan ta’adda

Ya bayyana cewa, wannan kira nasa na gaggawa ya zama dole saboda ƙaruwar ta’addanci da  miyagun laifuka a faɗin Najeriya, tare da rashin ganin matakan da gwamnati ke ɗauka a zahiri.

Ya bayyana wa Tinubu cewa, “A cikin makonni biyu da kuka yi a waje, sama da ’yan Najeriya 150 sun rasa rayukansu sakamakon rashin tsaro a faɗin ƙasar, musamman a jihohin Filato da Zamfara. Fashewar bututun mai da aka yi a yankin Neja Delta, ya ƙara nuna kasar cikin kunci.

“A Arewa Maso Gabas, shugabannin Jihar Borno na kuka game da dawowar ’yan ta’adda, inda ake kashe sojoji da fararen hula ba tare da dalili ba. A Kudu Maso Gabas, labarin haka yake: kashe-kashe da garkuwa da mutane.

“A cikin duk waɗannan, shugaban kamfanin da ke da cikin matsala, mai suna Najeriya, ya bar hedikwatar kamfanin ya je ya yi zamansa a ƙasar Faransa,” in ji Obi.

Ya jaddada cewa, babban aikin kowace gwamnati shi ne tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyin ’yan kasarta, yana mai tambayar “dalilin zaman a wata ƙasa da shugabanninsu suka tabbatar da zaman lafiya yayin da jini ke ci gaba da zuba a tamu ƙasar.”

Obi ya ce, gwagwarmayar samun Najeriya ta gari ba batu ne na tabbatar da cewa kowane ɗan kasa ya ga, ya ji, kuma ya amfana da manufofi da shawarwarin waɗanda ke kan mulki.

“Don haka, ina kira ga shugaban ƙasa da ya dakatar da duk abin da yake yi a Faransa da sauri ya dawo gida ya ɗauki mataki ta hanyar magance waɗannan batutuwa masu tayar da hankali,” in ji Obi.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Faransa Najeriya Tsaro

এছাড়াও পড়ুন:

Iyaye Sun Yi Fitowar Farin Dango Don Yi Wa “Yayansu Allurar Rigakafi a Sule-Tankarkar

Daga Usman Muhammad Zaria 

Aikin rigakafin watan Disamba a karamar hukumar Sule-Tankarkar ta jihar Jigawa ya samu gagarumar nasara, yayin da iyaye suka fito kwansu da kwarkwata domin tabbatar da cewa an yi wa ’ya’yansu cikakken rigakafi.

Wasu daga cikin iyayen da suka kawo ’ya’yansu domin karbar rigakafin yau da kullum da na shan inna sun bayyana jin dadinsu kan yadda aka gudanar da aikin cikin kwanciyar hankali.

 

Daya daga cikinsu, Malama Ummahani Danbala, ta ce an wayar da kan jama’a sosai ta hannun mata ’yan sa-kai a unguwarsu, inda aka karfafa gwiwar iyaye mata su kawo ’ya’yansu domin karbar rigakafin yau da kullum da na shan inna.

Malam Yunusa, wani mai sa ido a karamar hukumar, ya bayyana gamsuwarsa da yadda aka gudanar da aikin rigakafin a yankin.

A cewarsa, aikin wayar da kan jama’a ya yi matukar tasiri, domin mutane na kawo ’ya’yansu da kansu ba tare da kin amincewa da rigakafin ba.

Yunusa ya bayyana cewa duk da kasancewar karamar hukumar tana kan iyaka, aikin ya gudana cikin nasara, sakamakon hadin gwiwar da aka samu daga dukkan masu ruwa da tsaki.

Ya kara da cewa ana sa ran rigakafin yara kusan 45,221, inda aka yi niyyar kai rigakafin makarantu da wuraren ibada domin gano yaran da ba a musu ba.

Rediyon Najeriya ya ruwaito cewa karamar hukumar na da cibiyoyin lafiya guda 28, kuma aikin rigakafin ya gudana cikin kwanciyar hankali a al’ummomin Ablasu, Kings, Amanda, Togai, Nagwamatse da Hannun Giwa.

Ana sa ran kammala zagayen rigakafin shan inna na watan Disamba a ranar Juma’a a fadin kananan hukumomi 27 na jihar Jigawa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ’Yan sanda sun ba da tabbacin isasshen tsaro a zaɓen ƙananan hukumomin Borno
  • Iyaye Sun Yi Fitowar Farin Dango Don Yi Wa “Yayansu Allurar Rigakafi a Sule-Tankarkar
  • Zan yi amfani da Salah a wasan Liverpool da Brighton — Arn Slot
  • Kungiyar NLC A Najeriya Ta Shirya Zanga-Zanga Kan Matsalar Rashin Tsaro A Fadin Kasa
  • Sojoji sun kashe ’yan ta’adda 2, sun ƙwato makamai a Borno
  • Tinubu Ya Yaba Wa Jami’an Tsaro Kan Ceto Dalibai 100 Da Aka Sace A Neja
  • NLC Ta Shirya Zanga-Zangar Rashin Tsaro A Faɗin Ƙasa Ranar 17 Ga Disamba
  • Gwamnonin Arewa Sun Yi Rawar Gani A Kafa Gidauniyar Fuskantar Matsalar Tsaro
  • Kotu Ta Yanke Wa Wani Mutum Hukuncin Kisa Bisa Garkuwa Da Kashe Mai Gidansa A Kano
  • ‘Sojojin Najeriya da na Ivory Coast 200 sun shiga domin tsaftace Jamhuriyar Benin’