HausaTv:
2025-12-14@14:46:25 GMT

 Amurka Ta Kai Hare-hare A Yankunan Kasa Yemen

Published: 11th, April 2025 GMT

Rahotanni daga kasar Yemen sun ambaci cewa jiragen yakin Amurka sun kai jerin hare-hare a yankuna mabanbanta na kasar Yemen da su ka hada da birnin San’aa.

Tashar talabijin din al-masirah ta ambaci cewa; jiragen yakin Amurka sun kai hare-haran ne har sau 7, biyu a cikin yankin Hamadan, da Banu Hashish sai kuma babban birnin kasar Sanaa.

Kawo ya zuwa babu cikakken bayani akan adadin wadanda su ka jikkata ko shahada sanadiyyar wannan harin.

Amurkan dai tana kai wa Yemen hare-hare ne saboda taimakawa HKI a yaki, da kokarin hana dakarun Ansarullah ci gaba da kai hare-hare akan manufofin HKI.

A daren jiya Alhamsi shugaban kungiyar Ansarullah Sayyid Abdulmalik al-Husi ya  bayyana cewa; hare-haren da Amurka take kai musu ba su yi wa makaman da suke da su illa ba,kuma akasin haka suna kara musu azama ne.

Sojojin Yemen suna kai hare-hare a HKI saboda yin matsin lamba akan HKI ta dakatar da hare-haren da take kai wa Gaza, sannan kuma da mayar da martani akan jiragen dakon jiragen yaki na Amurka a tekun “Red Sea’ bayan da su ka fara kai wa Yemen din hari.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: hare hare a

এছাড়াও পড়ুন:

Amurka ta kama jirgin ruwan dakon man Najeriya

Amurka ta kama wani katafaren jirgin ruwan dakon man Najeriya kan zargin safarar ɗanyen mai na sata.

Jami’an tsaron Amurka sun kama jirgin mai suna Super Tanker, mai lamba 9304667, ne, bayan sun gano cewa ya yi basaja, inda ya maƙala tutar wata kasa daban maimakon ta Najeriya yayin shigarsa ruwan Amurka.

Wannan ya haifar da shakku kan sahihancin jirgin da ma wadanda ke tafiyar da shi. Daga bisani kuma aka gano cewa ba ya cikin tsarin jiragen da ake tsammani a hukumance.

Hukumomin Amurka sun ƙaddamar da bincike kan jirgin, wanda ake hasashen zai bankaɗo badaƙalar safarar man sata da fataucin miyagun ƙwayoyi da ayyukan ’yan fashin teku da ke shafar ƙasashe da dama.

An shafe shekaru ana magana ba kan matsalar yawan satar ɗanyen mai ayankin Neja Delta mai arzikin mai ya zame wa al’umma tamkar tamkar masifa.

Bayanan kama jirgin

Jirgin mallakin wani babban ɗan kasuwa a Najeriya mai kamfanin Thomarose Global Ventures, yanzu haka yana tsare a hannun jami’an tsaron Amurka.

Bayanan farko sun nuna cewa an fara gudanar da bincike kan alakar jirgin da safarar muggan ƙwayoyi da kuma harkokin barayin kan teku, musamman a zirin Tekun Gunea da ke addabar kasashe da dama, ciki har da Najeriya, Kamaru, Sao Tome da Ghana.

Alƙaluman da aka fitar a watan Nuwamba, shekarar 2025, sun nuna cewa Najeriya ta yi asarar kimanin dala biliyan 300 sakamakon satar ɗanyen mai a ciki da wajen kasar.

Wannan satar mai ba wai kawai tana jawo asarar kudi ba, har ma tana barin baya da kurar gurbata muhalli, lamarin da ke ci gaba da kassara yankin mai arzikin mai na Niger Delta.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shugaba Tinubu Ya Karrama Shugaban NPA Da Lambar Yabo Ta Musamman
  • Dantsoho Ya Yaba Wa Ƙoƙarin Oyetola Na Dawo Da Nijeriya Tsarin Sufurin Jiragen Ruwa Na Duniya
  • Sojoji sun daƙile harin ’yan ta’adda a Borno
  • Amurka ta kama jirgin ruwan dakon man Najeriya
  • Hamas Ta Ce Ci Gaba Da Kai Hare-Haren Isra’ila Ya Nuna Gazawar Tsarin Duniya Na Dakatar Da Ita.
  • Iran Ta soki Kasashe Masu Karfi Na Bawa Isra’ila Dama Ta Musamman Wajen Kai Hare-hare
  • Osimhen ya lashe kyautar gwarzon ɗan wasan bana na Turkiyya
  • Duniyarmu A Yau: Iran Da Amurka A Yakin Kwanaki 12 Wa Ya Sami Nasara
  • Sojoji sun kashe ’yan bindiga 3 a Binuwai
  • Taron Abuja kan Tattaunawakan Tattalin Arziki Kasa- “Akwai yiyuwar tattalin arzikin kasa zai murmure a shekarar 2026”