HausaTv:
2025-06-15@10:12:16 GMT

Pezeshkian: Iran ba ta neman yaki da kowace kasa

Published: 5th, April 2025 GMT

Shugaba Masoud Pezeshkian ya ce Iran ba ta neman yaki da kowace kasa, amma ba za ta yi kasa a gwiwa ba wajen kare kanta saboda tana da kyakkyawan shiri a kan hakan.

Da yake magana a wata tattaunawa ta wayar tarho da yarima mai jiran gado na Saudiyya Mohammed bin Salman, Pezeshkian ya ce Jamhuriyar Musulunci ta Iran a shirye take ta shiga yin shawarwari don warware wasu matsaloli, bisa maslaha da mutunta juna, inda ya kara da cewa: “Ba ma neman yaki da wata kasa, amma ba mu da wani shakku wajen kare kanmu, kuma mun riga mun shirya tsaf dangane da hakan.

Shugaba Pezeshkian ya mika sakon taya murna ga yarima mai jiran gado na kasar Saudiyya, da sarkin kasar, da kuma al’ummar kasar ta Saudiyya dangane da idin karamar Sallah.

Ya ce kasashen musulmi ta hanyar dogaro da kansu zasu iya  karfafa hadin kai a tsakaninsu, tabbatar da zaman lafiya da tsaro da ci gaba a dukkanin matakai.

Shugaban ya kara da cewa, idan musulmi suka hada karfi da karfe, za su iya hana zalunci da laifukan da ake yi wa wasu kasashen musulmi da suka hada da Falasdinu da al’ummar Gaza, shugaban ya kara da cewa: Ina da tabbaci a kan cewa kasashen musulmi ta hanyar yin aiki tare za su iya samar da tsaro da wadata a yankin.

A nasa bangaren yarima mai jiran gadon sarautar Saudiyya Bin Salman ya taya shugaba Pezeshkian da al’ummar Iran murnar idin karamar salla, inda ya bayyana jin dadinsa ga kiran da shugaban kasar Iran ya yi na hadin kai tsakanin al’ummar musulmi.

Ya kuma bayyana fatan cewa, karfafa hadin gwiwa tsakanin Iran da Saudiyya zai  samar da ci gaba mai ma’ana da kwanciyar hankali, tsaro, da ci gaba a yanking abas ta tsakiya.

Yarima mai jiran gado na Saudiyya ya kara jaddada cewa, hadin gwiwa tsakanin kasashen Iran, Saudiyya da sauran kasashe na iya inganta zaman lafiya a yankin, yana mai jaddada aniyar Riyadh na taimakawa wajen tinkarar duk wani kalubalen da ke da nasaba da kawar da ta’addanci a yankin.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

DA ƊUMI-ƊUMI: Gwamnati Ta Janye Taron Addu’ar Neman Wadatar Abinci

Ma’aikatar Gona da tsaron abinci ta ƙasa ta dakatar da shirinta na gudanar da addu’a da azumi na kwanaki uku, bayan martani mai zafi daga jama’a. Tun da farko, an tsara addu’ar ne domin neman taimakon Ubangiji wajen tabbatar da tsaron (wadataccen) abinci a Nijeriya.

Wata takarda da ta bayyana ga jama’a, wadda Daraktar Gudanarwa ta Ma’aikatar, Mrs. Adedayo Modupe O., ta sanya wa hannu, ta gayyaci daraktoci da sauran manyan ma’aikata domin halartar wannan taron addu’a a shalƙwatar ma’aikatar a Abuja, a ranakun 16, 23 da 30 ga Yuni, 2025.

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Addu’ar Kwana 3 Don Samun Isasshen Abinci Wani Gidan Gona A Jihar Ogun Zai Fitar Da Tarwada Ta Kimanin Naira Biliyan Shida A 2025

Sai dai cikin wata sabuwar sanarwa daga wannan darakta, an bayyana cewa an dakatar da shirin addu’ar har sai wani lokaci na gaba, ba tare da bayyana dalilin janye umurnin ba. Wannan matakin ya biyo bayan suka da jama’a suka yi a kafafen sada zumunta kan dacewar shirin.

Masu sukar sun bayyana cewa gwamnati ya kamata ta mai da hankali wajen samar da tsare-tsare na zahiri kamar gyaran dabarun noma, da tallafawa manoma da kuma inganta rarraba abinci, maimakon dogaro da addu’a wajen shawo kan matsalar yunwa da hauhawar farashin abinci.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Martanin sojojin Iran ga Isra’ila zai zama mafi muni idan aka ci gaba da kai hari (Pezeshkian)
  • Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Sun Shaida Gamsuwa Da Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Tsakiyar Asiya
  • Gwamnatin Najeriya Ta Yi Allawadai Da Harin Da “Isra’ila” Ta Kawo Wa Iran
  • Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Kara Habaka Daga Manyan Tsare-Tsare Zuwa Matakai Na Ainihi
  • DA ƊUMI-ƊUMI: Gwamnati Ta Janye Taron Addu’ar Neman Wadatar Abinci
  • Jagoran Juyin Juya Halin Musulunci Ya Aike Da Sako Ga Al’ummar Iran Bayan Harin Da Iran Ta Fuskanta
  • Jami’in Hamas Ya Jinjinawa Iran Kan Kakkausan Martanin Da Ta Mayar Kan Haramtacciyar Kasar Isra’ila
  • Iran : harin da Isra’ila ta kai ‘ ayyana yaki’ ne_ Araghchi
  • Jagora: Sojojin Iran ba zasu sararawa Isra’ila ba
  • Salami: Babu Inda Ba Za Mu Iya Kai Wa Hari Ba A Fadin HKI