Leadership News Hausa:
2025-04-30@19:27:39 GMT

Me Yakin Harajin Fito Zai Haifar Wa Amurka?

Published: 5th, April 2025 GMT

Me Yakin Harajin Fito Zai Haifar Wa Amurka?

Gwamnatin kasar Amurka ta sanar da sanya harajin fito na ramuwar gayya kan dukkan kawayen cinikayyarta a ranar 2 ga wata, inda kasar Sin ta mayar da martani nan take, da zummar kiyaye halastaccen hakkinta. Daga baya a ranar 3 ga wata, Sin ta sanar da wasu jerin matakai, ciki har da kara sanya harajin fito na kaso 34% kan dukkan kayayyakin da ake shigowa da su daga Amurka, da shigar da kara a gaban kungiyar cinikayya ta duniya WTO, kan matakin da Amurka ta dauka, gami da kara wasu kamfanonin Amurka a cikin jerin sunayen kamfanonin da ta dauki matakin hana fitar da kayayyaki zuwa kasashen waje a kansu, matakan da suka janyo babbar raguwar darajar takardun hannayen jari a Amurka.

Sin da Amurka za su iya cin gajiya daga hadin-gwiwarsu, amma dukkansu za su gamu da hasara in sun yi fada da juna. Manazarta na ganin cewa, matakin Amurka na kakaba harajin fito na ramuwar gayya, zai iya haifar da illa ga tattalin arzikin kasar Sin a cikin wani gajeren lokaci. Amma ganin yadda kasar ta Sin ta shawo kan sabanin kasuwanci sau da dama, dorewar tattalin arzikin kasar Sin na kara inganta. Kazalika, kwararan shaidu sun riga sun nuna cewa, kara sanya harajin fito da Amurka ta yi, ba zai daidaita matsalar rashin daidaiton cinikayya ba, sai dai kara illata tattalin arzikin kanta.

A halin yanzu, sassan kasa da kasa na kara yin mu’amala tsakanin juna, har ma tattalin arzikin duniya na kara dunkulewa waje guda. Ra’ayin daukar matakai na kashin kai, da ra’ayin kariyar cinikayya, sam ba za su samu goyon-baya ba. Ya dace Amurka ta gyara kura-kuranta, ta dakatar da yin amfani da batun kakaba harajin fito wajen tilasta wa sauran kasashe. Sa’an nan, ya dace sassan kasa da kasa su hada gwiwa, don adawa da irin bangaranci da babakeren da Amurka ta nuna, da ci gaba da kiyaye tsarin cudanyar kasa da kasa a fannin kasuwanci. Babu tantama, ba wanda zai yi nasara daga yakin harajin fito da yakin cinikayya. (Murtala Zhang)

 

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: tattalin arzikin harajin fito

এছাড়াও পড়ুন:

Lebanon:  Isra’ila Ta Kai Hari Akan Unguwar Dhahiya A Birnin Beirut

Jiragen yakin HKI sun kai hari a yankin Hangara dake unguwar “Dhahiya” a cikin birnin Beirut. Yankin da jiragen yakin na ‘yan sahayoniya su ka kai wa harin, yana cike da mutane da kuma makarantu biyu.

Jiragen yakin na HKI sun harba makamai masu linzami 3, da hakan ya haddasa tashin gobara.

A sanadiyyar wannan harin, an sami shahidi daya,yayin da wasu da dama su ka jikkata.

A ranar 1 ga watan Aprilu ma dai sojojin HKI sun kai wani harin a unguwar Dhahiya wanda ya yi sanadiyyar shahadar mutane 4 da kuma jikkata wasu da dama.

Tun bayan tsagaita wutar yaki a ranar 27 ga watan Aprilu 2025, HKI ta keta wutar yakin fiye da 2000.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Xi Ya Jaddada Muhimmancin Tsara Nagartaccen Shirin Raya Tattalin Arziki Da Zamantakewar Al’umma Tsakanin 2026-2030
  • Nazarin CGTN: Ana Kara Bayyana Rashin Gamsuwa Da Sabuwar Gwamnatin Amurka Daga Ciki Da Wajen Kasar
  • Gwamna Namadi Ya Nada Aisha Mujaddadi Sabuwar Shugabar Hukumar InvestJigawa
  • Karin Wata Kasa Da Bai San Ta Ba A Doron Duniya
  • Nijeriya Na Ke Yi Wa Biyayya Ba Wani Ko Jam’iyya Ba – El-Rufai
  • Shugaban Putin Na Rasha Ya Bada Sanarwan Tsagaita Wuta Da Ukraine Na Sa’o’ii 72
  • Sin Na Maraba Da Karin Abokai Daga Kasa Da Kasa Su Ziyarci Kasar
  • Jiragen Yakin Amurka Sun Kashe Mutane Da Dama A lardin Sa’ada Na Kasar Yemen
  • Lebanon:  Isra’ila Ta Kai Hari Akan Unguwar Dhahiya A Birnin Beirut
  • Kasar Sin Za Ta Samar Da Dokar Da Ta Shafi Raya Kasa