Aminiya:
2025-08-01@02:04:37 GMT

An naɗa mace ta farko mai magana da yawun rundunar sojin Nijeriya

Published: 16th, April 2025 GMT

An naɗa mace ta farko a matsayin mai magana da yawun rundunar sojin Nijeriya.

Appolonia Anaele mai muƙamin Laftanar Kanar ce za ta karɓi muƙamin daga hannun Manjo-Janar Onyema Nwachukwu.

An taƙaita zirga-zirgar babura da haramta kiwon dare a Filato Matashin da ya yi iƙirarin kashe mutane ya kai kansa ofishin ’yan sanda a Kano

Bayanai sun ce muƙamin nata zai fara ne a ranar Talata 22, ga watan Afrilun da muke ciki.

Shekaru sama da 50 ke nan da kafa rundunar sojin Nijeriya, kuma babu wata mace da ta taɓa riƙe wannan muƙami.

Duk da cewa kawo yanzu tana a matsayin mai riƙon muƙami ne, amma duk da haka wannan shi ne karon farko.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Manjo Janar Onyema Nwachukwu Rundunar Sojin Kasa ta Najeriya

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamna Lawal Ya Naɗa Sabon Sarkin Gusau

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya amince da naɗa Alhaji Abdulkadir Ibrahim Bello a matsayin sabon Sarkin Gusau kuma Sarkin Katsina na Masarautar Gusau.

Sakataren Gwamnatin Jihar Zamfara, Malam Abubakar Mohammad Nakwada ne ya sanar da hakan, inda ya bayyana cewa an yi naɗin ne bisa ga shawarwarin da masu zaɓen sarakuna na masarautar Gusau suka bayar, tare da bin al’ada da dokokin da suka dace.

A wata sanarwa da mai taimakawa na musamman kan harkokin yaɗa labarai a ofishin Sakataren Gwamnatin Jihar Zamfara, Sulaiman Ahmad Tudu, ya fitar, ya ce sabon Sarkin, Alhaji Abdulkadir Ibrahim Bello, shi ne ɗa na farko ga marigayi Sarki, kuma kafin naɗin nasa yana riƙe da mukamin Bunun Gusau.

Alhaji Abdulkadir ya hau karagar mulki a matsayin Sarkin Gusau na 16, bayan rasuwar mahaifinsa, Mai Martaba Dokta Ibrahim Bello, wanda ya rasu a ranar 25 ga Yulin 2025, bayan shafe shekara goma yana mulki.

Yayin da yake taya sabon sarkin murna, Gwamna Lawal ya bukace shi da ya ci gaba da rike kyakkyawar jagoranci da mutumtaka da aka san kakanninsa da shi, musamman kasancewarsa  tsatson Malam Sambo Dan Ashafa.

Gwamnan ya kuma bukaci sabon Sarkin da ya kasance jajirtacce wajen kawo haɗin kai, zaman lafiya da cigaba, tare da ƙarfafa hadin kai  a ciki da wajen masarautar Gusau.

 

Daga Aminu Dalhatu

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Salisu Yusuf Ya Ajiye Aikinsa Na Kocin Nasarawa United
  • Gine-gine 8 Sun Ruguje, Makabarta Ta Nutse A Wata Sabuwar Ambaliyar Ruwa A Borno
  • Gidauniyar ‘Ya’yan Sarakunan Arewa Sun Marawa Sarkin Musulmi A Matsayin Shugaban Majalisar Sarakuna
  • Rashin Nasarar DPP A Zagayen Farko Na Kuri’ar Kiranye Ya Nuna Rashin Amincewar Al’ummar Taiwan Da Salon Mulkin Jami’yyar
  • Gwamnan Kaduna Ya Sauke Kwamishinan Yaɗa Labarai, Ya Maye Gurbinsa Da Maiyaki
  • Gwamna Namadi Ya Naɗa Shugabannin Hukumar Hisbah Ta Jihar Jigawa
  • Sojojin Sin Sun Bi Sahun Shiga Ayyukan Ba Da Agajin Ambaliyar Ruwa
  • Gwamna Lawal Ya Naɗa Sabon Sarkin Gusau
  • ‘Yan Sanda A Kano Sun Kama Kasurgumin Dan Fashin Nan Barga Da Wasu Mutum 14
  • Gwamnan Zamfara Ya Naɗa Abdulkadir Ibrahim A Matsayin Sabon Sarkin Katsinan Gusau Na 16