Pezeshkian: Iran ba ta neman yaki da kowace kasa
Published: 5th, April 2025 GMT
Shugaba Masoud Pezeshkian ya ce Iran ba ta neman yaki da kowace kasa, amma ba za ta yi kasa a gwiwa ba wajen kare kanta saboda tana da kyakkyawan shiri a kan hakan.
Da yake magana a wata tattaunawa ta wayar tarho da yarima mai jiran gado na Saudiyya Mohammed bin Salman, Pezeshkian ya ce Jamhuriyar Musulunci ta Iran a shirye take ta shiga yin shawarwari don warware wasu matsaloli, bisa maslaha da mutunta juna, inda ya kara da cewa: “Ba ma neman yaki da wata kasa, amma ba mu da wani shakku wajen kare kanmu, kuma mun riga mun shirya tsaf dangane da hakan.
Shugaba Pezeshkian ya mika sakon taya murna ga yarima mai jiran gado na kasar Saudiyya, da sarkin kasar, da kuma al’ummar kasar ta Saudiyya dangane da idin karamar Sallah.
Ya ce kasashen musulmi ta hanyar dogaro da kansu zasu iya karfafa hadin kai a tsakaninsu, tabbatar da zaman lafiya da tsaro da ci gaba a dukkanin matakai.
Shugaban ya kara da cewa, idan musulmi suka hada karfi da karfe, za su iya hana zalunci da laifukan da ake yi wa wasu kasashen musulmi da suka hada da Falasdinu da al’ummar Gaza, shugaban ya kara da cewa: Ina da tabbaci a kan cewa kasashen musulmi ta hanyar yin aiki tare za su iya samar da tsaro da wadata a yankin.
A nasa bangaren yarima mai jiran gadon sarautar Saudiyya Bin Salman ya taya shugaba Pezeshkian da al’ummar Iran murnar idin karamar salla, inda ya bayyana jin dadinsa ga kiran da shugaban kasar Iran ya yi na hadin kai tsakanin al’ummar musulmi.
Ya kuma bayyana fatan cewa, karfafa hadin gwiwa tsakanin Iran da Saudiyya zai samar da ci gaba mai ma’ana da kwanciyar hankali, tsaro, da ci gaba a yanking abas ta tsakiya.
Yarima mai jiran gado na Saudiyya ya kara jaddada cewa, hadin gwiwa tsakanin kasashen Iran, Saudiyya da sauran kasashe na iya inganta zaman lafiya a yankin, yana mai jaddada aniyar Riyadh na taimakawa wajen tinkarar duk wani kalubalen da ke da nasaba da kawar da ta’addanci a yankin.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Saudiyya ta saki ’yan Najeriya 3 da ta kama kan zargin safarar miyagun ƙwayoyi
Hukumomin a Ƙasar Saudiyya, sun saki wasu ’yan Najeriya uku da aka kama a Jeddah kan zargin safarar miyagun ƙwayoyi.
Waɗanda aka saki sun haɗa da Hajiya Maryam Hussain Abdullahi, Hajiya Abdullahi Bahijja Aminu, da Malam Abdulhamid Saddieq.
Tinubu bai shirya gudanar da sahihin zaɓe ba a 2027 – Buba Galadima Gwamnati ta fara duba yara marasa galihu kyauta a asibitin Aminu KanoSun shafe makonni huɗu a tsare kafin aka tabbatar da cewa ba su da laifi.
A wajen taron manema labarai a Abuja, mai magana da yawun Hukumar Yaƙi da Sha da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi (NDLEA), Femi Babafemi, ya ce sakin ya biyo bayan tttaunawa da Shugaban NDLEA, Janar Mohamed Buba Marwa (mai ritaya), tare da Hukumar Hana Fataucin Miyagun Ƙwayoyi ta Saudiyya.
Shugaba Bola Ahmed Tinubu ne, ya bayar da cikakken goyon baya wajen ganin an saki waɗanda aka kama.
Bincike ya gano cewa wasu masu safarar miyagun ƙwayoyi ne a Filin Jirgin Sama na Mallam Aminu Kano, suka ƙwayoyin a jakunkuna waɗanda aka kama.
Mutanen uku da aka kama, sun tashi a jirgin Ethiopian Airlines a ranar 6 ga watan Agusta don yin Umara, amma aka kama su a Saudiyya.
Binciken NDLEA ya kai ga kama wani shugaban masu safarar miyagun ƙwayoyin, mai shekaru 55, Mohammed Ali Abubakar (wanda aka fi sani da Bello Karama).
Hakazalika, hukumar ta kama wasu mutum uku ciki har da ma’aikatan jirgi.
Mutanen da aka kama su ne suka shirya safarar ƙwayoyin a jakunkunan mutane da aka kama a Saudiyya.
NDLEA ta gabatar da shaidun da suka tabbatar da cewa mutanen da aka kama a Saudiyya ba su da laifi.
Sakamakon haka, hukumomin Saudiyya suka sako ɗaya daga cikinsu a ranar 14 ga watan Satumba, sannan suka sako sauran biyun a ranar 15 ga watan Satumba.
Babafemi, ya ce Marwa ya gode wa hukumomin Saudiyya saboda mutunta yarjejeniyar haɗin kai tsakaninsu da Najeriya.
Ya kuma gode wa Shugaba Tinubu da sauran manyan jami’an gwamnati, ciki har da Ministan Shari’a, Ministan Harkokin Ƙasashen Waje, Ministan Sufurin Jiragen Sama, da Mai Bai Wa Shugaba Shawara Kan Harkar Tsaro, saboda gudummuwarsu.
Ya ƙara da cewa wannan lamari ya nuna cewa Najeriya tana tsayawa wajen kare ‘yan ƙasarta a ƙasashen waje kuma ba za ta yadda wani ɗan Najeriya ya sha wahala saboda laifin da bai aikata ba.