Al-Houthi: Hare-haren Amurka sun kasa dakatar da gwagwarmayar Yeman
Published: 5th, April 2025 GMT
Madugun kungiyar Ansarallah ta kasar Yeman ya yi ikirarin cewa, zafafan hare-haren wuce gona da iri da Amurka ke kaiwa kasar Yemen, ya kasa dakatar da ayyukan gwagwarmayar Yeman na goyon bayan al’ummar Gaza ko kuma kare jiragen Isra’ila a tekun Bahar Rum.
A wani jawabi da ya yi a ranar Juma’a, Abdul-Malik al-Houthi ya ce Amurka ta zafafa kai hare-hare a kan kasar Yemen, inda wasu lokutan ta kai hare-hare sama da 90 a kowace rana, a wani bangare na goyon bayan da take baiwa kasar Isra’ila a yakin kisan kare dangin da ta ke yi a zirin Gaza.
Duk da haka, ya jaddada cewa, hare-haren na Amurka “sun kasa dakatar da ayyukan soji da ke tallafawa al’ummar Falasdinu, ko kuma tabbatar da kare zirga-zirgar jiragen ruwa na Isra’ila a cikin Bahar Maliya, Gulf na Aden da kuma Tekun Oman.”
Ya kuma ce jami’an sojin Amurka sun amince cewa hare-haren sun kasa dakile karfin sojojin Yemen.
Al-Houthi ya ce: “Amurka ta gaza cimma burin da ta sanya a gaba na kawar da shugabanni da kuma kawar da ‘yantacciyar kasar Yemen.”
Ya yi alkawarin cewa kasar Yemen za ta ci gaba da kai hare-hare na daukar fansa, kafin ya bayyana cewa: “Amurka ba ta tsoratar da mu.”
Shugaban kungiyar Ansarallah ya kuma gargadi gwamnatocin kasashen Larabawa da kasashen da ke makwabtaka da su kan goyon bayan hare-haren da Amurka ke kaiwa kasar Yemen sannan ya kara da cewa kutsawar da Ministan Isra’ila mai tsatsauran ra’ayi, Itamar Ben-Gvir ya yi a harabar masallacin Kudus, shaida ce ta ci gaba da cin zarafi da Isra’ila ke yi kan “daya daga cikin mafi girman wurare masu tsarki ga musulmi.”
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: kasar Yemen
এছাড়াও পড়ুন:
Trump ya fitar da Amurka daga UNESCO saboda amincewa da Falasdinu a matsayin Mamba
Amurka ta yanke shawarar ficewa daga hukumar kula da ilimi da kimiya da al’adu ta Majalisar Dinkin Duniya UNESCO a karo na biyu saboda matakin da ta dauka na shigar da Falasdinu a matsayin mamba.
Mataimakiyar sakatariyar yada labaran fadar White House Anna Kelly ta sanar da matakin a cikin wata sanarwa a ranar Talata.
Kelly ta ce dalilin da ya suka dauki wannan kan hukumar UNESCO, shi ne ta tallafa wa shirye-shiryen da Amurka ke kallonsu a matsayin wadanda ba su dace da muradunta ba.
“Shugaba Trump ya yanke shawarar janye Amurka daga UNESCO, wadda ke kula da ayyuka a bangaren raya al’adu da ilimi da zamantakewar al’umma, saboda daukar wau matakai wadanda ba su dace da manufofin Amurka ba,” in ji Kelly.
Ta ci gaba da cewa, shigar da Falasdinu a matsayin mamba a hukumar UNESCO, Amurka na Kallon hakan a matsayin babbar matsala kuma ya saba wa manufofin Amurka, wanda hakan ke ke kara haifar da karuwar kalaman kyama ga Isra’ila a cikin kungiyar.
Darakta-janar na UNESCO, Audrey Azoulay, ya bayyana matukar Rashin jin dadinsa kan matakin da Trump ya dauka na ficewa daga kungiyar, amma ya kara da cewa dama tuni aka yi hasashen haka, kuma UNESCO ta shirya ma hakan, tare da yin nuni da cewa hukumar ta dauki matakin karkata hanyoyin samar da kudadenta, inda kusan kashi 8% na kasafin kudin ta ke fiowa daga Washington.