Amurka Ta Kai Hare-hare A Yankunan Kasa Yemen
Published: 11th, April 2025 GMT
Rahotanni daga kasar Yemen sun ambaci cewa jiragen yakin Amurka sun kai jerin hare-hare a yankuna mabanbanta na kasar Yemen da su ka hada da birnin San’aa.
Tashar talabijin din al-masirah ta ambaci cewa; jiragen yakin Amurka sun kai hare-haran ne har sau 7, biyu a cikin yankin Hamadan, da Banu Hashish sai kuma babban birnin kasar Sanaa.
Kawo ya zuwa babu cikakken bayani akan adadin wadanda su ka jikkata ko shahada sanadiyyar wannan harin.
Amurkan dai tana kai wa Yemen hare-hare ne saboda taimakawa HKI a yaki, da kokarin hana dakarun Ansarullah ci gaba da kai hare-hare akan manufofin HKI.
A daren jiya Alhamsi shugaban kungiyar Ansarullah Sayyid Abdulmalik al-Husi ya bayyana cewa; hare-haren da Amurka take kai musu ba su yi wa makaman da suke da su illa ba,kuma akasin haka suna kara musu azama ne.
Sojojin Yemen suna kai hare-hare a HKI saboda yin matsin lamba akan HKI ta dakatar da hare-haren da take kai wa Gaza, sannan kuma da mayar da martani akan jiragen dakon jiragen yaki na Amurka a tekun “Red Sea’ bayan da su ka fara kai wa Yemen din hari.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: hare hare a
এছাড়াও পড়ুন:
Amurka za ta hana ’yan Najeriyar da ake zargi da yi wa Kiristoci kisan kiyashi biza
Ƙasar Amurka ta yi barazanar sanya takunkumin izinin shiga kasarta ga ’yan Najeriyar da aka gano suna ɗaukar nauyi ko goyon bayan ayyukan da ke take ’yancin yin addini da yi wa Kiristoci kisan kiyashi.
Sakataren Harkokin Wajen Amurka, Marco Rubio, ya bayyana haka a cikin wani saƙo da ya wallafa a shafin X, inda ya ce Amurka na ɗaukar mataki mai ƙarfi kan munanan ayyuka da tashin hankali da ake yi wa Kiristoci a Najeriya da sauran sassan duniya.
NAPTIP ta daƙile yunƙurin safarar mutum 7 daga Kano zuwa Saudiyya Na gana da Tinubu kan Kanu ba batun sauya sheƙa ba — Gwamnan Abia“Ma’aikatar Harkokin Wajen Amurka (@StateDept) za ta takaita bizar Amurka ga waɗanda suka san da gaske suna jagoranta, ba da izini, ɗaukar nauyi, goyon baya, ko aiwatar da take hakkin ’yancin yin addini. Wadannan manufofin biza sun shafi Najeriya da sauran gwamnatoci ko mutane da ke zaluntar jama’a saboda addininsu,” in ji Rubio.
Maganganun Rubio sun zo ne kwana guda bayan ’yan majalisar Amurka sun gudanar da taron jin ra’ayi a Washington tare da masana kan ’yancin yin addini da dangantakar ƙasashen waje domin tattauna ƙaruwa da tashin hankali a Najeriya da kuma “zaluncin da aka fi karkata ga Kiristoci.”
Taron majalisar ya kasance wani ɓangare na bincike da ake ci gaba da yi kan batun, bisa umarnin Shugaban Ƙasa Donald Trump.