An naɗa mace ta farko mai magana da yawun rundunar sojin Nijeriya
Published: 16th, April 2025 GMT
An naɗa mace ta farko a matsayin mai magana da yawun rundunar sojin Nijeriya.
Appolonia Anaele mai muƙamin Laftanar Kanar ce za ta karɓi muƙamin daga hannun Manjo-Janar Onyema Nwachukwu.
An taƙaita zirga-zirgar babura da haramta kiwon dare a Filato Matashin da ya yi iƙirarin kashe mutane ya kai kansa ofishin ’yan sanda a KanoBayanai sun ce muƙamin nata zai fara ne a ranar Talata 22, ga watan Afrilun da muke ciki.
Shekaru sama da 50 ke nan da kafa rundunar sojin Nijeriya, kuma babu wata mace da ta taɓa riƙe wannan muƙami.
Duk da cewa kawo yanzu tana a matsayin mai riƙon muƙami ne, amma duk da haka wannan shi ne karon farko.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Manjo Janar Onyema Nwachukwu Rundunar Sojin Kasa ta Najeriya
এছাড়াও পড়ুন:
NAJERIYA A YAU: Dalilin karyewar farashin shinkafa a kasuwannin Najeriya
More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba
Rahotanni suna nuna cewa farashin shinkafa, ɗaya daga cikin nau’ukan abincin da ’yan Najeriya suka fi ci, ya karye a wasu sassan ƙasar.
Sauyin farashin ya sa ana tambayoyi — shin me ya haifar da wannan sauyi? Kuma me hakan ke iya haifarwa a rayuwar talaka?
NAJERIYA A YAU: “Dalilin da muke sauya sheƙa zuwa jam’iyya mai mulki” DAGA LARABA: Dalilan Rashin Wutar Lantarki A Wasu Jihohin ArewaA kan wannan sauyi da dalilansa ne shirin Najeriya a Yau na wannan lokaci zai yi nazari.
Domin sauke shirin, latsa nan