Mai magana da yawun hukumar, Dele Oyewale ya tabbatar da kama mutanen

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp.

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Wasu jiga-jigan ADC za su dawo jam’iyyarmu — Shugaban Jam’iyyar APC

Shugaban Jam’iyyar APC na Kasa, Farfesa Nentawe Yilwatda, ya bayyana cewa wasu manyan jiga-jigan jam’iyyar ADC, za su koma APC a mako mai zuwa.

A makonnin da suka gabata, ’yan siyasa da dama daga jam’iyyun adawa suna sauya sheƙa zuwa APC, yayin da ake shirin tunkarar babban zaɓen shekarar 2027.

HOTUNA: Al’ummar Jihar Neja sun yi addu’o’in neman zaman lafiya Ta’addanci: An fi kashe Musulmi a kan Kiristoci a Najeriya — Jakadan Amurka

Idan ba a manta ba, Gwamnan Jihar Enugu, Peter Mbah, ya koma APC, sannan Gwamnan Jihar Bayelsa, Douye Diri, shi ma ana sa ran zai sanar da sauya sheƙarsa a hukumance nan ba da jimawa ba.

Yilwatda, yayin ganawarsa da mambobin APC a Jos, Jihar Filato, ya ce: “A mako mai zuwa zan karɓi wasu fitattun mutane daga ADC. Wasu daga cikinsu sun bar PDP sun koma ADC, amma yanzu za su dawo APC.”

Ya ƙara da cewa, yawancin waɗanda za su koma jam’iyyar “sun riga sun kammala gwajin lafiyarsu” kuma za a tarbe su a hukumance a mako mai zuwa.

“A cikin makonni biyu masu zuwa, za mu kuma bayyana wani babban ɗan siyasa da ya kammala gwajin lafiyarsa. Za mu karɓe shi a hukumance nan gaba kaɗan,” in ji shi.

Shugaban jam’iyyar ya bayyana APC a matsayin “amaryar siyasa ta yanzu”, inda ya ce ’yan siyasa da yawa na rubibin shiga jam’iyyar.

Ya ce akwai sanatoci, gwamnoni, da ’yan majalisa da dama da ke shirin komawa APC.

“APC jam’iyya ce mai maraba da kowa,” in ji shi.

“Ba sai ka kasance daga cikin waɗanda suka kafa jam’iyyar ba kafin ka samu ci gaba a cikinta. Ni shaida ne a kan hakan. Da zarar ka shiga, kana da cikakken haƙƙi da damar da kowa yake da ita. Wannan shi ne tsarin jam’iyyarmu.”

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sojojin HKI Sun Shiga Cikin Yankin Qunaidhara Na Kasar Syria
  • Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja
  • Wasu jiga-jigan ADC za su dawo jam’iyyarmu — Shugaban APC
  • Wasu jiga-jigan ADC za su dawo jam’iyyarmu — Shugaban Jam’iyyar APC
  • HOTUNA: Al’ummar Jihar Neja sun yi addu’o’in neman zaman lafiya
  • Iran: Kauyuka Guda Uku Na Kasar Sun Shiga Cikin Kauyukan Yawon Shakatawa Ta Duniya
  • NSCDC Ta Kama Wadanda Ake Zargi Da Lalata Kadarorin Gwamnati A Kaduna
  • Gwamnatin Kano Ta Kai Ƙarar Ganduje Da Wasu Kotu Kan Zargin Almundahanar N4.4bn
  • 2027: Peter Obi Ya Shiga Rudani Kan Jam’iyyar Da Zai Tsaya Takara
  • Yadda ‘Yan Bindiga Ke Zafafa Hare-hare A Jihohin Arewa Maso Yamma