MDD Ta Bukaci Taimako Dangane Rikicin Sudan Wanda Ya Isa Kasar Chadi
Published: 12th, April 2025 GMT
Shugaban hukumar yan gudun hijira na MDD Filippo Grandi wanda ya ziyarce sansanonin yan gudun hijira na kasar Sudan a Chadi ya bayyana cewa akwai bukatar kasashen duniya su taimaka don kula da bukatun yan kasar sudan wadanda suke gudun hijira a kasar Chadi.
Grandi ya kara da cewa akwai bukatar agaji da gaggawa zuwa kasar Chadin da kuma sauran kasashen da suke daukar nauyin yan gudun hijira na sudan.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: yan gudun hijira
এছাড়াও পড়ুন:
Yaukaka Zumunci Da Makwabta A Aikace Tsakanin Sin Da Malaysiya
Kasar Sin ta kuma nuna aniyarta ta lale marhabin ga shigar da karin kayan amfanin gona masu inganci na Malaysiya zuwa katafariyar kasuwarta inda ta kuma nemi kasar ta Malaysiya ta kara bai wa kamfanoninta kwarin gwiwar zuba jari a kasar.
Kasar Malaysiya ta san irin alheran da kamfanonin Sin suke ci gaba da kawo mata wajen raya tattalin arziki da ci gaban masana’antunta. Wannan ya sa Sultan Ibrahim ya bayyana cewa, Malaysiya tana dora fifiko sosai a kan zumuncinta da kasar Sin, kuma za su ci gaba da yin aiki tare domin samun nasara ga kowane bangare, tare da kara matsa kaimi ga gina al’umma mai makoma ta bai-daya a karkashin ingantattun manyan tsare-tsare kuma a duk wani sauyi da za a iya samu a duniya.
Tabbas, Malaysiya tana shaida irin ci gaban da kamfanonin kasar Sin suke kawo mata. Babban jami’in kasuwanci na tashar teku ta Kuantan, Mazlim Husin, ya bayyana yadda yankin masana’antu na hadin gwiwar Sin da Malaysiya (MCKIP) ya bude sabon babi ga bunkasa ci gaban Kuantan tun bayan kaddamar da shi a shekarar 2013. Kafa kamfanin mulmula karafa na Alliance Steel ya kara wa sauran kamfanoni kwarin gwiwar bude rassansu a yankin masana’antun wanda ya habaka samar da ayyukan yi da walwalar al’ummar wurin.
Kasar Sin ta kasance kasar da ta fi kowace kasa zuba jari a Malaysiya, inda ko a bara ta zuba kimanin dala biliyan 6.4 a kasar wanda ya kai kaso 16 na kudin shigar da Malaysiya ke samu daga zuba jarin kasashen waje kuma ana sa ran ya samar da sabbin guraben ayyukan yi 20,000.
Kazalika, wani jami’in ofishin jakadancin Malaysiya mai kula da zuba jari dake Guangzhou, Safwan Nizar Johari ya tabbatar da cewa akwai karin kamfanonin Sin dake zuba jari a kasar musamman a bangaren motocin sabbin makamashi, wanda hakan na nuna zumunci mai kyau tsakanin Sin da makwabtanta.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp