Mai magana da yawun hukumar, Dele Oyewale ya tabbatar da kama mutanen

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp.

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

NAFDAC ta lalata kayayyakin Naira biliyan 5 a Jihar Nasarawa

Hukumar kula da ingancin abinci da magunguna ta Najeriya (NAFDAC) ta lalata kayayyaki marasa inganci da suka kai sama da Naira biliyan 5 a Jihar Nasarawa.

Kayayyakin da aka ƙwato daga jihohin Arewa ta Tsakiya da suka haɗa da Nasarawa, Benuwe da Kogi da Filato, an lalata su ne a wurin zuba shara a Angwan Rere da ke Lafiya.

Manchester United ta shiga zawarcin Sergio Ramos Zanga-zanga ta ɓarke bayan haɗarin tirela ta kashe mutum a Yobe

Darakta Janar ta Hukumar NAFDAC, Farfesa Christianah Adeyeye, wanda Daraktan shiyyar Arewa ta Tsakiya, Mista Kenneth Azikiwe ya wakilta, ya bayyana cewa an ƙwace kayayyakin ne a lokacin gudanar da aikin sa ido.

Ta kuma jaddada cewa hukumar na da burin hana waɗannan kayayyaki masu hatsarin gaske su sake shiga kasuwa tare da haifar da illa ga jama’a.

“Wasu daga cikin waɗannan kayayyakin an ɓoye su ne da gangan, an kuma sake sabunta su da gangan bayan ƙarewar wa’adin amfanin da su, an ajiye su da mugun nufi, wasu marasa kishi ne suke sayar da su ga ‘yan Najeriya.

“Har ila yau, lalata kayayyakin da wa’adinsu suka ƙare don son rai ga wasu ’yan kasuwa maza da mata, inda wasu masu kishi da tsoron Allah suka miƙa mana rahoton.”

Kayayyakin da aka lalata sun haɗa da abinci mara kyau, magunguna na jabu, na’urorin likitanci na jabu, ƙayatattun kayan kwalliya da sinadarai da wa’adinsu suka ƙare.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • EFCC na ƙoƙarin daƙile muradin Malami na yin takarar gwamna — ADC
  • Haɗin Kan Musulmai Da Kirista A Nijeriya Zai Kawo Saukin Matsalar Tsaro — Shehu Sani
  • Amurka ta kama jirgin ruwan dakon man Najeriya
  • Benin ta fitar da sammacin kama dan fafutuka Kemi Seba
  • Zaɓen 2027 ya hana ni korar wasu ma’aikata – Bago
  • Kotu Ta Umarci EFCC Ta Biya Wani Ƴan Kasuwar Kano Miliyan 5, Ta Nemi Afuwar Su
  • Tinubu Ya Yaba Wa Jami’an Tsaro Kan Ceto Dalibai 100 Da Aka Sace A Neja
  • NAFDAC ta lalata kayayyakin Naira biliyan 5 a Jihar Nasarawa
  • EFCC ta tsare tsohon ministan ƙwadago, Chris Ngige
  • Cin hanci da rashawa sun yi ƙatutu a Najeriya — ICPC