Mai magana da yawun hukumar, Dele Oyewale ya tabbatar da kama mutanen

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp.

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

’Yan sanda sun kama ƙunshi 66 na Tabar Wiwi a Gombe

Rundunar ’Yan Sandan Jihar Gombe ta kama ƙunshi 66 na ganyen tabar wiwi a wani samame da ta kai a garin Deba, bayan samun wasu sahihin bayanan leƙen asiri.

Mai magana da yawun rundunar, DSP Buhari Abdullahi, ya bayyana cewa lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 9:30 na dare a ranar 16 ga Nuwamba, 2025, lokacin da aka hango wata mota mara lamba, ƙirar Toyota Corolla, da ake zargi tana ɗauke da kayan, a kan hanyar Kuri zuwa Deba.

Hauhawar farashi ya ƙara raguwa a Nijeriya — NBS An ɗaura auren Sanata Kawu Sumaila da wata jami’ar soji a Kano

Aminiya ta ruwaito cewa, bayan isar jami’an wurin da ake zargin akwai kayan laifin ne, sun lura da wasu mutum uku suna ƙoƙarin yi wa wani mutum lodi a kan babur, lamarin da ya sanya ababen zargin suka tsere bayan hango ’yan sandan.

Kayan laifin da aka kama a Gombe

Binciken farko da aka gudanar ya kai ga gano buhuna uku ɗauke da ƙunshi 66 na ganyen da ake zargin tabar wiwi ce.

An dai kwashe kayayyakin zuwa ofishin ’yan sanda, kuma an fara bincike don kamo waɗanda suka tsere.

Kwamishinan ’Yan Sanda na Jihar Gombe, CP Bello Yahaya, ya jinjina wa jami’an da suka gudanar da wannan aiki, yana mai tabbatar da cewa rundunar za ta ci gaba da fatattakar masu safarar miyagun ƙwayoyi a faɗin jihar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Mutane 7 sun mutu a hatsarin mota a Jigawa
  • Mayaƙan ISWAP sun kashe kwamandan soji a Borno
  • ’Yan sanda sun kama ƙunshi 66 na Tabar Wiwi a Gombe
  • Sojojin HKi Sun Kashe Wasu Falasdinawa Guda 2 A Sansanin Yan Gudun Hijira
  • Shugaban Nukiliyar Iran Yace Amurka Da Israila Sun Shiga Sabon Mataki Mai Hadari
  • Mutane 42 Sun Mutu A Wani Hatsarin Tankar Dizal Da Motar Masu Umrah A Hanyar Makka
  • ’Yan bindiga 5 Sun shiga hannun ’yan sanda a Kebbi
  • Afirka ta Kudu na Binciken shigar wasu ‘yan gudun hijirar Falasdinu 153 cikin kasar
  • Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara
  • APOSUN Ta Jaddada Aniyarta Na Daƙile Hada-hadar Haramtattun Kuɗaɗe