HausaTv:
2025-12-13@22:08:24 GMT

 Amurka Ta Kai Hare-hare A Yankunan Kasa Yemen

Published: 11th, April 2025 GMT

Rahotanni daga kasar Yemen sun ambaci cewa jiragen yakin Amurka sun kai jerin hare-hare a yankuna mabanbanta na kasar Yemen da su ka hada da birnin San’aa.

Tashar talabijin din al-masirah ta ambaci cewa; jiragen yakin Amurka sun kai hare-haran ne har sau 7, biyu a cikin yankin Hamadan, da Banu Hashish sai kuma babban birnin kasar Sanaa.

Kawo ya zuwa babu cikakken bayani akan adadin wadanda su ka jikkata ko shahada sanadiyyar wannan harin.

Amurkan dai tana kai wa Yemen hare-hare ne saboda taimakawa HKI a yaki, da kokarin hana dakarun Ansarullah ci gaba da kai hare-hare akan manufofin HKI.

A daren jiya Alhamsi shugaban kungiyar Ansarullah Sayyid Abdulmalik al-Husi ya  bayyana cewa; hare-haren da Amurka take kai musu ba su yi wa makaman da suke da su illa ba,kuma akasin haka suna kara musu azama ne.

Sojojin Yemen suna kai hare-hare a HKI saboda yin matsin lamba akan HKI ta dakatar da hare-haren da take kai wa Gaza, sannan kuma da mayar da martani akan jiragen dakon jiragen yaki na Amurka a tekun “Red Sea’ bayan da su ka fara kai wa Yemen din hari.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: hare hare a

এছাড়াও পড়ুন:

Osimhen ya lashe kyautar gwarzon ɗan wasan bana na Turkiyya

Ɗan wasan gaban Ƙungiyyar Ƙwallon Ƙafa ta Galatasaray ɗan asalin Najeriya, Victor Osimhen ya lashe kyautar gwarzon ɗan wasa na bana, a bikin bayar da kyaututtuka ta GQ Türkiye na maza na 2025.

Ɗan wasan mai shekara 26 ya sami kyautar mafi girma a bikin da aka gudanar mai ban sha’awa.

Matatar man Dangote ta rage farashin fetur zuwa N699 Sojoji sun kashe ’yan bindiga 3 a Binuwai

Ya sami kyautar ne saboda rawar da ya taka a Galatasaray a kakar wasa ta bara, inda ya zura ƙwallaye 37 kuma ya taimaka wajen zura ƙwallo sau bakwai a wasanni 41, wanda hakan ya sa Galatasaray ta lashe gasar Turkiya.

Osimhen ya karya tarihin Galatasaray na zama ɗan wasan da ya fi tsada a tarihin Ƙungiyar bayan ya koma akan kuɗi Yuro miliyan 75 daga Napoli.

Osimhen ya ci gaba da yin abin a yaba a wannan kakar, inda ya riga ya zura ƙwallaye 11 a wasanni 14 da ya bugawa ƙungiyar da ke birnin Istanbul.

Galatasaray na matsayi na ɗaya akan teburin babbar gasar ƙwallon ƙafa ta ƙasar Turkiyya da maki 36 a wasanni 15 da ta buga yayin da Trabzonspor ke matsayi na biyu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shugaba Tinubu Ya Karrama Shugaban NPA Da Lambar Yabo Ta Musamman
  • Sojoji sun daƙile harin ’yan ta’adda a Borno
  • Amurka ta kama jirgin ruwan dakon man Najeriya
  • Hamas Ta Ce Ci Gaba Da Kai Hare-Haren Isra’ila Ya Nuna Gazawar Tsarin Duniya Na Dakatar Da Ita.
  • Iran Ta soki Kasashe Masu Karfi Na Bawa Isra’ila Dama Ta Musamman Wajen Kai Hare-hare
  • Osimhen ya lashe kyautar gwarzon ɗan wasan bana na Turkiyya
  • Duniyarmu A Yau: Iran Da Amurka A Yakin Kwanaki 12 Wa Ya Sami Nasara
  • Sojoji sun kashe ’yan bindiga 3 a Binuwai
  • Taron Abuja kan Tattaunawakan Tattalin Arziki Kasa- “Akwai yiyuwar tattalin arzikin kasa zai murmure a shekarar 2026”
  • Ansarallah: Dole Ne Kasar Yemen Ta Tsarin Musulunci Na Kaiwa Ga Daukaka