Gwamnatin Tarayya ta nemi kafafen watsa labarai da su daina kawo rahoton ayyukan ‘yan ta’addan da ke tada hankali a jihohin Filato, Borno, Zamfara, Binuwai, da sauransu.

Aminiya ta rawaito cewa jihohin na fama da tashe-tashen hankula musamman a baya-bayan nan in da aka yi asarar rayuka da dukiyoyin al’umma.

Dangote ya karya farashin fetur karo na biyu a mako guda Hisbah ta kama matashi yana ‘baɗala’ da Akuya a Kano

Wannan ya sanya wasu ‘yan Nijeriyar da suka haɗa da sarakuna, ‘yan siyasa, ƙungiyoyin cikin gida da na waje tuhumar gwamnati kan aikinta na kare ‘yan ƙasa.

Sai dai gwamnatin ta bakin Ministan Yaɗa Labarai da Al’adu, Mohammed Idris, ta ce yaɗa labaran ayyukan ’yan ta’addan da ’yan jarida ke yi ne ke ƙara kawo barazana ga tsaron ƙasar.

Ministan ya bayyana hakan ne a hedikwatar rundunar soji da ke Abuja a yayin a wani taron masu ruwa da tsaki a harkokin kafafen yaɗa labarai.

Ministan wanda babban daraktan kafar Muryar Nijeriya, Jibril Ndace ya wakilta, ya ce gwamnatinsu na ƙoƙari wajen kawo ƙarshen matsalar tsaro, ta hanyar samar wa jami’an tsaro kayan aiki, horo, da tattara bayanan sirri.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: yan ta adda Ministan Yada Labarai Tsaro Zamfara

এছাড়াও পড়ুন:

Akwai Kure A Maganar Gwamna Kan Kulawa Da Masu Rauni – Ƙungiyar Dattawan Zamfara

“Mutanen Zamfara ba wawaye ba ne. Gwamnan ya kamata ya daina waɗannan maganganun ƙarya, ya daina farfaganda, ya kuma haɗa kai da masu ruwa da tsaki na gaskiya don magance matsalar tsaro,” in ji Gummi.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Babu Wata Matar Da Aka Gurfanar Saboda Wai Ta Zama Kirista – Gwamnatin Zamfara
  • Babu Wata Matar Da Aka Gurfanar Saboda Wai Ta Zama Kirista – Gwamnatin ZamfaraBabu Wata Matar Da Aka Gurfanar Saboda Wai Ta Zama Kirista – Gwamnatin Zamfara
  • Gwamnatin Jihar Neja Ta Jaddada Shirinta Na Yaki Da  Matsalar Tsaro 
  • Gwamnati za ta sayar da gidaje 753 da EFCC ta ƙwato a hannun Emefiele 
  • Gwamnatin Tarayya Ta Nanata Kudurin Koyawa Matasa Sana’o’in Hannu
  • Hajji: Kawo Yanzu An Kammala Jigilar Maniyyatan Jihohi 12 A Nijeriya – NAHCON
  • An kama matar ɗan ta’adda Ado Aliero da mahaifiyarsa a cikin maniyyata a Saudiyya
  • Zulum ya roƙi Gwamnatin Tarayya ta kai wa Marte ɗauki
  • Akwai Kure A Maganar Gwamna Kan Kulawa Da Masu Rauni – Ƙungiyar Dattawan Zamfara
  • Fira Ministan Libiya Ya Tantance Bangarorin Da Kula Da Hakkin Tsaron Kasar Ya Rataya A Wuyarsu