Me Yakin Harajin Fito Zai Haifar Wa Amurka?
Published: 5th, April 2025 GMT
Gwamnatin kasar Amurka ta sanar da sanya harajin fito na ramuwar gayya kan dukkan kawayen cinikayyarta a ranar 2 ga wata, inda kasar Sin ta mayar da martani nan take, da zummar kiyaye halastaccen hakkinta. Daga baya a ranar 3 ga wata, Sin ta sanar da wasu jerin matakai, ciki har da kara sanya harajin fito na kaso 34% kan dukkan kayayyakin da ake shigowa da su daga Amurka, da shigar da kara a gaban kungiyar cinikayya ta duniya WTO, kan matakin da Amurka ta dauka, gami da kara wasu kamfanonin Amurka a cikin jerin sunayen kamfanonin da ta dauki matakin hana fitar da kayayyaki zuwa kasashen waje a kansu, matakan da suka janyo babbar raguwar darajar takardun hannayen jari a Amurka.
Sin da Amurka za su iya cin gajiya daga hadin-gwiwarsu, amma dukkansu za su gamu da hasara in sun yi fada da juna. Manazarta na ganin cewa, matakin Amurka na kakaba harajin fito na ramuwar gayya, zai iya haifar da illa ga tattalin arzikin kasar Sin a cikin wani gajeren lokaci. Amma ganin yadda kasar ta Sin ta shawo kan sabanin kasuwanci sau da dama, dorewar tattalin arzikin kasar Sin na kara inganta. Kazalika, kwararan shaidu sun riga sun nuna cewa, kara sanya harajin fito da Amurka ta yi, ba zai daidaita matsalar rashin daidaiton cinikayya ba, sai dai kara illata tattalin arzikin kanta.
A halin yanzu, sassan kasa da kasa na kara yin mu’amala tsakanin juna, har ma tattalin arzikin duniya na kara dunkulewa waje guda. Ra’ayin daukar matakai na kashin kai, da ra’ayin kariyar cinikayya, sam ba za su samu goyon-baya ba. Ya dace Amurka ta gyara kura-kuranta, ta dakatar da yin amfani da batun kakaba harajin fito wajen tilasta wa sauran kasashe. Sa’an nan, ya dace sassan kasa da kasa su hada gwiwa, don adawa da irin bangaranci da babakeren da Amurka ta nuna, da ci gaba da kiyaye tsarin cudanyar kasa da kasa a fannin kasuwanci. Babu tantama, ba wanda zai yi nasara daga yakin harajin fito da yakin cinikayya. (Murtala Zhang)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: tattalin arzikin harajin fito
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Jigawa Za Ta Gina Gidaje 52 A Babban Birnin Jihar
Daga Usman Muhammad Zaria
Majalisar Zartarwa ta Jihar Jigawa ta amince da bayar da rancen kudi ga hukumar gidaje ta jihar domin gina gidaje 52 a Dutse.
A cikin wata sanarwa da kwamishinan yada labarai na jihar, Alhaji Sagir Musa Ahmed ya fitar, ya bayyana cewa gidajen za su kunshi masu dakuna uku da kuma dakuna biyu kowanne.
Ya ce aikin zai kasance a gaban tsohuwar unguwar majalisar dokoki, kusa da hanyar wucewa ta Jami’ar Tarayya da je Dutse, a matsayin wani shiri na asusun gina gidaje karkashin ma’aikatar gidaje, ci gaban birane da tsare-tsaren yankuna, ta hannun hukumar gidaje ta jihar.
Alhaji Sagir ya bayyana cewa, wannan mataki na nuna kudirin gwamnati wajen magance matsalar gidaje a babban birnin jihar, kara habaka ci gaban birane, tare da samar da ayyukan yi ga matasan jihar.
Ya ce an tsara wannan asusu ne domin tabbatar da dorewa, ta yadda za a ci gaba da zuba jari a ayyukan samar da gidaje masu araha a fadin jihar.
Haka kuma ya kara da cewa, gwamnatin jihar tana da kudirin ci gaba da inganta rayuwar al’ummarta, ta hanyar ayyuka masu amfani da jama’a, da ke inganta walwala, karfafa tattalin arziki, da tallafa wa matasa.
Kwamishinan ya kuma bayyana cewa, majalisar ta amince da bayar da kwangilar gyara da inganta gidan baki guda biyu (Malam Adamu Chiroma House da kuma Senator Francis Ella House) da ke cikin G9 Quarters a Dutse, da kudin sama da naira miliyan 219.7.
Ya ce aikin zai haɗa da cikakken gyara da inganta gine-ginen, gyaran hanyoyin ruwa da kuma girka tankokin ruwa ga kowanne daga cikin gidajen biyu.
Ya ce hakan na da nufin tabbatar da wadataccen ruwan sha mai dorewa a wuraren.
Alhaji Sagir Musa Ahmed ya kara da cewa, amincewar da aka yi da wannan kwangila na nuna jajircewar gwamnatin jihar wajen kula da dukiyar jama’a da kuma tabbatar da cewa gine-ginen gwamnati suna cikin yanayi mai kyau da nagarta.