Amurka Ta Kai Hare-hare A Yankunan Kasa Yemen
Published: 11th, April 2025 GMT
Rahotanni daga kasar Yemen sun ambaci cewa jiragen yakin Amurka sun kai jerin hare-hare a yankuna mabanbanta na kasar Yemen da su ka hada da birnin San’aa.
Tashar talabijin din al-masirah ta ambaci cewa; jiragen yakin Amurka sun kai hare-haran ne har sau 7, biyu a cikin yankin Hamadan, da Banu Hashish sai kuma babban birnin kasar Sanaa.
Kawo ya zuwa babu cikakken bayani akan adadin wadanda su ka jikkata ko shahada sanadiyyar wannan harin.
Amurkan dai tana kai wa Yemen hare-hare ne saboda taimakawa HKI a yaki, da kokarin hana dakarun Ansarullah ci gaba da kai hare-hare akan manufofin HKI.
A daren jiya Alhamsi shugaban kungiyar Ansarullah Sayyid Abdulmalik al-Husi ya bayyana cewa; hare-haren da Amurka take kai musu ba su yi wa makaman da suke da su illa ba,kuma akasin haka suna kara musu azama ne.
Sojojin Yemen suna kai hare-hare a HKI saboda yin matsin lamba akan HKI ta dakatar da hare-haren da take kai wa Gaza, sannan kuma da mayar da martani akan jiragen dakon jiragen yaki na Amurka a tekun “Red Sea’ bayan da su ka fara kai wa Yemen din hari.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: hare hare a
এছাড়াও পড়ুন:
Jamhuriyar Nijar Da China Sun Kusa Warware Sabanin Dake Tsakaninsu Akan Batun Man Fetur
Tashar talabijin din ‘almayadin’ ta ce, wata majiya mai karfi a jamhuriyar Nijar ta ce; An kusa kusa kawo karshen sabanin dake tsakanin gwamnatin jamhuriyar Nijar da kamfanonin kasar China da suke aiki a fagen hako da tace man fetur, bayan da bangarorin biyu su ka yi nisa a tattaunawar da suke yi.
Sauyin da aka sami shi ne amincewar kamfanin man fetur na kasar China ( CNPC) da sauya tsohon manajan dake tafiyar da ayyuka a Nijar, da wani sabo kamar yadda gwamnatin Yamai ta bukata.
Su ma kamfanonin WAPCO da SORAZ za su dauki sabbin matakai na samar da sauye-sauye a cikin harkokin tafiyar da su.
Ana sa ran cewa, sabbin matakan da kamfanoni na China da Nijar suke dauka zai bude sabon shafi a alakar kasashen biyu da za ta kare manufofin kowane bangare.