Ka dawo Najeriya ka magance matsalar tsaro —Obi ga Tinubu
Published: 17th, April 2025 GMT
Ɗan takarar shugaban kasa na Jam’iyyar Labour (LP) a zaben 2023, Peter Obi, ya buƙaci Shugaba Bola Ahmed Tinubu da ya dawo gida nan take domin tunkarar matsalar rashin tsaro da ke ƙara ƙamari.
Ya bayyana hakan ne a shafinsa na X, a daidai lokacin da ake samun ƙaruwar hare-haren ’yan bindiga a jihohin Filato, Zamfara, Borno da wasu sassan ƙasar.
Shugaba Tinubu ya tafi Faransa a ranar 2 ga Afrilu don “tafiyar aiki” na makonni biyu. Daniel Bwala, Mataimakin Shugaban Ƙasa na Musamman kan Yaɗa Manufofi, ya ce tafiyar na da nufin yin yin bitar tsare-tsaren gwamnatin Tinubu da kuma sauye-sauyen, gabanin cikar shekaru biyu na gwamnatin.
A cikin saƙonsa na ranar Laraba, Obi ya ce ya zama dole ya ja hankalin “shugabanmu mai janyewa, zuwa ga ƙalubalen tsaro a gida,” yana mai jaddada buƙatar “ya dakatar da kansa bayan da yake yi a ƙasar waje nan take, ya dawo gida domin magance matsalar tsaro da ta mamaye ƙasar.”
An kashe shanu 36, an ba 42 guba a Filato Gwamnatin Tarayya ta buƙaci ’yan jarida su daina kawo rahoton ayyukan ’yan ta’addaYa bayyana cewa, wannan kira nasa na gaggawa ya zama dole saboda ƙaruwar ta’addanci da miyagun laifuka a faɗin Najeriya, tare da rashin ganin matakan da gwamnati ke ɗauka a zahiri.
Ya bayyana wa Tinubu cewa, “A cikin makonni biyu da kuka yi a waje, sama da ’yan Najeriya 150 sun rasa rayukansu sakamakon rashin tsaro a faɗin ƙasar, musamman a jihohin Filato da Zamfara. Fashewar bututun mai da aka yi a yankin Neja Delta, ya ƙara nuna kasar cikin kunci.
“A Arewa Maso Gabas, shugabannin Jihar Borno na kuka game da dawowar ’yan ta’adda, inda ake kashe sojoji da fararen hula ba tare da dalili ba. A Kudu Maso Gabas, labarin haka yake: kashe-kashe da garkuwa da mutane.
“A cikin duk waɗannan, shugaban kamfanin da ke da cikin matsala, mai suna Najeriya, ya bar hedikwatar kamfanin ya je ya yi zamansa a ƙasar Faransa,” in ji Obi.
Ya jaddada cewa, babban aikin kowace gwamnati shi ne tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyin ’yan kasarta, yana mai tambayar “dalilin zaman a wata ƙasa da shugabanninsu suka tabbatar da zaman lafiya yayin da jini ke ci gaba da zuba a tamu ƙasar.”
Obi ya ce, gwagwarmayar samun Najeriya ta gari ba batu ne na tabbatar da cewa kowane ɗan kasa ya ga, ya ji, kuma ya amfana da manufofi da shawarwarin waɗanda ke kan mulki.
“Don haka, ina kira ga shugaban ƙasa da ya dakatar da duk abin da yake yi a Faransa da sauri ya dawo gida ya ɗauki mataki ta hanyar magance waɗannan batutuwa masu tayar da hankali,” in ji Obi.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Faransa Najeriya Tsaro
এছাড়াও পড়ুন:
Labarin yi wa Kiristoci kisan kiyashi a Najeriya ƙarya ne – Sarkin Musulmi
Sarkin Musulmi, Alhaji Sa’ad Abubakar III, ya karyata zargin kisan kiyashi ga Kiristoci a Najeriya, yana mai cewa wannan ikirari ƙarya ne kuma bai kamata a ci gaba da yada shi ba.
Sarkin ya bayyana hakan ne a taron Babban Majalisar Sarakunan Gargajiya na Arewa na shekarar 2025, wanda aka gudanar a Birnin Kebbi, Jihar Kebbi, a ranar Talata, da taken: “Ƙarfafa Haɗin Gwiwar Al’umma Domin Samun Zaman Lafiya da Tsaro Mai Dorewa a Arewa.”
Masu kwacen waya sun kashe ma’aikaciyar lafiya a Zariya Majalisa ta soma binciken yadda aka kashe $4.6bn na tallafin kiwon lafiyaYa ce: “Sun dade suna cewa ana kisan kiyashi ga Kiristoci a Najeriya daga ƙasashen Yamma kamar Amurka, Kanada da sauransu. A ina? Yaushe? Wannan labari ne na ƙarya.”
Sarkin, wanda kuma shi ne Shugaban Majalisar Sarakunan Gargajiya na Arewacin Najeriya ya ce ba zai yiwu a ce ana irin wannan kisa a wani yanki na Najeriya ba, kuma sarakunan gargajiya ba su sani ba.
Ya roƙi shugabannin ƙasa da su sanya dokoki kan amfani da kafafen sada zumunta saboda illar da suke haifarwa da kuma abubuwan batanci da ake wallafawa game da ƙasa da mutane a cikinsu.
Sarkin ya kuma buƙaci ‘yan Najeriya da su daina zagin sojoji, yana mai jaddada cewa da babu sadaukarwarsu, da ƙasa ba za ta ci gaba da kasancewa ƙasa ɗaya mai zaman lafiya ba.
Sai dai ya amince cewa sojoji na fama da ƙalubale da gazawa, amma ya soki maganganun da ake yi a kafafen sada zumunta da ke zargin jami’an tsaro da haɗin gwiwa da ‘yan ta’adda, yana mai cewa hakan rashin tausayi ne kuma bai dace ba.
Sarkin ya sake jaddada goyon bayan sarakunan gargajiya ga ci gaban dimokuraɗiyya da biyayya ga dukkan shugabannin da aka zaɓa, ciki har da Shugaban Ƙasa, Majalisun Tarayya da na Jihohi, da Gwamnoni.
Ya kuma buƙaci sarakunan da suka halarci taron da su haɗa kai domin fuskantar ƙalubalen da ƙasa ke ciki, yana mai cewa za a mika shawarwarin da suka bayar ga Gwamnonin Arewa domin ɗaukar matakin da ya dace.
Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Kasa, Femi Gbajabiamila, wanda ya wakilci Shugaba Bola Tinubu a taron ya ce sarakunan gargajiya na da muhimmiyar rawa wajen inganta zaman lafiya da kwanciyar hankali.
Ya ce suna da ƙwarewa wajen rage tashin hankali, warware rikice-rikice, da kawo zaman lafiya a lokacin ƙalubale.