HausaTv:
2025-12-12@01:19:44 GMT

 Amurka Ta Kai Hare-hare A Yankunan Kasa Yemen

Published: 11th, April 2025 GMT

Rahotanni daga kasar Yemen sun ambaci cewa jiragen yakin Amurka sun kai jerin hare-hare a yankuna mabanbanta na kasar Yemen da su ka hada da birnin San’aa.

Tashar talabijin din al-masirah ta ambaci cewa; jiragen yakin Amurka sun kai hare-haran ne har sau 7, biyu a cikin yankin Hamadan, da Banu Hashish sai kuma babban birnin kasar Sanaa.

Kawo ya zuwa babu cikakken bayani akan adadin wadanda su ka jikkata ko shahada sanadiyyar wannan harin.

Amurkan dai tana kai wa Yemen hare-hare ne saboda taimakawa HKI a yaki, da kokarin hana dakarun Ansarullah ci gaba da kai hare-hare akan manufofin HKI.

A daren jiya Alhamsi shugaban kungiyar Ansarullah Sayyid Abdulmalik al-Husi ya  bayyana cewa; hare-haren da Amurka take kai musu ba su yi wa makaman da suke da su illa ba,kuma akasin haka suna kara musu azama ne.

Sojojin Yemen suna kai hare-hare a HKI saboda yin matsin lamba akan HKI ta dakatar da hare-haren da take kai wa Gaza, sannan kuma da mayar da martani akan jiragen dakon jiragen yaki na Amurka a tekun “Red Sea’ bayan da su ka fara kai wa Yemen din hari.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: hare hare a

এছাড়াও পড়ুন:

Kasashen ECOWAS sun rage kudin sufirin jiragan sama a tsakaninsu  

Kungiyar Raya Tattalin Arzikin Kasashen Yammacin Afirka (ECOWAS) ta amince da wasu sauye-sauye da nufin rage tsadar tafiye-tafiyen jiragen sama a tsakanin kasashe mambobin kungiyar.

A cikin wata sanarwa da ta fitar a ranar Laraba, Hukumar ECOWAS ta sanar da cewa shugabannin kasashe da gwamnatoci, a taronsu a Abuja, sun amince da wata manufa ta kawar da harajin sufurin jiragen sama da kuma rage kudin tikitan jirgin sama da kashi 25 cikin 100, wanda zai fara aiki daga ranar 1 ga Janairu, 2026.

Hukumar ta bayyana cewa wannan matakin ya biyo bayan shekaru da dama na koma baya a fannin sufurin jiragen sama a Yammacin Afirka, galibi saboda yawan haraji, wanda ke hana bukatar tafiye-tafiye da kuma raunana jarin da ake zubawa a fannin tafiye tafiye na jiragen sama.

Nazarin da ECOWAS da Tarayyar Afirka, da Kungiyar Jiragen Sama ta Afirka (AFRAA), da Kungiyar Sufurin Jiragen Sama ta Duniya (IATA) suka gudanar sun nuna cewa Yammacin Afirka ya kasance daya daga cikin yankuna mafi tsada don tafiye-tafiyen jiragen sama, inda fasinjoji wani lokacin ke biyan har zuwa caji 66 daban-daban, yayin da kamfanonin jiragen sama ke fuskantar kudade daban-daban.

ECOWAS ta yi gargadin cewa hauhawar farashin jiragen sama na hana tafiye-tafiyen fasinjoji, rage yawan yawon bude ido, kawo cikas ga ciniki, da kuma lalata ajandarta ta ‘yancin zirga-zirga da hadewar yankuna.

A cewar sanarwar, amincewa da Dokar na da nufin magance wadannan kalubalen da kuma daidaita yankin da ka’idojin jiragen sama na duniya.

Kungiyar ta jaddada cewa ya kamata wadannan gyare-gyare su taimaka wajen rage farashin tikiti, kara yawan fasinjoji, karfafa kamfanonin jiragen sama na yankin, bunkasa ayyukan filayen jiragen sama da kuma samar da karin damammaki na tattalin arziki ga al’ummomin da ke karbar bakuncin.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Dakarun IRGC 3 Sun Yi Shahada A wani Harin Ta’addanci A Kudancin Kasar Iran December 11, 2025 Hamas: HKI Tana Ci Gaba Da Keta Bangaren Farko Na Yarjejeniyar Tsagaita Wuta A Gaza December 11, 2025 Iran Ta Yi Tir Da Yanke Tallafin Da MDD Take Bawa Yan Gudun Hijiran Afganistan December 11, 2025 Ansarallah: Dole Ne Kasar Yemen Ta Tsarin Musulunci Na Kaiwa Ga Daukaka December 11, 2025 Shugaban Iran Ya Isa Astana Babban Birnin Kazakhstan December 11, 2025 ECOWAS ta bukaci waware batutuwa na siyasa ta hanyoyin lumana a yammacin Afirka December 11, 2025 Reuters: Amurka na matsa lamba kan kotun ICC don janye bincike kan yakin  Gaza da Afghanistan December 11, 2025 Ghana ta yi Allah wadai da cin mutuncin ‘yan kasarta da ke balaguro a Isra’ila December 11, 2025 Sakamkon Jin Ra’ayi: Yawancin Amurkawa na adawa da kai hari kan Venezuela December 11, 2025 Hamas Ta yi Tir Da Sabbin Matsugunan Yahudawa Da Isra’ila Ke yi A Yankunan Da Ta Mamaye December 10, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kasashen ECOWAS sun rage kudin sufirin jiragan sama a tsakaninsu  
  • Ansarallah: Dole Ne Kasar Yemen Ta Tsarin Musulunci Na Kaiwa Ga Daukaka
  • Shugaban Kasar Iran Yace Mata Su ne Ginshin Gina Makomakar Kowacce Kasa
  • Hamas Ta yi Tir Da Sabbin Matsugunan Yahudawa Da Isra’ila Ke yi A Yankunan Da Ta Mamaye
  • Rikicin Iyakar Thailand da Cambodia Ya Tilasta wa Dubban Mutane Barin Muhallansu
  • ‘Yan Ta’adda Sun Kai Hare-Hare Kan Sojojin Pakistan Sun Kuma Kashe 6 Daga Cikinsu
  • Kasar China Ta Zartar Da Hukuncin Kisa Akan Wani Babban Jami’in Banki
  • Isra’ila ta sake kai hare-haren a kudancin Lebanon
  • Yara masara zuwa makaranta barazana ne ga kasa — Shettima
  • Nigeria Ta Aike Da Jiragen Yaki Zuwa Kasar Benin Domin Dakile Yunkurin Juyin Mulki